BABU SO HAUSA NOVEL

FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL PART 2

      Duk yanda yaso ya jure abinda yake ji game da feeling ɗin ta amma abun ya citura, bare yanda ruwa ya dake shi duk tsigan jikin sa ya gama tashi. ƙirr idanun sa sun kasa barci, dole ya miƙe ya bi umarnin zuciyar sa a kan zuwa ɗakin ta, shi kansa be san meyasa ba amma yana son zuwa gare ta ko da kallon fuskar ta ne ya riƙa yi, ya san a yanzu tayi barci shiyasa ya lallaɓa ya wuce ɗakin nata kanshi tsaye

A hankali ya tura ƙyauren ya shige, akwai fitilan aci bal-bal da bata kashe ba, da sanɗa ya ƙarisa kusa da ita ya sauke idanun sa a kan fuskar ta. Ajiyan numfashi ya sauke yana matsawa kusa da ita ya sanya hannun sa a hankali ya soma shafa mata fuska

The more Yana shafa mata fuska the more Yana ƙara jin feeling ɗin ta. Duk yanda yaso ya daure ya koma tunda yayi mintoci a ɗakin yana ƙare mata kallo, amma ina tuni zuciyar sa ta ingiza shi yin abinda be taɓa tunanin mata ba. Wanda ya kasa controling zuciyar sa da gangan jikin sa ga abinda suke muradi a halin yanzu.

     Kamar a mafarki haka take amsar saƙonnin nashi, tun tana iya jurewa domin a zaton nata lallai mafarkin ne, but a lokacin da ta farka tuni yayi nisan kiwon da bazai taɓa jiyo ta ba, duk yanda taso ta ƙwaci kanta amma ina ta gaza, haka take kuka tana roƙon shi saboda bata shirya zuwan ma wannan ranan ba, kuma ga wanda zuciyar ta ke cike da zallan tsanar sa, amma ta kasa cin nasara, dole tana ji tana gani ya raba ta da budurcin ta ba tare da ta iya ƙwatan kanta ba….

        Kuka ta fashe dashi a sanda tazo nan a tunanin ta

Da sauri Yusra ta buɗe ƙofan bayin tana kiran sunan ta. Sai ta ƙarisa wajen ta tana riƙo ta ganin ta a zube a ƙasa. Duk tambayoyin da ta jero mata a kan sanin abinda ke damun ta, amma taƙi ƙo motsa wa bare ta tanka ta, dole ta kamo hannun ta suka fito

Duk ƴan ɗakin da kallo suka bi ta ganin yanda hawaye ke zuba a saman fuskar ta. Kuma duk tambayar da suka yi mata sai dai tace musu, “babu komi”. Sai gaba ɗaya tunanin su sai ya tafi a kan bayyanar cikin ne, duk da babu wanda ya kawo wani zargi wanda kowa zuciyar sa cike take da amince wa da cikin Usman ne, amma tabbas abun da ciwo a gare ta, kuma kowa ya gane abinda take ma kuka

Aunty Jamila ce kawai da bata gama sanin abinda ke faruwa ba, duk da ta san akwai saɓani a tare da su. Ita take ta faman rarrashin ta

Su Abbu dai fita suka yi a ɗakin. Inda Yusra ta mayar mata da ƙarin ruwan.

            Mutanen gidan basu koma ba har sai da bayan sallan isha’i yayi, inda suka tafi tare da Ɗahiran tunda an bata sallama.

           Suna koma wa Big Dady ya nemi Usman yazo ya same shi a part ɗin su. Nan ya titsiye shi a kan ya ba shi takardan sakin Ɗahira

Amma Usman babu kunya yace ma Big Dadyn, “shi fa yana son Matar sa yanzu bazai sake ta ba, bare kuma yanzu tana ɗauke da cikin ɗan sa, be ga wanda ya isa ya saka shi sakin ta ba”.

Marin shi Big Dadyn yayi saboda jin kalaman sa

Daga Usman ɗin har Hajiya dake zaune tana sauraron su sai da suka shiga shock sabida zallan mamakin sa. Maganar sa ne ya dawo da su hayyacin su

“Mutumin banza mutumin hofi, har kai ka isa ka faɗa mana abinda ya kamata? Da can meyasa baka ɗauke ta a matsayin matar ka ba sai yanzu? Tunda kai mara kunya ne duk abinda kayi mata kace zamu bar ka haka, a kan daughter babu abinda bazan iya maka ba in dai in ƙwato mata haƙƙin ta ne…”

Da sauri Usman ɗin ya tashi tun kafin ya gama jin zantukan nashi ya fice yana zubar da hawaye.

      Hajiya da itama hankalin ta yayi ƙololuwar tashi a kan abinda Big Dadyn yayi, tace dashi, “haba Dadyn Zainab meyasa baza ka tausaya wa yaron nan ba? Wlh tunda har kaji ya buɗe baki ya ce yana son zama da matar sa, to, har zuciyar sa ne, kuma…”

“Ki yi min shiru Asiya baza ki koya min abinda zan yi ba, bari kiji wlh kema duk sanda na sake magana irin wannan kika sako min baki zaki ga abinda zan miki, tunda ke kike ɗaure masa gindi yake son mayar damu mutanen banza. Aure ne kuma babu fashi sai an raba shi”. Sai ya tashi fuuu ya wuce ɗaki ya bar ta a nan.

             ***

        Kai tsaye Part ɗin shi ya wuce, ya buɗe ƙofan ya shige sai kan gadon shi ya faɗa riƙe da kumatun shi har Yanzu, idanun sa na tsiyayar da hawaye kamar ba shi ne Jarumin nan me dakakken zuciya ba, samun ka ga hawaye a kyakykyawar fuskar sa sai an jima, amma yau sai ga shi a kan abinda be shirya masa ba yana zubar da hawaye, shi dai ya san cewa har zuciyar sa yanzu yana matuƙar jin ta, kuma bazai iya rabuwa da ita ba domin babu macen da ta cancanci zama dashi sai ita, ita kaɗai yanzu yake ganin ta dace da shi, ba zai taɓa iya zama da kowa ba sai ita, shiyasa kawai yake son daidaita komi ya wuce, amma kuma yana ganin ba sauƙi ne abun ba. Ya zai yi?

Ya jima a haka a wannan mawuyacin halin da ya kasa controling ɓacin ransa, babu abinda yake muradi yanzu illa ya saka ta a idon sa, amma kuma yanda yake ji bazai iya ko da motsa wa bane a wurin.

       A wannan daren daƙyar barci ɓarawo ya sace sa. Be farka ba sai ƙarfe 09:00am. Komawar sa bayan sallan asuba

Koda ya tashi wanka ya soma yi fuskar sa duk babu walwala, har wani kumbura tayi fuskar saboda damuwa da rashin barci da be samu yayi ba

Yana shirya wa ya fice yayi Part ɗin su Ɗahira, da shigan sa da sallama

Aunty amarya da Umma dake karin safe suka amsa mishi suna bin shi da kallo cike da mamakin ganin shi

Shi kuwa be damu da kallon da suke mishi ba, daƙyar ya saki fuskar sa ya gaishe su yana tambayan Abbu?

Umma ce ta ba shi amsa da faɗin, “yanzu ya fita shi da Fadil ai”.

Sai ya ɗan shafa kansa yace, “Nafeesa fa?”

Sai duk suka tsaya suna kallon sa don basu fahimci da wa yake nufi ba

Tunanin ko Ɗahira ce yake nufi da Aunty Amarya tayi, shi ne tace mishi, “bata tashi daga barci ba”.

“Ok bari in duba ta”. Yayi maganar yana yin gaba ya shige ɗakin ta

Sai suka saki baki kawai suna bin shi da kallo cike da zallan mamakin rashin kunyan sa.

      Shi ko, ko a jikin sa. Yana shiga ya ganta kwance daga ita sai doguwar riga mara nauyi me taushi da aka yi kwalliyan Flower’s a jiki, kalan fari da Green. Ba barci take yi ba tunda ta tashi tun ɗazu har tayi wanka, kawai koma wa tayi ta kwanta sabida ba ta jin daɗin jikin ta, ga tunanin cikin nan ya hana ta sukuni, tana tuna wa sai hawaye. Bata ji shigowar sa ba sai jin mutum tayi yana shirin hayo wa kan gadon. Kan ta farga ya haye abun shi. A firgice ta ciro kanta dake ƙarƙashin matashi saboda ba ƙaramin tsorata tayi ba, bata taɓa tunanin shi zata gani ba shiyasa ta saki baki zata kurma ihu sabida tsaban kiɗima

Take ya rufe mata baki da nashi yana janyo ta jikin shi

Duk iya mutsu-mutsun da take yi wajen ƙwatan kanta amma ina ta kasa, lokaci ɗaya hawaye ya wanke mata fuska tare da fashe wa da kukan da ba’a jin muryan ta sai gunjin kukan, sabida tsaban takaici da ya cika ta ta kasa motsa wa ma

     Shi kuma sai da ya gama tsotsan bakin ta son ransa, sai da ya ga zai iya rasa tunanin sa kafin ya janye bakin nashi yana ajiyan zuciya idanun sa har sun sauya kala

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button