NOVELSUBAYD MALEEK COMPLETE HAUSA NOVEL

UBAYD MALEEK COMPLETE

Ana cikin hakan kaleeb yaga lokaci nata ja zaman maleek guda baiyi Masa ba Babu mace ataredashi ma’ana Babu gurin sauke buqatarsa Sam Sam ubayd shine jika mafi soyuwa a rayuwarsa Kuma Wanda yakeji cikin ransa fiyeda ‘yayan daya Haifa Dan haka bazaiso wata mishkila ta bangarensaba ko kadan zai Masa shirin negestati yatafi da ita inda yake kafin yafara nazari da duban inda zai samo Masa matarda duniya zata shaida UBAYD MALEEK yayi matarda ko indatake akace matarsa lailah data watsa Masa qasa a ido ta kalla tasan tayi babban kuskurenda har abada bazai gyaruba.
A jiya ‘daya daga cikin amintaccin bayinsa da tun iayayensu nada rai sukai Masa bauta yai tunanin yonas Wanda cikin wainda aka bawa sauyin ‘yanci shikadai ne me ‘ya mace wadda zataso amatsayin negestati…..
wani irin numfashi ya sauke ahankali Yana gyara kishingidarsa akan qatuwar shimfidar babbar dardduma me tsananin laushi dayayi sallah bai tashiba Yana adhkar ya numfasa tareda daukar wayarsa dake gefensa ya Kira numbern daza’ayo Masa Kiran tsohuwar jakadiyar marigayiyar matarsa.

Cikin qanqanin lokaci saigata ta iso akai Mata iso tana shigowa ta zube qasa tana kwasar gaisuwa batareda ya dagoba cikin wani irin iko na tsohon sarki yace”

Akwai sabuwar sauyin ‘yancin bawai ta negestati ‘ya daga wajen bawa yonas ‘dan tsohon amintaccen bawana ilyas gasasshiyar tabbarwa nakeso Kuma a sirrance zancen zaizama kije kidubota da kanki ki tabbatarda igancinta idan ta isa ta zamo wadda UBAYD MALEEK zai iya hada shimfida da ita wadda zai iya tafiya da ita can qasar dayake kafin asamo wadda zata maye gurbin igiyoyin aurensa idan yarinyar Bata kaiba atara bayi Mata azabi wadda tafi tsohuwar matarsa komai a killaceta anan cikin delah afara kulawa da ita Ana Bata gyara kafin zuwansa yatafi da ita kokuma kafin na aika Masa da ita.

Angama Kaleeb me delah me gizah.

Juyawa tayi da hanzari Dan zuwa cika umarninsa cikin sauti me amo taji yace”

Babu Wanda zaisan ubayd maleek ya rabu da matarsa hakama babu Wanda zaisan negestatin ta ubayd maleek ce.

Da saurin ta zube qasa cikin girmamawa da tabbarwa tace”

Duk ranarda wannan zancen yafita ta hanyata na bada kaina acire fansar cin amanar danayi.

Jinjina Mata Kai yayi ta miqe tafice tana sake basa gaisuwa.


Zaune suke jigum jigum fuskokinsu cikeda damuwa da baqin ciki Babu me iya mgn se sautin kukan padima dake fita ahankali ahankali tana roqon abal da ummi dasu yafe Mata tsautsayi ne.

Cikin nauyin zuciya abal ya dago ya kalleta da idanuwansa dasukai jajir kafin ya kalli ummin da ita shita kalla da idanuwanta dake cikowa da hawaye tana maidawa sbd batason zubarwada padima hawaye kada Allah ya kamata da laifin sakasu zubda hawaye abin yamata yawa,
Fahimtar abinda abal ke nufi da kallon dayai Mata yasa ta bude Baki daqyar cikin nauyin nurya data toshe da baqin ciki tace”

Padima mune iyayenki da bazamu taba zabar Miki abinda zai cutatar dake Dan haka kiji tsoron Allah kifada gskiar abinda yake faruwa,
Nice na haifeku duk ku duka Kuma nasan halin kowannenku fiyeda ku kanku tun ranarda akai maganar badake delah zuciyarki Bata amintaba Kuma shine dalilin dayasa Kika Hana kanki sukuni koba haka ba???

Tsit tayi tana Dan share hawayenta cikin jin tsoron anfara ganota takasa dago Kai ta kalli kowa cikin tsananin fushi da baqin ciki abal yace”

Hakane koba haka ba?

A kidime cikin tsoro tace”

Eh Hakane.

Dukkaninsu wani sabon baqin cikine ya turniqesu musamman NURU da hawayenta suka fara gangarowa.

A qyamace ummi tasake jefa Mata kallon baqin ciki tace”

Sbd baqyason abadake delah shiyasa jika bawa wani kanki yayi Miki ciki sbd ki nuna bamu isa dakeba duniyar dakikeso ita Kika saka gaba….

Da sauri ta girgiza Kai tana fashewa da kuka tace”

Ummi kuyi hakuri wlh banda ciki Amma..Amma…Amma tsoron hukuncin kasheku danima idan naje delah aka….aka..aka gano…yasa nace inada ciki sbd NURU ta yarda taje ta yanda Babu abinda zaisamu kowa wlh ummi sharrin shedan ne Kuma….

Wani wawan gigitaccen Mari abal ya sauke Mata guda biyu Wanda yasata zubewa kwance tana hadiye sauran maganar cikin tsananin tashin hankali sbd yaune karo na farko da aka taba lafiyar jikinta.

Kasa mgn ummi tayi sai hawaye sbd sunkasa riquwa yanxu Kam,
Cikin baqin ciki abal yace”

Sbd son ranki Kika siyarda mutuncinki,
Kika ringa wasa da amfani da qaunarda ‘yar uwarki ke Miki harkina qarya da zance me girma na cewar kinada ciki Dan kawai bakyaso.
Kinyiwa kanki padima,
Kinyiwa rayuwarki,
Ban Miki bakiba Amma wannan abinda kikai shine babban kuskure mafi girma dazakiyi danasani akansa Amma tunda ke Kika zaba hakan ‘yar uwarki zataje delah kekuma idan kingama tsare tsaren burikan naki amed din yafito zanmuku aure dashi Allah yabawa kowa alkhairinda yake fata.

Miqewa yayi Rai bace ya fice yabar gidan ummi ma qala batace Mata ba ta miqewarta meryam na riqeda hannunta.
Ba kunya padima ta tashi zaune tana share hawaye duk fushinda za’ayi tasan kowa zai sauko itadai tunda buqata tabiya angama me wahalar.
Kallon NURU tayi zatai mgn NURUn ta miqe batareda ta kalletaba zuciyarta na Mata zafi da radadin abinda padima tai Mata baqin ciki goma da ashirin ga tafiya delah ga abinda padima tayi ita rayuwartama ta ruguje gabaki dayanta sbd shikenan ta tabbata batada rabon zama acikin igiyoyin aure idan taje delah tariga tazama negestati idan ba Allah ne yayi Mata raboba tasamu damar shiga inuwar aure.

Gabaki daya gidan rikicewa yayi Babu me farin ciki bare walwala tundaga ranar sai padima data bushe ido tasakewarta da walwalarta da komai tunda buqatarta tabiya kowama yayita baqin cikinsa duk zasu dawo daidai idan komai yasake wucewa.

NURU ta sauya sosai gabaki daya yanxu batada walwala kullum cikin damuwa da tunani take idanuwanta harsum bushe da kukan tayi tayi tagaji harta daina saidai ido.

Ranarda jekadiyar Kaleb tazo duba NURUn tayi Mata kallo harna qurulla take tagama tabbatarda NURUn itace mafi cancantuwa Nan take takaiwa Kaleb rahoto yabada umarnin afara gyaranta tun agidansu kafin kwanakin daukota su cika.

Al’amari yadawo sabo sbd irin zarya da matakan tsaro da bayin da aka kawo aka zuba a gidan yasa al’amarin yafara bawa kowa tsoro da mamaki itadai padima ko ajikinta matsuwartama ayi ayi agama NURUn ta tafi sbd tsoron karma wani abu ya gitta aqara dawoda abun kanta.

Hankalin iyayensu yafara tashine sbd tunanin wannan tsananta tsaron da matakan dasukai yawa da wuya idanba gizah za’a Kai NURU ba sbd sai ‘da mafi kusanci da sarauta akewa irin wannan taka tsantsan din Amma dai Babu iko ko hurumin tambaya.

Cikin kwana goma sha daya dukkanin Wanda yayiwa NURU kallo daya baya sakewa a qaidance idan ba hakaba hukunci zai hau kansa sbd wani irin sauyi me yawa datayi,
Fatarta ta sauya fiyeda tsammani,
Haskenta ya ninku komai nata santsi yake musamman gashinta dako dankwali baya zama sbd tsantsi ga sutura ta alfarma da aka kawo daga Kaleb Kai tsaye a sirrance.

Ayau tun safiyar jiya take kuka har idanuwanta basa iya gani sosai sbd yaune ranar tarewarta/ma’ana tafiyarta,
Ammi da abal kwana sukai Bata nasihu da rarrashinta ita ammin ma Kamar yanda NURUn ke kuka hake takeyi Daren farko lafiyayyun motaci biyar sukazo daukeda dukiya da abinci tareda sitiru na alfarma wa iyayen negestatin kafin aka dauketa a sirrance tareda mahaifinta yakarata yakaita har gaban Kaleb Wanda yasake narkawa abal din dukiyar tukaici rakiya aka nufi wani kebantattcen sashe na musamman daya gama hada jin dadin duniya da NURUn tareda sabbin masu kula da ita su shida cif cif ha’di da jekadiyar Kaleb Wanda ke sake yaba zabinsu na NURUn.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button