HASKEN RAYUWATA COMPLETE HAUSA NOVELS

Tana cikin karatu manyan baƙi suka ƙarasa nan ta koma gurinsu Aunty Fido ta zauna nan akashiga gudanar da jawabai m.c yafara sanarda irin kyaututukan da suka samu aka kira ɗaliban suka amsa har Hafsat zata sauka da niƙiƙin kyaututuna m.c yace”sarki yaƙarama wadda tayi na ɗaya da scholarship a jami’arh Madina setazo ta ƙara godiya a gaban sarki”.
amsar loudspeaker tayi tashiga zazzaga larabci tana hawaye anan ne tace sede ɗan uwanta Yah Amin yayi ita makaranta zata tafi sosai kowa yaji daɗin bayaninta nan akashiga walima har zasu zauna suci abinci Aunty Fido tace”gaskiya ku tashi mutafi saboda ayi komai da wuri”.
“toh Aunty”.
nansuka tafi suka shiga mota suka nufi Airport kowa cike da farinciki suna zuwa ana kiran ƴan flight ɗinsu ansar ticket sukayi suka hau aka lula dasu United Kingdom(U.K).
2:00pm
Jirginsu na sauka a ƙasar London wasu haɗaɗun roice-roice guda biyar na danna kan hancinsu filin jirgin inda suka shiga a jere sababbi dal dasu kowacce da kalarta ta farko an rubuta 5 ta biyu a jikinta an rubuta D har zuwa ta ƙarshe da aka rubuta P inka haɗa rubutun gabaki ɗaya rubutun yabada 5DBCP !!!!!!
Tofa ya za’ayi kenan ga Hafsat ga 5DBCP koya zata kaya?.
Tallah! Tallah!! Tallah!!!
Ina kuke masoyana na haƙiƙa kufito ku nunamun ƙauna ta hanyar siyen littafina me suna BAR RAINA ALLURA(Itama Ƙarfe ce) ta wannan account number 2411022356 Aisha Umar Ibrahim Zenith Bank aiko da shedar ka ta wannan number 08108362334 ko katin Vtu ta wannan number 08108362334 Mtn or Airtel sena jiku.
Kuyi share dan Allah saboda masu karatu su cigaba.
Vote and Comments
Plz share to others
Daga Alƙalamun ƴar Mutanen Gwarzo.✍️✍️_✍️???? HASKEN RAYUWATA
MALLAKIN
REAL EESHOW
HOME OF QUALITIES WRITERS ASSOCIATION
Nagode sosai da irin soyayyar da kuka nunamun Allah yabarmu tare ina Alfahari daku masoyana aduk inda kuke Alherin Allah yakaimuku nima nayi missing ɗunku idan kin karanta ki tura wani group ɗin saboda ya isa zuwa gurin masu karatu ko a ina kike ki nunamun ƙauna ta hanyar suburbuɗamun comments and votes da sharing much love.
PAGE 4️⃣1️⃣➡️4️⃣2️⃣
Buɗe ƙofar motar farko akayi seda aka ɗauki mintuna sannan ya zura haɗaɗiyar ƙafarsa dake sanye cikin wani haɗaɗen takalmi black yafito cikin jinkai inka ganshi seka ɗauka macene sakamakon necklace da earing ɗin dake kunnensa ga gashinannan yasha gyara anyi parking ɗinsa a tsakiyar kansa inda iska ke kaɗashi su Adam ma fitowa sukayi daga motocinsu cikin jinkai a jere suka jera su biyar ɗin suka nufi gurin wani white Jet da aka rubuta 5DBCP a jikinsa.
Jirgi na sauka Aunty Fido ta kalli Abdallah da Salman tace”ku abinda za’ayi ku wuce kufara kammala musu da registration mukuma semu wuce gida danso nake na nemamusu ƙawaye kafin mu koma saboda halin rayuwa”.
“toh Aunty “.
“ku kutashi mutafi”.
“toh”.
Hafsat tafaɗa jiki ba kwari suka fara fita ta ƙofar baya a sanyaye take tafiya harta isa step ɗin benen jirgin takawa tayi ta fara sauka lokaci ɗaya gabanta ya yanke ya faɗi tashiga duniyar tinani jin muryar Fatimah tayi tace”Aunty Hafsat lafiya naga duk jikinki yayi sanyi kin tsaya”.
dawowa tayi daga duniyar tinanin data lulua tace”bakomai “.
nanta sauka suka jera suka nufi inda motocinsu suke Fatimah ce tace”Aunty Hafsat wai meke damunki banason ganin Auntyna cikin damuwa?”.
sauke numfashi Hafsat tayi cikin kulawa tace”sweetheart ɗina wlh bakomai kawai dai jikina ke bani kamar anan gurin akwai wani abu dana ajiye a gurinnan me mahimmanci a gareni amma kuma ninasan ban aje komaiba hasalima bansan kowa ba”.
murmushi Fatimah ta saki tare da cewa”kodai mijinnaki ne yazo gurinnan”.
duka Hafsat takaimata cikin wasa gocewa tayi tare da cewa”Allah kuwa kinsan yanzu kindawo kusa dashi”.
“ke kikasan ma wani miji ni am single”.
nan sukaita surutunsu har suka isa suka shiga motocin da sukazo ɗaukarsu suka tafi.
Yazo shiga Jet ɗin kenan yaji gabansa ya faɗi yakasa ko ɗaga ƙafarsa har motocin da sukazo ɗaukarsu Hafsat sukazo suka wuce bin motocin yayi da ido jiyayi yashiga wani irin yanayi dakyar yaƙarasa shiga cikin jirgin ya zauna tare da ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya ya lumshe sexy eyes ɗinsa ya kwantar da kansa jikin kujerar jirgin har suka tashi sama maganganun Ammi ne suka faɗomasa a zuciyarsa yace”so never F2 da faɗawa cikin wannan westing time ɗin kamar ba F2 ɗinda mata ke rububiba dole nayi ƙoƙarin saita kaina dan kar mutane su fuskanci halin da nike ciki akan wannan mara kunyar”.
wata zuciyarce tace”to ka kira Ammi kaji yadda mutum zeyi ƙoƙari ya cire mutum a zuciyarsa”.
suna sauka suka hau mota ya turawa Ammi text bejima da turamataba takira tare da cewa”me sunan Malam naga text ɗinka”.
murmushin gefan baki yayi haɗe da cewa”Ammi ina yini wlh damuna yayi wai to yanzu taya zeyi ya cireta daga zucuyarsa danshi bayason raini”.
murmushi Ammi tayi har yana jin sautinsa tace”aishi so ba’ah sanin lokacin da yake shiga zuciyar mutum haka ba’ah sanin lokacin da yake fita”.
“toh yanzu kenan ba yadda zeyi kenan Ammi”.
“gaskiya ba yadda za’ayi ya iya cireta saboda Allah ne ya ɗoramasa sonta bashi ya ɗorawa kansaba shawarar da zan baka ka bashi kacemasa yayi gaggawar sanar da ita sirrin zuciyarsa kodako zata wulaƙantasa ya jure yafaɗamata yana sonta yasanima ko itace HASKEN RAYUWARSHI kuma Alkhairinsa kuma kacemasa ya cire girman kai ya sanar da ita cikin yau zuwa gobe ya nemeta ya faɗamata”.
“toh zan sanar dashi Ammi”.
yafaɗa a taƙaice nan sukayi sallama ya kashe zuciyarsa ce tace”dolene kayi nesa da duk wani abinda zesa kaji labarinta dan inba hakaba ajinka zubewa zeyi kan wannan small babyn yarinyar”.
yana wannan zancen yaji Ahmad na cewa “ammafa yarinyar nan ta wahalar damu sosai wlh”.
“wlh kuwa amma ai zata gane kurenta sosai”.
jiyayi duk wani takaicinsu yakamashi dakyar ya iya control ɗin kansa suna isa hall ɗin da aka karramasu Hafsat suka tsaya daga can nesa da gurin sukayi parking Ahmad yace”bara nakira Bengement su ɗakkota”.
“yauwa Auta”.
hankalin F2 ne yayi mugun tashi ya rasa mekemasa daɗi can zuciyarsa tace”inbanda abunka F2 meye na damuwa ne akanta bayan kuma ka yadda da zuciyarka akan ba sonta kakeba karfa zancen Ammi yazama gaskiya”.
ɗaya zuciyarce tace”ba haka bane kawaidai ina tausayintane banaso a ɓatamata tarbiyya dole nayi wani abu dan bazan taɓa bari abunnan yafaruba”.
yafaɗa tare da gyara zamansa kira ɗaya Ahmad yayiwa Bengement ya ɗauka tare da cewa”Boss kun iso ne?”.
“eh mun iso ku ɗakkota muna ɗan nesa da gurin hall ɗin”.
“toh bara muje mu ɗakkota”.
“toh”.
nanya kashe wani shu’umin murmushi Abbakar yayi tare da cewa”kace yarinya tashigo hannu”.
“sosaima kuwa yanzu yace zasu kawota”.
“kace yau akwai zuwa Queen Club kenan”.
“sosaima kuwa”.
suna magana su Bengement suka ƙaraso sauke glass ɗin motar da suke akayi Bengement ya leƙa tare da cewa”Boss wlh anduba ko ina na gurin ba’ah sametaba anyako wannan yarinyar ba aljana bace Boss saboda abun da mamaki yazunfa naga yarinyar amma yanzu ina zuwa bata sama ko ƙasa”.
a hassale Adam yace”badai ku duba sosaiba daiko amma yarinyar nan suna nan cikin gurin wlh idan muka fitone mu dole za’ah san munzo gurin”.
“toh Boss bara muƙara dubawa”.
“gatacan yimaza ku ɗakkota”.
kallon gurin Bengement yayi tare da cewa”aiko itace bara mu ɗakkota”.
gaban F2 ne yabada damm ganinsu Bengement sun ɗakko yarinyar sun shaƙamata cocaine ta zube sun cicciɓota suna zuwa Obama ya wangale ƙofar mota suka sakata har zasu rife Adam yace”ku buɗe niƙab ɗin fuskarta saboda iska”.
“toh oga”.
gaban F2 ne yabada damm cikin sauri ya buɗe idonshi cikin tashin hankali suna buɗewa yaga ba ita bace cikin daka tsawa Ahmad yace”mezan gani haka aiba ita bace ku ɗaukemana wannan sharar tinkafin raina ya ɓaci”.
murmushin gefan baki F2 yayi tare da rife idonsa yanajin wani irin farinciki a zuciyarsa ɗauke yarinyar su Bengement sukayi aka fita da ita suka shaƙamata abu ta dawo hayyacinta nan suka tambayeta Hafsat nanta sanar dasu takoma ƙasarsu dan taga fitarsu sakata sukayi tabasu Address ɗin Hafsat sannan suka sallameta.