NOVELSUBAYD MALEEK COMPLETE HAUSA NOVEL

UBAYD MALEEK COMPLETE

Jawo wani zance afia tayi ta hanyar cewa Nuru ta qaraso ta zauna acikinsu.
A Dan kakkame ta qaraso Amma Bata zaunaba saita zauna a qasa Yana cewa hakanma she’s ok.

Ganin NURU da farhat yasa Anneti bataiwa afia maganar mahaifiyarsuba Wanda afia ta lura da hakan hankalinta yatashi sosai matuqa musamman batason ayi tambayar gaban farhat Dan zata fada cewar mum dinsu ta Dade da tafiya tabarsu.

Basu bar sashenba sai dare suna zuwa wanka sukai suka kwanta Banda NURU data fara waya da Imran.

Kasa bacci afia tayi tana saqa da warwara,
Babban abin tsoronta anan shine Dole ita Anneti zata tambaya mum dinsu Dan kuwa MALEEK ko sunyi mgnar da Anneti bazai taba fada Mata komai akaiba ita Kuma duk qaryar dazatayi na kawo wani excuse dazatace ya Hana mum zuwa bazai shigaba Dan kuwa Anneti zata gane komai Daren dadewa Dan haka take buqatan lokaci Wanda zatai amfani dashi ta shirya iyayenta kafin agano.

Da wannan tunanin tayi bacci takuma farka,
Washe gari ma agurin Anneti suka wuni saidai Banda NURU wadda ta Kama kanta ta zauna guri daya sbd yawo ba nata bane acikin masarautar gizah ta yayan masu masarautar ne
Sai washe gari dazasu yawon ziyara cikin masarautar zuwa sashe sashe na ‘yayaye da sarauniyoyin gizah shine tabisu saidai tayi danasanin Binsu Dan kuwa sake tabbatarda rashin darajarta tayi shiyasa Bata Kuma gigin binsu ba idan zasu fita acikin gizah din ta Kama kanta ta zauna guri daya sai tunanin gida da iyayenta yadawo Mata Kamar sabo.

Duk yanda Afia ke zamewa Anneti sbd kada tasamu damar yimata maganar mahaifiyarsu yau da kanta taje gurinta Dan tabbatarwa da kaman jita jitan da kaman yakeson fita na rabuwar iyayenta din sbd shekaran jiya da jiya duk sashen dasukaje sai anyi tambayar matar maleek guda ace bataxo duba Anneti ba wane irin uzurine wannan.

Hakan yasa hankalinta tashi matuqa sbd tabbas Kam kowa zaiyi nasa tunanin daban daban ace Annetin delah gizah mahaifiyar MALEEK guda ace matarsa batazo dubata ba tabbas zance yafara bayyana take ta aika sako na musamman ga mahaifinta na cewa akwai karatu me mahimmanci a makaranta sunada buqatan komawa Kuma tana roqonsa daya koma taredasu sbd shine jigonsu bazaso komawaba bataredashiba.

Hakan datayi saiya sake saka Anneti cikin shakka da mamaki sbd sakon MALEEK saiya biyota gurinta yake Isa gurin maleek Dan haka ta aika aje akawo Mata farhat batareda sanin afia din ba.

Agurinta ranar farhat ta kwana da daddare bayan sunyi Shirin kwanciya ta kalli farhat din tana shafa Mata Kai cikin kulawa tace”

Farhat mamanki meyasa bata biyoku ba bayan ga abal dinku dayafita ayyuka yazo dubani??.

Kai tsaye farhat tace”

Mum ta Dade da tafiyanta munata kuka nida afia
Daddy ma da kansa yace idan ta tafi kada tasake dawowa yabata da ita koyaushe.

Wani mummunan bugawa zuciyar Anneti tayi har Saida ta dafe Dan kuwa kiris ne yahana ciwon zuciyarta tashi duk da hakan wani radadin tashin hankali takeji,
Idan dagaske MALEEK yarabu da lailah zancen yafito Babu ta yanda zai karbi mulkinsa Dan kuwa kaf a tarihinsu sarakuna basa sakin matansu wannan wace irin masifa ce.

Cikin tashin hankali tasake sanyaya harshenta tace”

Tun yaushe ne ta tafi?

Tun kafin aunt NURU tazo ne ta tafiyan munata kuka hadda Afia Amma tunda aunt NURU tazo daga delah jekadi takawo Mana ita shikenan muka daina kuka sbd Aunt NURU tana Sona sosai tunda tazo AFIA tadaina damuwa suka zama Best friends tanamun pancakes da komai nakeso Kuma daddy ma tana Masa abinci fa yafi nasu mum Sarah Dadi aunt NURU tafi mum sbd ita Bata barina Ina kuka Kuma tace bazata tafi tabarniba kaman yanda mum tayi idan sunyi aure da uncle Imran ma Dani zata tafi.

Wuta Anneti ta dauke gabaki daya
Numfashinta yafara yankewa tana dannewa,zufa kuwa kaman tana cikin dakin gashin biredi.

Daqyar ta iya daidaita numfashinta ta kalli farhat tana nazartan zantuttukanta daya bayan daya tana fahimtarsu tana kawowa inda farhat tace jekadi takawo musu NURU daga delah sai kawai ta tsaya anan ta shafa kan farhat din tareda kwantar da ita tana Mata addua har tayi bacci.

Palon hutawarta ta Isa ta zauna tareda daukar wayarta ta Nemo numbern jekadi ta Danna Mata Kira.

Cikin girmamawa me girma jekadi ta dauki wayar tareda zubewa qasa tana jerowa Anneti gaisuwa cikin tsananin girma.

Shiru Anneti tayi na mintuna biyu kafin tace”

Jekadi bayanin komai nakeso na NURU yarinyar dake zaune agidan MALEEK.

Tsit jekadi tayi tana juya zancen zufa na karyo Mata cikin tsananin ladabi da girmamawa tayi kasa da Kai kaman agaban Anneti din tace”

Allah ya taimaki Anneti kimun afuwa nafara tambayo izinin fadar wannan magana agurin KALEEB.

KALEEB?” Anneti ta fada ahankali cikin mamaki duk da tasan dama Dole Saida sanin Kaleeb jekadi ke komai.

Katse wayar tayi ta Nemo numbern kaleeb da kanta takirasa.

Kira uku tayi se Ana hudu ya daga cikin muryar girma da mulki take itama tayi qasa da murya tahau gaisuwa cikin tsananin girmamawa tana sake tambayarsa manyanci.

Shiru tayi bayan gaisuwar tarasa ta inda zata faro har Saida yayi gyaran murya a kame yace”

Kiyi maganarki kada ki damu kaleeb zai duba koma menene.

Cikin sanyin murya tace”

Allah ya taimaki kaleeb idan banyi shishigiba inason sanin wacece yarinyar da jekadi takai gidan MALEEK.

Murmushin manya yayi Kai tsaye yace”

Negestatinsa ce sbd ya rabu da matarsa.

Hawaye ne suka ciko Mata ido tace”

Allah ya taimaki kaleeb nagode Allah yaqara girma ina fatan ban dameka ba da Kiran dare danayi.

Bakomai Anneti Allah ya taimakemu duka.
Maganar rabuwar MALEEK da matarsa kuwa kinsan meya dace kiyi qato shiru sbd fitar hakan barazanace ga maleek.

Inshallah kaleeb ngd ahuta lafiya.

Kasa daurewa tayi Saida wasu irin hawaye me zafi suka gangaro Mata sbd wannan masiface agurinta babba.
Ta Yaya zata Hana fitar maganar rabuwar MALEEK da matarsa.

Jekadi takira anan jekadi ta fayyace Mata komai na yanda rabuwar take Wanda yasa ran Anneti baci sai yanzu ne tagano dalilin qin barin ayi maganar da afia keyi sbd Kare mahaifiyarta kada mutuncinta ya zube.
Ko so daya adaren Anneti Bata rintsaba Dan kuwa ki NEGES bazata Bari yaji zancenba tunda zargi kawai yake zata barshi yayita zargin kawai batareda ya tabbatarba.

Washe gari tun qarfe Tara ta aika cewa tana gayyatar su AFIA cin abincin safe a sashenta tareda ita.

Da farko AFIA taji wani Abu na kwanan da farhat tayi acan gurin Anneti Amma da bataji bayani ko ganin sauyi afuskan Anneti ba saita sake abinta Dan ma kada asamu damar yin maganar saita saka NURU shiryawa Dole suka taho tare.

Tunda suka zauna cin abinci Anneti tayiwa NURU kallon sakanni ta dauke kanta ta maida kan Afia dake cin abinci ba damuwar komai aranta.

Suna gamawa NURU ta fice daga sashen gaba daya sbd kallon da Anneti ke Mata yasa hankalinta tashi matuqa tashiga wani irin matsanancin tsoro.

Kai tsaye Anneti ta kalli afia bayan fitar NURUn tace”

Maleek da lailah sun rabu gaskia ne kokuwa???

Wani irin mummunan tarine ya kufcewa afia ta dago da jajayen idanuwanta ta kalli Annetin cikin tsananin firgici da tashin hankali tace”

Aa Basu rabu ba sunanan tare.

Meya hanata zuwa ita?

Sake dagowa tayi dukkanin idanuwanta na qarasa sauyawa cikin dakewa da qarfin hali tace”

Ayyukane sukai Mata yawa tayi tafiya.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button