FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL PART 2

“Momy na ce miki aiki na koma shiyasa”. Yayi maganar kamar zai yi kuka
“Mtsww! dalla rufe min baki, meye amfanin aikin tunda ka ajiye? To, Ni ban amince ka kai tsawon wannan lokacin ba, yarinyan da ba ka so meye kuma na zuwa da ita wani waje? Ka gaggauta shirin dawowa tun yanzu domin hutun ya isa haka, kuma ka kira Dadyn ka yanzu domin suna ta neman ka su ma basu same ka ba, ga Kakan ku can har rashin lafiya ya yi amma baka da labari”.
“Ok”. Kawai yace mata saboda be da abun cewa, ba kuma wai don ya yarda zai yi abinda take so ɗin bane na game da dawowar sa
Sallama suka yi, inda ya mayar da akalan kiran ga Mahaifin sa, ringing biyu ya ɗauka, gaishe shi ya soma yi
Amma Big Dady be amsa ba, sai ya fara jeho masa tambaya kamar yanda Hajiya tayi masa, “me ya tsayar dashi tsawon lokacin nan ba tare da ya kira gida an ji sun sauka lafiya ba?”
Be da amsar faɗa masa, illa shiru da yayi
Nan kuwa ya dinga mishi faɗa, ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba, sannan daga ƙarshe yace masa “ya ba wa Ɗahira wayan”.
Duk da maganar ta bugi Usman, amma hakan be sa ya nuna akwai wani ruɗe wa a tattare dashi ba, illa gyara murya da yayi ya ce masa, “uhmmm Dady tana barci yanzu haka, sabida nan dare ya soma nisa”
“Ok ka tabbatar gobe idan ta tashi ka haɗa Ni da ita”.
“To”. Ya amsa masa
“Ka kira wayan Kaka sabida yanzu ba na gida bare na faɗa masa ka kira”. Cewar big Dady
Amsa mishi yayi, sannan suka yi sallama. Inda ya kira Kaka. A lokacin Fadil ke zaune dashi tunda jikin nasa da sauƙi, sai abinda ba a rasa ba
Nan Kaka yayi murna da jin suna lafiya, ya tambayi Ɗahira yace, “a bata wayan”
Sai ya faɗa masa yanda yace wa Big Dady.
Koda suka gama wayan tsaki yaja fuska babu walwala, ya ajiye wayan, kasa ci gaba da aikin yayi sabida ransa duk a ɓace yake, ya tashi ya sauya kaya zuwa gajeren wando da Singlet ya kwanta.
WASHE GARI
Da safe da ya tashi, zuwa ƙarfe 09:00am. Ya gama shirin sa, ya fito Parlour, inda Ɗahira take kwance ya kalla, sai ya kawar da kai yana tamke fuska kamar an aiko masa da saƙon mutuwa, kai tsaye kichen ya nufa, ya haɗa coffee ya shanye a kichen ɗin, sannan ya fito ya nufi ƙofan fita, har ya buɗe ƙofan; ko me ya tuna ya dawo da baya ya nufe ta
Tana nan kwance kamar yanda ta kwanta tun jiya, tun barcin da ya ɗauke ta a yammacin jiya bata ko motsa ba, kallo ɗaya kayi mata zaka gane tana shan matuƙar wahala, daga gani ba barcin lafiya bane, duba da yanda take haɗa gumi tana fitar da numfashi da ƙarfin gaske, kuma duk da uwar gumin nan da take yi amma hakan be hana jikin ta rawan ɗari ba.
Yana zuwa kusa da kanta, ya sanya ƙafa ya bugi kan nata
Wani irin zabura tayi tana sakin ƙara, lokaci ɗaya ta buɗe shanyayyun idanun ta da suka kaɗa suka yi jazur suka shige ciki tsaban kumburan da suka yi, dafe kanta tayi saboda sara matan da yayi lokaci ɗaya, sai wani jiri da ya kawo mata mamaya lokaci ɗaya ta koma yanda take tana me runtse idanun ta da suka soma ruwan hawaye, ko kaɗan ta kasa buɗe ido balle ta kalli inda yake, duk da kuwa ta san shi ne a kanta sabida ƙamshin turaren sa da ta jiyo, kuma ta san babu wanda zai mata haka sai shi
“Get up and sit down”. Yayi maganar kamar ana masa tilas, sai dai yanda muryan nasa ta fita hakan zai saka ka gane a cikin ɓacin rai yake
Bata motsa ba don bata da ƙarfi ko na sisin kobo, kamar dai an zare mata laka a jikin ta take ji, kamar kuma ana yayyanka naman jikin ta saboda mugun ciwon da yake mata, ga rashin sabo na kwanciyar ƙasa, duk ya bi ya haɗe mata ya saka mata wani irin ciwo me wuyan fassara, ji take yi tamkar dai ta mutu ta huta
Tsawa ya daka mata yana sake bata umarnin tashi
Babu yanda ta iya dole ta soma yunƙurin tashi, hawaye na ambaliya a fuskar ta tamkar ana tsiyayar wa daga famfo, gaba ɗaya jiri take ji, hakan yasa daƙyar ta tashi zaune tana ƙanƙame jikin ta, komi ganin sa take yi bibbiyu, ba ma tasan takamaiman inda yake tsaye ba, domin ba ta gane komi, ga hawayen da ya cika mata ido fal
Shi kuwa wayan sa ya zaro cikin aljihu, sannan ya latsa yana kallon ta yace, “za kiyi waya da mutanen gida, ko kaɗan ba na son ki nuna wani alama da zai saka su gane halin da kike ciki, idan kuwa kika yi haka..” ya ci je ƙasar bakin sa yana sake tamke fuskar sa, “wlh summa tallahi sai na binne ki da ranki a gidan nan, kuma kar kiyi tunanin idan kin faɗa musu kin sha ne”.
Wayan ya miƙa mata bayan ya kira Numban Big Dady, sannan ya bata umarnin ta amsa
Jiki na rawa ta miƙa hannu tana laluba inda zata ji wayan, nan ta cafke wayan da hannun sa
Da sauri ya zame nasa hannun saboda jin wani abu da ya tsarga masa daga kwanyan sa har ƙafafun sa, har wani ƙanƙame jiki yayi yana lumshe ido saboda jin yanayin abinda da ya kasa fassara mene ne
Ba don Allah yasa ta rigada ta riƙe wayan ba, da tuni tasha ƙasa. Kara wayan tayi a kunne jin muryan Big Dady na faɗin, “Hello.. Hello”.
“Hel..llo.. Daddddy..”. Tafaɗa da wani irin murya tana me fashe wa da kuka lokaci ɗaya.
????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTOR’S
????
????????????????????????????????????????
????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????
MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL
بسم الله الرحمن الرحيم
⚖
FEENAH WRITER’S ASSO????
”’®Ɗaya tamkar da Dubu”’????✓
JIKAR LAWALI CE✍️
Wattapad: UmmuDahirah????
\F.W.A????/
SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY
.
EPISODE Forty Five
Zaro mata ido Usman yayi, lokaci ɗaya ya damke dantsen hannun ta tare da matse wa da ƙarfi yana caka mata ƙumba; ta yanda zata ji zafi
Sosai kuwa taji zafin da har yasa ta saki siririyan ƙara tana hawaye
Sake zare mata idanu yayi yana ɗaura hannun sa saman baki alamun tayi shiru
Kallon sa kawai take yi tana tsiyayar da hawaye ba tare da ta amsa tambayoyin da Big Dady yake jero mata ba, Sai da ya sake kiran sunan ta a karo na uku kafin ta amsa shi tana faɗin, “na’am Dady. I miss You so Much!” Tayi maganar cikin rauni tana ci gaba da hawayen ta
“What’s the matter, daughter? What’s wrong with you? Did I hear you? Did you tell me if there was a problem?”
Still idanun ta suna kallon Usman da ya kasa ya tsare yana mata gargaɗi, gaba ɗaya ya ɗaure fuskar sa alamun babu imani. Hakan yasa taji tsoro sosai, domin ta san ko ta sanar wa Dady dole ne yayi mata abinda yayi ninya, tunda ba kusa suke ba, kafin su koma gida ya gama aiwatar da duk abinda yake so, ƙarshe ma ta ƙara wa kanta uƙuba, don haka sai ta daure still cikin raunin murya na wacce take jin jiki sosai tace,”Daddy, it’s all right, okay,”
“I don’t agree. Let me know if there’s a problem, ko akwai abinda yake miki ne?”
Girgiza kanta tayi kamar yana ganin ta, wasu sabbin hawayen suna sake sauko mata, murya a matuƙar sanyaye tace, “Daddy I’m not feeling well”.