NOVELSUBAYD MALEEK COMPLETE HAUSA NOVEL

UBAYD MALEEK COMPLETE

Sake zubewa qasa jekadi tayi cikin girma da tabbacin abinda zata fada Kai tsaye tace”

Allah ya qarawa Kaleeb Nisan kwana da lafiya.
NURU negestati ce wadda zance komai nata da yardar Allah yayi abisaga tsarin da kake son Matar MALEEK ta kasance,
NURU jikace Kuma ‘yar asalin amintaccin bayinka da kakanta da mahaifinta,
NURU baiwace me biyayya tareda da’a wadda takaita ga samun ribar zaman rayuwa,
Anneti ce da kanta tayi zabin NURU tazaman Matar aure ga MALEEK wadda zan bada rayuwata akan Anneti Bata yanke komai akan garaje Wanda wannan halin na zurfi da tsaftataccen tunanin daukarsa tayi daga cikin halayen girmanka da adalcinka ya kaleeb.

Jinjina Kai yakuma Yi tareda kallonta wannan karon ya bude Baki cikin gamsuwa da zallar cikar ikonsa yace”

Ahada dukiyar neman auren MALEEK UBAYD zuwaga mahaifinta tareda saqon ‘yantawa ga dukkanin zuriarsu tareda tukuicin zuwa gizah ga dukkanin ahalin Dan halartar auren ‘yarsu.

Sake zubewa jekadi tayi tana miqa tsagwaron godia da kirari tareda fatan nasara da tarin aduoi ga wannan aure harta fice tanayi cikin tsananin farin take da wannan aure sbd har cikin ranta Allah yasanya Mata kaunar NURU take Kuma fatar cigabanta Wanda tun zuwanta ta yaba takuma Yi tunanin kyawu da halaye na gari irin na NURU matuqar ta zama negestatin MALEEK to ko Bai auretaba wata Rana to tabbas saita zamana negestatinsa datafi matansa daraja a zuciyarsa saigashi abin yazo alokacinda Babu zato ba tsammani Dan haka ko minti biyu Bata qaraba aka fitarda saqon kaleeb take aka fara hada dibbin dukiya da tarin zinarai masu nauyi da daukar ido Wanda yasa take maganar ta fito filin Allah zancen auren ya bazu Kamar wutar daji wasu Basu tabbatarba Saida aka Kai dukiyar gidansu NURU yakasa dauka take aka sauya musu muhalli acikin qanqanin lokaci gari kuwa ya dauka tako Ina zancen akeyi wasu na qaryatawa wasu kuwa mamaki da firgici ya hanasu yadda.

Padima dake zaune bakin kofar dakin da aka jere dukiyar neman auren NURU dakuma Wai MALEEK UBAYD Wanda sunansa kawai sukeji kaf delah din Nan kila idan ba kakansaba sai wasu qalilan ance Babu Wanda ya taba ganinsa koda cikin sa’a ne.,
Sam Bata yardaba da wannan zancen tafi yarda da cewan wani dai acan gizah zai auri NURUn Amma badai MALEEK ba Dan kuwa har abada ko ita datake gaban NURU akomai Bata taba kawosa cikin rantaba bare NURU sokuwa wannna masarautar delah ta boyewa su abal ne amma tasan tsohon da take negestatinsace zai aureta Kuma a iya saninta ba ace musu maleek ba da akazo daukarsu negestati.

Kallonta amminsu tayi lokacinda ta fito dayan dakin riqeda hannun meryam daketa tsalle tsalle da farin ciki me tsanani tun jiya da akace Mata zasuje inda zasuga NURUnta.
Da mamaki ammin tace”

Padima tun jiya kin kasa dogon motsi kin kasa kin tsare kofar dakin Nan bayan kinsan Babu Wanda zai shigo gidan Nan idanma sata kike gudu ki kwantar da hankalinki Mana idanma tambaba kike na waye NURUn zata aura ai zamuje saimu tabbatar sbd muma munkasa yadda da abin al’amarin yazo mana a wani irin girmame saidai koma wane munsan wannan babban cigabe da abin farin ciki ga NURU sbd aure abune me girma dazai tabbatarda darajarta.

Qala padima Bata samu cewaba dan kalma daya acikin zancen ammin Bata fahimta ba babban burinta da damuwarta yanzu shine su tafi gizah din tasamu ganin NURU taji komai daga bakinta shine kawai zai Bata kwanciyar hankali tanaji meryam na fada Mata amed na kiranta waje harso shida tayi kamar batajitaba qarshe korata tayi da wani mugun kallo dayasa meryam din tafiya gurin ammi tana waiwayen padiman sbd ganin yau ko gyaran dogon gashinta batayiba Wanda kullum sai tayi gyaransa Kamar wani sarki.

Daga waje Kuma amed ganin Bata fitoba harya gaji da tsayuwa ya juya ya wuce Yana cewa”

Kome Zakiyi wlh sai anci dukiyar Nan Dani sbd rabona ya koka aciki Dan kuwa nasan yanzu tunda Zaki tafi gurin NURU a gizah dukkanin burinkanki kinsamu damar cikasu wlh maqalewa yanzu nafara Miki mutu ka raba komai Zaki samu taredani zamu cisa.


Zaune yake cikin makeken palonsa na quryar sashensa Wanda bayan masu gyarawa Babu Wanda yataba shigarsa ciki Koda kuwa mahaifiyarsace.,
Kyawu da tsarin palon kawai ya isa sanyaka lissafinda bazaka iya kaiwaba musamman sbd komai na sassansa na daban ne Dan zamowarsa MALEEK.
Akaro na biyu ya sake wani boyayyan numfashi Yana sake lumshe fararen idanuwansa dasuka Dan sauya sbd ciwon Kai me qarfi daya damqesa lokaci daya da kaleeb yakirasa ya sanar Masa da aure za’a daura Masa da negestatinsa abisaga umarni dakuma roqon alfarma da neman cika biyayya daga mahaifiyarsa da Bata taba neman wata alfarma daga garesaba ataqaice wannan ne Karo na farko data yanke hukuncin wani Abu akansa tun bayan rasuwar mahaifinsa Yana qarami.
Kaleeb ya sanar dashi an aika komai ankai qarshen komai jibi za’a daura auren Wanda har zancen ya fita shin tayaya zai musa wannan auren da yarinyar datake tamkar ‘yar cikinsa Dan kuwa idanma lissafin yaje daidai afia zata girmeta Koda da shekara biyune ko daya.
Ta Yaya aure zai shiga tsakaninsa da wadda yakewa kallo daya da farhat qanqanuwar yarinyar da batafi shekara gomaba.

Wayarsace tayi haske tana vibrating ahankali ya bude idanuwansa ya kalla wayar ahankali yaga sunan Mr Omar akai dauke Kai yayi tareda mayarwa ya rufe tsawon lokaci ahakan kafin ya bude idanuwan daidai Mr Omar nasake Kira sbd sanin MALEEK dakyau da yayi yasa yake iya kwatanta mintunan sake Kira na biyu idan yayi na farko cikin sa’a kuwa ya daga batareda yace komaiba.

Da sauri cikin girmamawa da kaucewa dogon bayani da MALEEK bayaso yace”

Barka da hutawa MALEEK.
Dama ‘yan media ne sukeson yada zancen…um..um..maganar auren ko za’a sirrantane?duk Wanda ya fitar Kuma mu dauka mataki akansa.

Kai tsaye yace”

Aure Yana boyune???

Jin haka yasa mr Omar cewa”

Allah ya huci zuciyar MALEEK.

Kashe wayarsa yayi ya ajiye tareda Miqewa yayi ciki Dan kuwa kila Babu me sake ganinsa sai gobe idan kaleeb ya iso daura auren Dan yasan zancen yanzu cikin awanni kadan zai bazu koina musamman NEGES da tun jiya yake son ganinsa Amma baya cikin mode dinda zai iya ganin kowa.

Yana daf da shigewa breaking news din auren THE KING OF DELAH GIZAH MALEEK UBAYD ya sauka acikin cikin qatuwar TVn dake palon ya juyarda idanuwansa ahankali zuwa kan time sai kawai yashige sbd Dama yasan media jira kawai suke abasu tabbacin zancen gashinan mintuna uku da zancen harsun sake breaking news.


Qarfe shida na yamma daidai lokacinda zancen auren ya fita adaidai lokacin Anneti tayo aike me qarfi na daukar NURU zuwa wani kebantaccen sashe dake cikin sashenta Wanda Babu Wanda yasan inda aka Kai NURUn har afia kuwa Dan Koda aka tafi da ita afian na bacci Dan ko daki ba’a Bari Takoma ba daga Palo Dan haka Koda afia ta tashi da mummunan labari biyu daya Bata mummunan shock taci Karo na farko tun a waya tasamu labarin auren mahaifinta ta fito a rude saikuma tasamu labarin kebe NURU Wanda kowa yace baisan inane aka kebetaba.

Wayar dad dinta ta nema arikice tafara Danna Masa Kira Bata shiga hannuwanta dukkaninsu rawa suke da qafafunta tana sake Danna Kiran dad dinta Kiran Imran sai shigowa wayarta yakeyi na kakkautawa tana kashewa Dan ayanzu batasan ma a Ina kanta yakeba ta zari takalmi tayi sashen Anneti saidai tana shiga bata samu ganinta ba sbd Wai tana hutawa Bata fitowa lokacin dawowa tayi a haukace ta nema numbern kaleeb ta Danna Masa Kira shima Bata samu damar magana dashiba Yana cikin dakin hutawarsa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button