NOVELSUBAYD MALEEK COMPLETE HAUSA NOVEL

UBAYD MALEEK COMPLETE

Ji take kamar ta Ari hauka sbd so take tasamu bayanin abinda tagani take kumaji idan zancen datayine aka dauka da gaske take ake Shirin auren tun anan.
Palo tadawo ta zaune tana neman rusa kuka sbd idanuwanta dasuka kada sukai jajir ta dafe kanta dake neman tarwatsewa.

Wayartace tayi ringing a zabure ta wawuro wayar tana dubawa sai jikinta yayi wani irin daskarewa sbd tsananin sabon firgici da mamakin data shiga sbd ganin sunan””
MUM” baro baro akan screen dinta sai kawai jikinta ya saki tana kallo wayar na ringing harta tsinke Bata iya dagawa Dan kuwa rabon data ji mum dinsu shekarunma batasaniba tun bayana tafiyarta sai yau Wanda tasan dalilin Kiran baya wuce labarin auren dad dinsu data gani a duniya.

Zubewa tayi kan kujera tareda sake kuka Mara sauti tanajin wani zafin mum dinta da duk itace silar watsewar farin cikinsu” i hate you mum”takeson cewa Amma zuciyarta na hanata saidai wani irin zafin mum din takeji,
Babban baqin cikinta biyu ta rusa rayuwar NURU bayan tasan yanda sukeson juna da Imran hakama Imran ta rusa Masa farin ciki uwa uba me gaba daya bazata iya yadda ta karbi wata ba mum dinsuba amatsayin matar dad dinsu Dan haka Dole zatasan yanda zatayi ta Raba wannan auren ko an hadashi sbd kowa yasamu abinda yakeso.


Duk wani gyara da shiri na musamman anfara yiwa NURU shi atake da aka zo da ita Wanda Kuma kala Babu Wanda yake cewa ga duk tambayoyin datake musu sbd ita tsoro da firgici abin yake Bata Dan batasan meyake faruwa duk ta daga hankalinta musamman dataga ire iren gyara na musamman da ake Mata tamkar wata sarauniya Wanda Kuma ta tabbatarda wannan Shirin na aurene kokuma na Shirin kaiwane ga NEGES,to kenen gurin NEGES dinta datake negestatinsa za’a kaita..wasu irin hawayene masu matuqar zafi suka ciko idanuwanta tuno komai ya ruguje kenan daga yanzu a rayuwarta.

DELAH GIZAH ta dauki babban amo na jama’a manyan qasashe da dauloli dabam dabam hadda turawa da larabawa na nesa Dana kusa sun cika gizah damqam shiyasa tsaro da matakai harsunyi yawanda ko matso na Wasa basayi sbd atake zakayi ta bakin ranka sbd matakan tsaron ba dama musamman idan washe gari tayi ranar daurin auren kenan matakan saisunfi tsananta dan kuwa ko yanxu bashiga ba fita a gizah idanba na manyan baqinsuba na daurin aure.

Anneti duk wani farin ciki tana cikinsa musamman datai ido biyu da kyakkyawar fuskar NURU wadda cikin kwana biyu kacal ta sauya sbd tsananin gyara daya maidata tamkar asalin sarauniyar gizah musamman har wani sheqi fatarta keyi tuni tasake bada odar dasa sabon gyaran ciki Wanda zaibadu damar janyo zuciyar MALEEK gareta daga sun kusantu.

Washe gari jekadi na isowa tareda iyayen NURU dasu padima acikin tawaga ta musamman ta kaleeb Wanda Yana shigowa gizah aka rufeta gabaki daya ba shiga ba fita sai bayan daurin aure da qarfe biyun Rana.

Guri na musamman aka sauke iyayen NURU wainda suketa fama da padima da zazzabi me qarfi ya rafketa reras Banda some some Babu abinda takeyi daqyar suka samu tayi bacci kafin sukaci abincin alfarma fiyeda kala goma suka koshi aka kawo kayan Shirin abal dinsu ya shirya masu tafiya dashi suna jira yafito suka nufi can bangarenda za’ayi daurin aure yabar amminsu da sallar nafila tana zuba adduaoin a daura auren Nan lafiya yasa idan akai auren sai mutuwa NURUnta.
Meryam Kuma a zaqe take dataga NURU wadda Babu me ganinta kaf sai mijinta idan tafara fitowa daga maboyarta Wanda wannan al’adarsu ce.

Qarfe biyu aka daura auren UBAYD MALEEK M KALEEB da NURULHUDA ABAL YONAS akan sadakin darhaman zinare Wanda dubban daruruwan hamshaqan duniya suka shaida a masarautar delah gizah dakeda kafaffen tarihin.
Daurin auren yasamu ‘yan farin ciki da Yan sabanin hakan da masu burika daban daban akansa Dana alkhairi Dana sharri.
Maganar aurensa ita ta batarda maganar rabuwarsa da matarsa data fara bulla.

Har yamma tayi lis afia Bata cikin cikakkiyar nutsuwarta Dan haka tanajin saqon fitowa da MUSHRAH(bride/sabuwar Matar sarki/amarya)yagama bazuwa a cikin delah gizah ta shirya cikin qarfin hali da danne damuwarta ta shirya tsaf cikin shigar alfarma ta li’ilitinta tafito Dan zuwa miqa gaisuwarta datake al’ada dakuma Dole Dole ga duk wani Wanda ke cikin masarautar delah gizah fitowa Kai gaisuwa ga duk MUSHRAn NEGES wato amaryar sarki.

MAMUH

ZAFAFA BIYAR????????????

Alkiblah–SAFIYYAH HUGUMA
Makauniyar qaddara–BILLYN ABDULL
Dalaal–MISS XOXO
Mabudin zuciya–HAFSAT RANO
Ubayd Maleek–MAMUH GEE

DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN..

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki????????

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)????????

08085405215

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU????????

0903 234 5899
[9/22, 8:52 PM] +234 703 598 9527: Mamuhgee 21
Tunda aka fito da ita taga sauyi me matuqar girma da mamaki sbd tsaro da girman da ake Bata kamar za’a bauta Mata yasa taji hankalinta ya ninku gurin tashi da firgici saidai sbd a rufe take Babu me iya ganin hakan gashi takasa Jin komai daga bakin kowa bare ta tabbatarda abinda yake faruwa Abu daya data tabbatar shi shine tabbas yau gurin NEGES dinta za’a miqata Wanda hakan yasa idanuwanta masifar cikowa da hawayen tausayin kanta dana im harma Dana afia da farhat dinta da zasu rabu gashi har abada Bata ikon sauya wannan ikon akanta.

Kai tsaye babban sassan MALEEK UBAYD aka nufa da ita Wanda shine yakeda ikon fara ganinta kafin tafito kowa yaganta Dan haka suna Isa tangamemiyar kofar gurinsa masu tsaro suka bude musu sbd tsananin tsaro da securities din gurin masu Kama da samudawa anan kowa ya tsaya daga ita sai jekadi suka shige aka rufo har lokacin Babu kala jekadi Bata ce ba shiyasa batama San da ita ake tareba bare tasan inda suka shigo.

A kofar palonsa na karshe Wanda dagashi saina hutawarsa sai master bedroom dinsa Dan haka daganan jekadi taja gefe ta tsaya cikin bawa NURUn girma tace”

NURU gaki a kofar shiga gurin uban gidanki Kuma mijinki na halak malak Wanda shine zai budeki kafin kifito al’ummar gizah nason sheda ganinki wato mace me sa’a.

Da haka tayi baya ta fice daganan Takoma can farkon shigowa jiran fitowar NURU din.

Kasa motsi tayi daga inda take tsaye sbd firgicinta daya koma zallar mamaki Dan kaman Bata fahimci me jekadin tagama fadaba ta wuce.
Saitaji kaman tace aure?

Girgiza Kai tayi ahankali tareda sauke Numfashi sbd sanin ba hakan bane itada samun arzikin daukar igiyoyin auren wani sai Allah tunda harta rasa igiyoyin auren im tasan aure gareta sai rabo me qarfi Dan tuni take cikin radadin hakan har lokaci da rayuwar data samu a Paris ya mantar da ita komai yanzu Kuma qaddararta tadawo gareta Dan haka ba gudu bare tsira.

Ahankali ta tura tareda saka Kai cikin qofar da jekadi ta ‘dan bude Mata ba dukaba sbd takaitawa NURU aikin bude qofar Wanda badan kofar MALEEK bace itace zata bude Mata ita har qarshe.

Wani irin sanyin AC ne Dana wani qamshi data sani suka fara tarbanta ta maida kofar ta rufe ahankali har lokacin fuskarta arufe take.
Tunda ta iso tsakiyar palon ta tsaya cak batareda ta qara taku ba sbd bugun zuciyarta daya qaru Yana fita da qarfi Dan zuwa yanzu tagama tabbatarda qamshin datake ji musamman data iso tsakiyar palon taji yasake gauraya gurin.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button