NOVELSUBAYD MALEEK COMPLETE HAUSA NOVEL

UBAYD MALEEK COMPLETE

So take ta yaye fuskarta taga inda take sbd firginta daya sake dawowa Amma ba hali sai kawai qafafuwanta suka hau rawa da dukkanin jikinta dama gashi ko abincin kirki tadaina ci kwana biyun sbd tsoro da shakkun datake ciki na abinda yake faruwa
Hannunta dake tsananin rawa ta daga ahankali ta shafo fuskarta dake lullube taji zufan tashin hankalin turaren MALEEK datakeji tako Ina na shiga hancinta take ta lalubo kujera ba shiri sbd jirin dayake Shirin dibarta ta ta zauna akan kejeran cikin rudewan rasa abin,
Dauke wuta tayi atake sbd Jin kusada mutum ta zauna batareda tasaniba rintse ido tayi cikin tsananin tashin hankalin rashin sanin meyene Wai yake faruwa da ita ta yunqura da sauri zata tashi taji anriqe hannunta ta tsaya cak tareda saurara abinda takeji na qamshin MALEEK zuciyarta na harbawa da qarfi kaman zata faso kirjinta.

Lullubinta taji an yaye ahankali Wanda yasata yin qasa da kanta tareda rufe idanuwanta sbd koma wanene bazata iya kallonsa Kai tsaye ba tunda shugabantane.

Tsit gurin yayi Babu wani motsi Babu wata magana tsawon mintuna shida ahakan kafin ya miqe ahankali har lokacin kayan daurin auren ne ajikinsa dasukai Masa matuqar kyau suka sake boye manyancinsa tareda bayyanarda asalin kyawunsa abun Kamar almara Amma har wani kyalli yakeyi Wanda ake cewa na anganci.

Ciki ya wucewarsa batareda yace komaiba,
Har lokacin Bata dagoba saidataji shigewarsa ta bude fararen idanuwanta ahankali ta dago Amma takasa bin inda yabi Koda kallo ne,
Hannunta daya Kama ta dago ahankali takai hancinta gabanta yasake wani irin faduwa,
Duk Wanda ya yaye fuskarka daga fitowarka wankan boyo shine yakeda Kai da ikonka Kona aure Kona negestati,
MALEEK???
MALEEK???

Toshewa kanta yayi gabaki daya Bata fahimci komaiba ta miqe har lokacin qafafunta na rawa ta fito dama wannan al’adace Kuma ancikata tunda ya yayeta.
Tana fitowa kallo daya jekadi Tai Mata ta hangi tsagwaron rudu da firgicewa atareda ita da hanzari ta qaraso gurinta cikin kulawa da girma tayi qasa da murya tace”

Ki nutsu kada ki daga hankalinki taron mutane ne keson ganin MUSHRAn MALEEK.

Cak ta tsaya tareda waiwayowa ta kalli jekadi da idanuwanta da zuwa lokacin tuni hawaye suka fara gangaro musu kenen dai ta tabbata maleek ne hancinta da wasi wasinta yazama gaskia.

Da sauri jekadi ta Kara gabanta ta boyeta tana cewa”

Allah ya taimaki mushrah wannan ba girmanki bane bayyanarda hawayenki agabanmu Dan Allah ki kwantarda hankalinki
Allah kuma ya huci zuciyarki da salama idan bazaki iya ganin kowaba ayanzu ko zamu rakaki gurin iyayenki dasuka zo kifara mgana dasu wannan sakone daga Kaleeb Kuma Yana Tayaki murnar tareda sanyawa aure albarka.

Ita gabaki daya batasan lokacinda kuka yazo mataba ba shiri jekadi ta nufi sashen Anneti da ita Wanda yafi kusa daga Nan din suna zuwa Anneti tace akaita kuryar dakinta abarta ta huta tukuna dama zataji abin wani iri tunda batada masaniyar komai.

Take aka sanar kowa ya tafi NURU tana hutawa bazata samu damar fitowaba yanzu Wanda hakan yasa kowa yafara mamakin irin sa’a da gata tareda daurewa da NURUn ta samu na take al’ada tun aranar farko.

Afia ma Bata datazo yau da mamaki Takoma sashensu sbd Bata samu damar ganin NURU ba sbd dolen Dole abarta ta huta tasamu nutsuwa Wanda itakuma tasan NURU na buqatarta yanzu sbd tayi Mata bayanin kada ta tayarda hankalinta idan sun bar Nan komai zai koma daidai zata samu Imran dinta.

Kuka tayi sosai batareda tasan Kona meneneba itadai yanzu iyayenta dataji suna kusa takeson gani Dan sune zasu Mata bayanin komai ta fahimta.
Sai dare lis ta fito cikin wasu kayan dabam da aka kawo Mata akasa tayi wanka ta sauya ta fito dukkanin abindake jikinta qyalli yakeyi tundaga kayan dake jikin nata har zuwa wata siririyar diamond necklace dake wuyanta ta daqyar ta iya cin abinci tareda Anneti suna gamawa Ana kawo Mata farhat data rikice musu kwana biyu na rashin ganin NURU din tana ganin NURU ta fallo da gudu itama NURU sai lokacin taji Dan damar abinda takeji ta rungume farhat din cikin samun nutsuwa tace”

I miss you sweetie.

I miss you more my Lewa ohhh Anneti tace ke mamanace yanzu bazaki taba tafiya kibarniba kaman mum ko??

Wani dum NURUn taji takasa dagowa ta kalli Anneti dake jinsu hakama takasa bawa farhat amsa ita Tama rasa kunyace ta kamata kome?

Riqeda hannun farhat din suka fito daga sashen Anneti jekadi da sauran mabiyanta uku na bayansu suka nufi gurin iyayenta farhat nata yaba kyawu da sauyawar datayi itadai gabaki daya tafiyar kawai take hankalinta baya tareda ita abubuwa da yawane suke yawo cikin kanta wainda suka girmi tunaninta.

Suna Isa dukkaninsu jekadi daga waje suka tsaya daga ita sai farhat suka shiga bayan an wangale Mata kofar tana shiga aka rufe abal da amminsu dake zaune a Palo suka kallo qofar atare fuskokinsu na bayyanarda wani yalwataccen farin cikinsu daya kasa boyuwa itama kasa motsawa tayi sbd kasa gasgata mafarki take kokuwa gata ga iyayenta bayan wasu shekaru take idanuwanta suka ciko da hawaye suna Shirin gangarowa meryam data fito daga gurin padima tana ganin kyakkyawar halitta a tsaye cikin palon ta tsaya cak taqare Mata kallo ta tabbatarda NURUntace a guje tayo kanta tana Kiran sunanta NURU ta ware Mata hannu tareda dauketa cak suka qanqame juna tana jero Mata yarensu Wanda farhat ce kawai batasan me take cewa NURUn ba.

Daqyar suka saki juna kowanne farin cikinsa yakasa raguwa ta qaraso gurin amminta ta rungumeta tareda riqo hannun abal dinta cikin yare da muryarta me sanyi tace”

Abal ubana nagari nayi kewarku fiyeda komai da kowa nayi farin cikin ganinku cikin lafiya da wadata.

Murmushin farin ciki me sauti abal yasaki Yana dafa kanta yace”

NURU ‘yata tagari munyi farin cikin ganinki cikin koshin lafiya da nustuwar rayuwa,
Bamu taba farin rayuwaba irin Wanda Kika bamu ayanzu na aurenki da muka gani cikin ahali me girma da daraja.

Amminsu kuwa sbd farin ciki takasa cewa komai sai kallon ‘yarta takeyi cikin tsananin so da kauna tareda alfahari Wanda yasa NURUn Jin nauyin iyayenta musamman da abal ya dauko maganar auren yana Mata nasihar hakuri da nutsuwa tareda tawakalli daya santa dasu Kuma yake qara Jan hankalinta dasu akan ta rungumi wannan aure da hannu bibbiyu.

Cikin mamaki ta kalli ammi tace”

Ammi Ina padima?

Ajiyar zuciya ammin tasaki tareda Dan satar kallon abal din kafin ta kalli kofar dakin da padiman ke ciki tace”

Tana can akwance batada lafiya sosai gobema inshallah zamu koma gida sbd aje can abal dinku yasamu maganin Bata Wanda zaiyi Mata tunda ciwon na jiri ne.

Subhanallh”NURU tace cikin damuwa da kulawa kafin ta miqe ta nufi hanyar dakin bayan ta kalli farhat dake maqale da ita tacewa ammi ga farhat Nan su gaisa
Ammin tajawota ta Dora kan cinyarta tana tambayarta tana lafiya?

Tana Isa dakin tashiga Kai tsaye padima dataji zuwan NURUn tasake sassake jiki tana maqale murya tareda qaro nishin ciwonda babusa hadda hawayen da tun safe suka kasa tsaya Mata na abinda ya tsaya ya danne zuciyarta.

Da sauri NURU ta qaraso bakin gadon tana kamo padiman tana Kiran sunanta cikin tsananin kulawa Tama dungumota gabaki daya tana cewa”

Padima meya sameki bayan yau Ina cikin tsananin farin cikin ganinku ku duka.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button