UWAR MIJINA COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINA COMPLETE HAUSA NOVEL

Tsawon awannin uku ya kwashe yana abu daya,kafin ya kamkameta yana sakin wani marayan kuka,shi kuka ita kuka,kanta ya hau shafawa yana fadin”Allah yayi miki albarka Zahirah ya rabaki da sharrin duniya dana lahira yakuma albarkaci rayuwarki”Yafada cikin Farinciki da zubowar kwallah,tana jinsa ammh bata da damar mgana saboda kowani gaba na jikinta ya saki,ga wani azaba dayaje ratsa ta ta kasanta kamar anzuba mata barkonu,fuskarta kuwa tayi shabe shabe da hawaye wanda har ya bushe tana ji ya fada tiolet yayo wanka,tana kuma kallonsa ya shimfida sallayyah yahau sallah,bayan ya kammallah ya dade yana addu”o”i kafin ya koma ya kwanta,kara jawota jikinsa yayi bayan ya rufesu da blanket,tana ji Numfashinsa yafara sauka alaman yayi barci kenan,itakuwa ta kasa domin wani zazzabine ya rufeta motsi kadan da tayi zai sake kamkameta kamar wani zai rabasu.Dole ta kyalesa bayan ta kara nitsa kanta bisa karjinsa tana sakin ajiyar zuciya kanta kamar zai tsage gida biyu.

Karfe 5:30 ya farka na asuba sakamakon yadda bargon da suke rufe dashi ya dau dumin jikin zahirah a tsorace ya kunna hasken dakin yana binta da kallo,lokaci daya gabansa ya fadi,ganin yadda take kwance shame shame kamar gawa,Numfashinta ne ke fita awahale,ga jini duk yabata zanin gadon da suke kai,cikin rudewa ya shiga girgizata yana fadin’Innalillahi..Me nayi kenan,Zahirah”Yakirata yana dorata bisa jikinsa,dakyar ta bude ido tana kallonsa,bakinta ya bushe tashi takeson yi ammh takasa saurin Rumgumeta yayi yana fadin’wayyo ni Mu”azzam menayi kenan,nakusa kashe Farincikina dakaina..”Yafada idanunsa sun kada ganin yadda ya rude ne yasa tayi karfin hali cewa”Don Allah Ya mu”azzam ka kiramim mama.”,Tafada tana kama hannunsa kallonta yayi yana damke hannunta kamar zaiyi kuka yace”Naji miki ciwo ko,bari kiyi wanka muje asibiti..”Girgiza masa kai tayi tana fadi dakyar”Karka damu kakiramin ita babu mtsala insha Allahu..”jin haka yasa ya ijiyeta bisa filo ya fice da Sauri kamar zai kife,tsausayinshi ya tsirgamata lokaci daya taji bata damu ba halin data ke ciki ba,tafi murnan ta mallakama mutum mafi daraja abu mai daraja agunta,lokaci daya taji gabanta yafadi data tuna Da Ummi,saboda Tasan sun deboma kansu ruwa dafa kansu ne matukar Ummi tadawo Ta fahimci miya faru,kila sai ta kusa kasheta.

Su karimr suna kwance adaki sukaji bugun kofan shashensu,Lami da itace bata da wani Nauyin barci ta mike tana tashin su Uwanj,suma aruden suka tashi,suna mamakin waye haka da asuban fari,Lami ce tayi karfin halin budewa,tako rude data ga yallabai tsaye da jallabiya hankalinsa tashe,kafin ma tayi mgana yace”Ina baba take? don Allah tazo zahirah ce bata da lafiya tace akira mata ita”Jin haka yasa karime dake bayan lami ta fito dafe da kirji tana sallallami,bai samu zarafin kara mgana ba yajuya itakuma tabi bayansa,su uwani basu bisu ba,tunda basu aka kira ba,daki suka koma suna mamakin wani irin ciwo ne haka farat daya,ammh daga wani barayin na zuciyarsu kamar suna kawo hasashen aikan aikan da yallabai yayi,ammh basu da tabbas.

Koda karime Ta kalli Zahirah dake kwance takasa tashi,kallo daya tamata ita da zanin gadon ta fahimci komai ke faruwa,dan mirmishinsu tayi na manya tana kallon yallabai yadda ya tarairayota jikinsa yana jeramata sannu,Wucewa kawai tayi tiolet ta hadamata ruwan zafi mai zafi takasa gishiri aciki tana Fitowa tace”Yallabai bari na shiga da ita bayi,insha allahu xata samu sauki”Kallon karime yayi yana fadin’Da gaske baba,kodai bazaki iyaba muje asibiti”dan mirmishinsu tayi na manya tace”Ko daya yallabai,ai haka kowacce mace mai daraja take fuskanta daren farkonta”Tafada tana dan sukunyar dakai,Fahimtar inda ta dosa ne yasa shima yaji kunya kawai sai ya basar,shi ya taimakama karimen suka kaita tiolet din,fitowa yayi yabasu waje,tunda Yagane Karime,Ta gano aikin da yayi.

Wai karime tasha fama da zahirah kan shiga ruwan zafi,sai da tasakamata karfi ne kana ta zauna aciki,runtse ido kawai takeyi hawaye na shatata,ruwa uku tana chanzamata,kuma ba laifi taji dadin Ruwan har jikinta yasaki daga Nauyin dayayi mata,dariya kawai karime take mata tana ayyana ranar da zata haihu,kenan akwai jarfa.

  Barota tayi tayi wankan tsarki itakuma takoma ta nado zani  gadon,bayan ta shimfida mata wani,tanan tsaye sai ga Zahirah ta fito tana taku a hankali kamar wacce akama kaciya,Rikota karime tayi tana fadin"Diyata ki kamma jikinki fa,ke mace ce,watarana ma haihuwa zakiyi,kinso mai gaddama ni,shiko yakasa hakuri ya shigeki da karfi,har ya jmiki rauni..'jin haka yasa zahirah dukar dakai tana tura baki dariya karime kawai tayi mata bata karamata zencen ba,ita ta taimakata ta shafamata mai ta,tayata tasaka wata doguwat riga ta shimfida mata darduma takabart sallah,itako toilet din takoma ta wanke zanin gadon tsaf ta shanyamata,koda ta fito bata idar da sallahn ba,sai kawai ta fice.

Allah sarki bawan Allah,yana falo yana safa da marwa,ganin fitowar karime yasa yanufeta da sauri yana fadin”Ya baba,ya jikin nata yanzu”Mirmishi tayi mai tana fadin’jiki Alhamdulillah yallabai ka shiga ka ganta na barota tana sallah ne”jin haka yasa yayi ajiyar zuciya yana fadin”ngd baba,Allah ya saka miki da alheri..”Da Amin ta amsa harta sakai zata wuce yakirata”am nace ba..”Ta waigo tana Saurarensa gyara tsayuwa yayi yana fadin”Baba wata alfarma nake nema..’tace” Namefa yallabai..”yace’Ina son Abunda kika Fahimci ya Faru tsakanin nida Zahirah kibarsa iya mu uku,don Allah bani son ko su uwani su sani,balle lbrin yakai kunnan Ummi don Allah..”kauda kai Baba tayi tana fadin”Ashhh yallabai ai dana zama uwar banza,kuwa,Insha Allahu hakan bazai Faru ba.”gyada kai yayi yana murda handle din bedroom din.

Yana Shiga ya isketa tana ninke sallaya saurin karisawa yayi ya rumgomota ta baya yana sakin ajiyar zuciya,numfashi taja tana Runtse ido,Juyo da ita yayi yana kallon idonta itakuwa ganin haka sai ta sadda kai,hannu yasa ya dagota yana fadin” Hirata.. Yafada yana kokarin saka idonshi anata ammh taki yarda saboda kunya,mirmishi yayi yana fadin”Ki yafema Yayanki,kuma mijinki,domin yakasa control din kansa yakusa miki illah,kidin ce wlh dabam kike,dadinki ya zarce marubuci ya rubuta sai dai kawai wanda ya tsinci kansa aciki..”yafada yana dage mata gira daya.

Fadawa tayi kirjinsa cikin kunya tana dan dukansa da hannu tana mai kukan,shagwaba Rumgumeta yayi yana dariya yake fadin”yauwa kokefa sai yanzu naji hankalina ya kwanta dana ga dariyanki,yar amaryata zumata..”Yafada yana tura kanshi kamar zai shige hijabinta,Cak yadagata bai direta ko”ina ba sai kan gadonsu,gyaramata kwanciya yayi kan jikinsa bayan ya zaremata hijabin jikinta yake fadin”Oya mu koma barci,kinsan jiya baki barmun Mun runtsa ba..”yafada cikin dakewa,Saurin dagowa tayi tana hararansa,yar dariya yayi yana fadin”Karya nayi..”,yafada yana kallon kwayar idonta..ganin kallom dayakemata ne,yasa takara dunkule kanta bisa kirjinsa tana dariya ganin wayon dayayi mata,shima dariyan yakeyi yanajin wani Nishadi aransa Fadi yake”Nagode ma Allah,nakuma godema Baffa,da dayabani Aurenki danaki karba,dana TAFKA KUSKURE…” itadai tana jinsa sai sakamata albarka yake har barci ya kwasheta.

karime ko tana Fita,takoma dakinsu tayi sallah su Lami yamai jiki kawai suka tambayeta tace da sauki,dayake suma ba masu surutu bane,kichen tafada tahau yima zahirah ferfesun kayan ciki wanda yaji citta,sai Ferfesun kan sa datayi,mata da fanten wake dayaji hanta da allayahu,dauka tayi takai har falon Zahirah,duk da lokacin basu tashi ba,ammh takai ta jera,suna tashi suka ci karo dashi hakika mu”azzam yaji dadi kwarai yadda karime ke kula da zahirah,shi ya mtsamata taci,ferfesun sosai da faten wake saboda dama tana so,hka dai ranar mu”azzam ya wuni lallashi,ita bataje mkranta ba shima baije aiki ba,toya zaiyi Tunda shi ya ballo aikin.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Leave a Reply

Back to top button