NOVELSUBAYD MALEEK COMPLETE HAUSA NOVEL

UBAYD MALEEK COMPLETE

Babbar masarautace datayi hudu zuwa biyar din delah ta garinsu wadda wannan komai nata ma basai anfadaba kana shigowa zaka kame kanka da kanka sbd Wasa ko laifi kadan saiyayi sanadinka ashafe labarinka.

Komawa tayi ita abiye kawai take dasu afiyan dandai duk tagama Shan jinin jikinta ta kame kanta farhat ce riqeda hannunta Taki saki sbd ita duk Bata wani Saba da kowaba Anan din sai Anneti AFIA ce kawai tasan kowa ta Saba da kowa harma da rayuwar mulkin itama ta iya tsaf Ashe akwai a jininta Dan kuwa take itama ta rikide Takoma li’iliti AFIA UBAYD MALEEK dinta Wanda yasa NURU sake Kama kanta.
Shi maleek ma sunsan ganinsa ayanzu ko su dasuke ‘yayansa abune me tsananin wuya agaresu Dan kuwa ayanzu MALEEK yafi komai tsada da wuyar gani a gizah Dan kuwa tsaron dake hanyar zuwa sashensa ko asalin sashen NEGES (sarki) bai samu tsatsauran tsaro ba Kamar nasa sbd shine asalin MALEEK na kujerar kowa yasan shine sarki kawai dai mulkin baya hannunsane Wanda shine yaso Kuma bai tashi karba bane Dan hakane yasa matuqar MALEEK na gizah to kowane irin tsaro da matakai sun ninku.

Babban sashen dake maqale Dana Anneti mahaifiyar MALEEK anan ne masaukinsu dama Wanda yagama Jin gyaran Jin dadin duniya.
Bayine da masu hidimarsu birjik a qaton babban daki guda dake gefen part din Wanda aka zuba musu gadaje irin na Yan makaranta masu hawa bibbiyu su anan suke rayuwa aikinsu kawai shine duk ranarda iyalin maleek sukazo sune masu hidimarsu.

MAMUH

ZAFAFA BIYAR????????????

Alkiblah–SAFIYYAH HUGUMA
Makauniyar qaddara–BILLYN ABDULL
Dalaal–MISS XOXO
Mabudin zuciya–HAFSAT RANO
Ubayd Maleek–MAMUH GEE

DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN..

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki????????

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)????????

08085405215

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU????????

0903 234 5899[9/22, 8:52 PM] +234 703 598 9527: Mamuhgee 19

Assalamu alaikum, ina masu son su iya baking da decoration na birthday cake wanda idan aka kalla sai an kara kalla????

toh ga dama ta samu er uwa kiyi maza kiyi rigista, sannan zaki koyi ydda ake hada whip cream din da yke daukar awanni ba tare da ya narke ba????????

zaki koyi ydda akeyin vanilla cup cake mai dadin gaske???? er uwa ba’a iya nan muka tsaya ba zamu koya miki ydda akeyin chocolate bar cookie domin farantawa mai gida da baki????

kuma duk akan kudi naira 3500 kacal????????
Online class neh full vedios kamar a gabanku akeyi, tare da note da voice note ydda zaku fahimci komai cikin sauki????

kada kubari wannan dama ta wuceku????
Domin neman karin bayani ki kira: 07089621678
I.G handle: Umsad cakes nd more????


Zama NURU tayi a makeken royal bed dinda yafi Kama Dana kwanciyar mutum hudu zuwa biyar sbd girmansa ga wani irin ado da komai na dakin yasamu kana shigowa komai na masarautar ma kana gani kasan kana cikin palace.
Sake wani marayan numfashi tayi zazzabin daya kamata Yana sake qarfafa ajikinta Dan kuwa itadai batamasan menene matsayin dazata dauka anan din ba,
Shin me Reno?
Kokuwa baiwa?
Kokuwa negestati?to idan negestatin ne to ta wa?

Dafata AFIA tayi tana zare dankwalin kanta dake nade da dogon gashinta ta zauna tana miqar da hannuwanta a gajiye tace”

NURU Yaya dai?
All okay right???

Dan dagowa tayi jiki ba qwari ta kalli afia din saita sauke kanta tanajin kallon afian ido cikin ido yanzu ba nata bane kila kozasu koma yanda suke sai sun koma gida.

Cikin sanyin harshe tace”

Headache ke damuna Amma inaga na gajiyane zai saki idan na huta.

Cikin kulawa afia tace”

Sorry.

Gyada Kai kawai tayi tana sake dauke kallonta daga kan afia din.

Wanka sukai sauya cikin wasu irin dogayen rigunan alfarma wainda aikene na musamman daga sashen Anneti.

Babban makeken palon suka fito har zuwa dining Wanda yake shaqe taf da kalolin abinci da abin Sha tareda snacks da fruits kowanne sai daukan ido yake yanda aka jeresu kaman mutum goma ne zasuci abincin.

Zama suka farhat na gefen NURU sbd wata irin maqalewa data sameta tun zuwansu sbd farhat din nata rashin son shiga mutane masu yawa irin hakan shiyasa ma ko acan dad dinsu ya Hana bayi ko masu aiki da yawa sbd ko bayan farhat shima bayason guri da mutane da yawa komai girman gurin kuwa.

Cikin nustuwa da kwanciyar hankali sukaci abinci suka koshi suka koma Palo suka zauna aka aika da asanarwa da Anneti zasu zo gurinta kawo gaisuwa Nan da mintuna kadan.

Tunda saqon gasunan zuwa sashenta ya iso Mata farin cikinta ya Dada bayyanuwa sbd a duniya idan abinda tafi so da qauna shine MALEEK dinta da ‘yayansa duk da kullum adduarta Allah yaqarowa UBAYD ‘yaya masu albarka sbd tanason ganin zuriar UBAYD MALEEK ta yadadu Amma ga dukkan alamu kila hakan bamai yiyuwa bane sbd matarsa kowa ya lura Kuma ya fahimci batason yawan haihuwa…..Dan faduwa gabanta yayi da tunanin wani zancen binciken NEGES yabayar daya fada Mata yana ganin kaman UBAYD MALEEK Bata tareda matarsa.

Saurin rufe fararen idanuwanta da maleek duk su ya sauko tayi cikin wani irin hali na damuwa me tsanani tace”

Ya Allah ya kabar da wannan zancen akan MALEEK dinta Dan kuwa har abada ko amafarki Bata fatan ace hakan yazama gaskia Dan kuwa sbd wannan zancen da NEGES ya fada matane ciwon zuciyarta ya tashi Wanda tasa aka bugawa MALEEK Dan kawai yazo ta tabbatarda abinda hankalinta ya dagu da jinsa.

Saida afia ta tabbatarda zuwa yanzu saqon zuwansu ya isa gurin Anneti kafin suka dungumo zuwa gurin nata.

Tun a hanya NURU ke sake shiga taitayinta tana sake Kama kanta farhat dai na maqale da ita bayi uku na bayansu.

Fadar tsari da kyawun sashen mahaifiyar MALEEK bamai faduwa bane saidai kawai ace Masha Allah da wannan daula.

A babban palonta na kurya suka taddata suna shiga da sallama dauke a bakunansu Banda farhat data saki hannun NURU tayi gurin Anneti da gudu ta fada jikinta cikin tsananin farin ciki.

Farin cikin ganinsu ya Hana Anneti rufe Baki ta budewa afia hannuwanta ta qaraso da sauri ta rumgumeta tana cewa”

Kemiri nafik’akelewi ya Anneti (I miss you so very much Anneti/nayi kewarki sosai Anneti)

Murmushin farin ciki Anneti tasaki itama cikin yare da muryarta me tsananin taushi da dattako tace”

Masha Allah li’iliti takusa zama Mata agurin me gagaruman sa’a
Ya Allah ya albarki rayuwanku ku duka.
Amin sukace dukkaninsu har NURU dake tsaye Dana farko ta kasa qarasowa.

Idanuwa ta zubawa NURU dake tsaye tana kallonsu cikin burgewa suna hada ido tayi saurin sauke kanta tareda zubewa qasa ta durqusa tana cewa”

Barka da hutawa Anneti.

Har lokacin kallonta Anneti keyi sbd kyawun NURU da yanayin kyan fatarta dake haskota yasa take Mata kallon ‘yar sarautar delah ce ta bude Baki cikin kulawa ta amsa mata tana maido kallonta kan Afia tace”

Wannan wacece??

Cikin sauri farhat tace”

Aunt NURU ce ta Dade agidanmu taredamu she’s family.

Da mamaki tasake kallon NURU tana kallon afia data share zancen Dan batason fadar matsayin NURU na ‘yar Taya zama da aka kawo musu ita wadda su tuni suka dauketa ‘yar uwa ta jini wadda takewa kallon wani bangare na rayuwarta Dan kuwa qaunace me qarfi a tsakaninsu.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button