NOVELSUBAYD MALEEK COMPLETE HAUSA NOVEL

UBAYD MALEEK COMPLETE

Muji pulse dinki.

Bata hannunta tayi ta riqe tana Jin pulse din NURUn tayi shiru zuciyarta na bugawa
Duk Bata yarda ba ta juya da ita kan gadon scanning din dake office din Dr Damien din NURU ta kwanta tana gyara Mata kafafunta.
Tana Dora Mata abin scanning din take cikin jikin NURUn ya bayyana baro baro ta ajiye abin tana kallon NURU da cikakken mamaki da tsoro harma da shakku da firgici duka
Bakinta na rawa Kai tsaye ta fuxgo kalmar cikin tsananin mamaki tace”

NURU you are 7weeks pregnant.

Da sauri NURU ta kalleta tana saukowa daga gadon tana goge jikinta da tissue ta Dora hannunta kan cikinta cikin son tabbatarwa tace”

Pregnant???
Ni¿

Wani irin Murmushin farin cikin da Bata taba tsammanin yiba ta sake dafe cikin tana dagowa ta kalli afia datai mutuwar tsaye tana kallonta cikin mugun mamakin da batasan lokacinda bakinta ya furta”

Dad ne???

Sai alokacin kunyar afia din takama NURU ta Dan takaita farin cikinta tana kallonta ta daga Mata Kai ahankali tana cewa”

Yes wannan qaninki ne afia.

Wani yawun sabon mamaki afia ta hadiye tana sake dulmiya cikin tunani da tsananin mamaki alokaci daya Kuma hadda kunya tana kamata
Daga ita har NURUn sai suka samu kansu da kunyar juna afian tayi saurin juyawa tana zaro takardar scanning din da batama Gama dubawa ta miqawa NURUn ba shiri bakinta na furta”

Congratulations.

Kallonta NURU tayi ahankali tace”
Thank you tana sakin murmushi.

Bakin afia mutuwa yayi murus da mamakin al’amarin dakuma kunyar dad dinta Haka ta raka NURUn har mota Dan Dole itace taja motar tabar gurin aikin ranar saidai Kuma gobe suka nufo gida tana satar kallon NURU wadda farin cikine fal cikin ranta Allah zai Bata ‘da ko ‘yar kanta.

Suna shigowa gidan tun daga motocin maleek dake harabar gidan taga alamun an sauya musu parking wanda hakan ke nuni da yadawo kenan
Cikeda murna ta fito motar tana mantawa da komai ta nufi hanyar office dinsa na cikin gidan dayake aikin office aciki sbd hango Mr Omar agurin tasan Yana can Dan Haka ta nufi gurin cikin tsananin farin ciki da murna.

Tsaye suke daga bakin kofa tareda baqinsu ‘yan China dasukazo wani aiki harsun Gama magana sun fito kenan zasu wuce ya hangota tana tahowa
Sanin sabon daya koya Mata da yanayin yanda take tahowar ya tabbatarda abinda zai faru ya hadiye wani ‘dan yawu ya waiwaya ya kalli Mr Omar Wanda take yagane kallon ya matso Yana washewa bakin Baki Yana nuna musu hanya da cewa”

chairman Zhou let me see off please?

Gyada Kai sukai suna sake bawa maleek hannu suka tareda Mr Omar zuwa gurin motocinsu da securities ke zagaye suna jiran fitowarsu.

Da gudu ta qarasa qarasowa ta fada jikinsa tana Dora bakinta kan nasa ta bashi wani lafiyayyan kiss daya sanyashi dagota ya kalli fuskarta kafin yasake maida fuskarsa yayi kissing din lips dinta Yana fidda wani lafiyayyan murmushin dayasa afia kusan suman tsaye sbd Bata taba ganinsa akan fuskar dad dintaba
Ita gabaki daya daburcewa tayi ganin abinda idanuwanta suka ganar Mata wato dai ba yanzu bane al’amarin ke faruwa sbd komai data gani ya nuna dad dinta ya dade da tsunduma wata sabuwar daddadar rayuwa hakama NURUn.
Wayyo Allahna” tace tana juyawa da sauri zata bar gurin sbd ita duk kunyar komaiba ya rufeta Jin take Kamar ta nutse a qasa
Tana juyowa saura kadan suyi Karo da Mr Omar da shima yake tsaye agurin Yana jiran sugama soyewar ya qarasa.

Kallon kallo sukai itada Mr Omar dake sakin murmushin Haka yakeson ganin megidansa ya sake kallon gefen su maleek din ya juyo ya kalleta da ido yayi Mata alamar tasake waiwayawa tagani
Ta juya ahankali daidai lokacin NURU ta Dan daga duga duganta takai bakinta kan kunnensa daya rankwafo yana riqeda qugunta cikin rada tace Masa”

Nenyì Irìguzí (Am pregnant).

Wani irin Abu yashigesa ya dagota ahankali yana kallon cikin idanuwanta da ido yake tambayar” da gaske??

Kai ta gyada tana zagayo da hannuwanta qugunsa tana cewa”

And I missed you yau duka bani muryanka ba.

Dago fuskarta yayi ya hade bakinsu yabata wani irin lafiyayyan kiss daya sata kallonsa a kasale tace”

Are you this happy??

Kamar yaro haka ya daga Mata Kai Yana kamo hannunta suka nufo ciki
Afia da Mr Omar sukai saurin barin gurin har suna ture juna tayi saurin fadawa Palo ta nufi dakinta da gudu tana cewa”

Heyyyy
NURU kin wuce tunanina
Dad kuma bazan iya cewa komaiba sbd yau Naga asalin MALEEK da bakowa zai taba samun damar ganiba sai su Mr Omar ‘yan kullum da kullum din MALEEK.

Suna shigowa dakinsa suka wuce Kai tsaye acan aka qarasa sauran murnar da farin cikin cikin Wanda yasata mamakinsa Dan Bata dauka yanada sauran son haihuwa har hakaba.

Sai dare gurin cin abinci Afia tasamu ganinsu lokacin ba kunya NURU tayi wanka tana sanye da wata lalatacciyar riga Mara tsayi Sosai gashinta daure tsakiyar Kai kaman baby shikuwa akai akai idanuwansa na kanta
Duk sai taji abin wani iri saidai Kuma farin cikin data gani taredasu din ya tabbatar Mata da ba qaramin so sukewa juna ba
Ta ajiye spoon dinta ahankali ta dago ta kallesu cikin farin ciki tana murmushi tace”

Congratulations dad you are having another child Allah yakawo manashi lafiya.

Murmushi yasake Ya kalli afian yace”

Thank you princess Afia.

Da ihu farhat tayi kan NURUn tana cewa”

My aunt zata haifamuna baby me kyau kamanta.

Murmushi NURU tasake tana kissing kumatun farhat din.

Tun daga dining din Babu Wanda yakuma ganin NURU sai washe gari da safe dasuka fito cin abinci sai alokacin afia tabada shawaran NURUn tafara ganin likita musamman akan jirin aikuwa ba Bata lokaci Mr Omar dakejin kaman ya taka kan jariri yakira Dr Damien yazo har gida ya duba NURUn daganan yafara zuwa dubata akai akai.

Lokacinda su abal dinta suka samu labarin cikin hadda sadaka ammynta tayi meryam kuwa tuni tafara takura tanason zuwa gurin NURUn saigashi kuwa maleek da kansa yasa jekadi taje har Delah ta daukota dama Kuma itama jekadin tana Shirin zuwa ne harsai NURUn ta haihu.

Zuwan jekadi da meryam da sati biyu maleek ya dauketa suka tafi Maldives inda sukai zamansu acan suna hutawa Saida cikin yashiga wata na budu kafin suka dawo lokacin anfara maganar auren afia Imran Wanda tun kafin suyi tafiya dad din Imran din ya nemesa yayi magana da afia tace da amincewarta take yace ya Basu aka tsaida Rana.

Imran yadawo Paris gabaki daya da lailah sbd gidansa a Nan Paris yake bazai zauna gidan mahaifin matarsa ba ba girma bane Dan Haka murna kan murna agurinsu NURUn da afian sbd bazasuyi nesa da juna ba take aka hau Shirin biki gadan gadan musamman uwar amarya lailah da ba laifi yanzu ta warke harta fara komawa ayyukanta zata fara daga farko Dan ma a qarqashin kamfanin dad din Imran din take aiki.

Sosai akai shagali a gizah na auren afia din Wanda hatta iyayen NURU sun halarto tareda kaleeb sosai tayi farin cikin ganin iyayenta Suma sunyi farin cikin ganinta musamman cikinta daya fara tsufa a gizah kowa yasan MALEEK na gaf da samun magaji kila suke fata.

Padima dai ba laifi tananan sama sama wani lokacin kalau wani lokacin Kuma abin ya Dan juye ahaka aka gama bikin suka tattara suka dawo Paris afia ta tare a babban gidan mijinta Wanda mum dinta take sashe guda na musamman da Imran din ya ware Mata.

Ranarda afia tacika wata hudu cif da aure ranar nakuda ta tasowa NURU
Maleek ya tattara mulkin da sarautar ya ajiye suka dunguma zuwa asibiti sbd ganin gidan zata wahala bazai iya jure ganin hakan ba
Saigashi cikin ikon Allah suna Isa ta haifi qatoton jaririnta me Kama da farhat sak.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button