BABBAN YAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

Taji shiru, tasake cewa “Hello my Dear…” nanma taji shiru Sai alamun ma kokawa dataji anayi tacikin wayar, kasa kunne tayi taji Babban Yaya yana cewa “Kibani wayata nace….”
Waheeda ta hanashi Sai dariya take, tana tsaye akan gadon shikuma yana tsugunne bai tashi tsaye ba, cikin dabara yariqo Hips d’inta da duka hannayensa, cikin dariya tayi baya zata fad’i saiya tareta tafad’o qirjinsa, breast d’inta Wanda ko bra babu, yasauka akan fuskar sa, cikin ransa yace “Ya Salam…….wayyo Allah nah….”
jiyayi gaba d’aya jikinsa ya mutu, yaso ace yanada Dama da saide yasake rungume ta a qirjinsa,zaiso ace yasake cusa Kansa acikin nashanunta, lokaci d’aya yana yinsa yafara sauyawa
Daurewa yayi, yayi ta maza sannan ya qwace wayarsa, yasake ta tafad’a kan gadon tana dariya, wayar ya kalla yaga har anyi minti uku da d’auka…. Ba tareda yayi magana ba yakashe wayar
Daga d’ayan bangaren Ummi tasaki ajiyar zuciya cikin bacin rai tace “Kan ubancan!, da wacce shegiyar yake tare? Ni za’a nunawa bariki?” 🤥ðŸ˜
1/28/22, 20:50 – Ummi Tandama😇: WN
Sake Kiran wayar Ummi tayi, Amma Naufal yana Gani yayi mursisi yaqi dauka, saima wuta daya kashe, yayi shirin bacci, saboda gaba d’aya yanayinsa ba daidai yake jinsa ba
Waheeda ma fillo taja zata kwanta akan gadon, yana jin alamun kwanciyar ta kamar an tsikare shi yayi sauri yatashi zaune, yace “mezakiyi?”
Kallan sa tayi cikin duhu tace “Bacci mana Babban Yaya”
“ok” abinda yace kenan, sannan ya sauko daga kan gadon ya shimfid’a wani blanket Mai laushi, yaja fillo d’insa ya kwanta, yana d’auke fillon Waheeda taga wannan dairy din, batayi masa magana ba saida taji shiru alamun yayi bacci sannan ta d’auka tafara bud’ewa, ‘Dakin yayi duhu bata ganin komai,saita janyo wayar Ummah ta haska tafara karantawa, shafin farko Zanan heart ne ajiki, yayi kyau sosai Zanan,har ya d’auki Hankalinta sosai, shafi na biyu ta bud’e tafara karantawa inda ya rubuta (Rayuwa Mai sauyi,a koda yaushe zata Iya sauya Maka, daga qaddara Mai kyau ko marar kyau,akoda yaushe qaddarar mutum tana iya sauyawa,banajin zan’iya rayuwa ba tareda itaba, Abaya kafin zuwanta komai nawa cikin nutsuwa da kwanciyar Hankali nake yi, tunda tashigo cikin rayuwa ta, komai ya sauya, Abaya Ina rayuwa ne tareda ‘yan’uwana cikin kwanciyar Hankali, haihuwar ta ne…… “
“mekikeyi ne bakiyi bacci ba? “
Waheeda ta tsinci maganar Babban Yaya, cikin sauri tarufe littafin ba tareda ta qarasa karantawa ba
Tasowa yayi ya d’auke Dairy d’insa, sannan yakoma ya kwanta, fatansa d’aya, Allah yasa bataga komai ba
Itama rufe wayar tayi tareda Lumshe idonta, akan me yake magana? Wacece wannan d’in? Yace mata me kama da’ita yakeso, but yanzu akan wa yake magana? Kanta ne ya d’aure gaba d’aya
Shima anasa 6angaren kwata kwata yakasa nutsuwa, yana tsoron ace taga abinda ya rubuta, ahankali yayi maganar qasa qasa yace “Kin karanta?”
Kamar daga sama ta tsinci maganar tasa, girgiza kanta tayi kamar yana ganin ta tace “A a”
Beqara cemata komai ba, itama haka, kasa runtsawa yayi saida yaga tayi bacci sannan yatashi yayi toilet yayi wankan tsarki, sannan ya 6oye dairy din yakoma ya kwanta
Washe gari yariga ta tashi, lokacin data tashi bata ganshi ba, Dakin ta gyara tayi wanka, tasaka wani Riga da wando data Gani acikin kayan daya siyo mata, kayan taketa juyawa tana mamaki Babban Yaya ne da Kansa yasiyo mata wannan kayan?shida baya son su dinga yawo babu hijabi Amma shine da siyo wannan kayan?
(hmm yo bashi za’a sakawa ba🤣)
Wandon crazy ne, Amma yagar jikin batada yawa, Sai Riga marar hannu yar qarama wadda da kadan ta wuce mata cibiya, Bayan rigar kuwa abude yake, Amma gaban rigar wajan breast din a rufe yake, mamaki ne yakamata sosai, haka tayi parking gashin kanta, tadauko bra din data Gani a kayan tasaka, tayi mata cif kamar Wanda ya gwada ta, ko Yaya akai yasan size dinta? 🤔
Saida tagama shirya wa tsaf sannan tafita falon, tad’an gyagygyra, daga Nan tayi kitchen tafara hada break fast, tana cikin soya qwai yashigo kitchen din, abakin kofar kitchen din ya tsaya tareda rungume hannun sa yana qare mata kallo tundaga sama har qasa, hips dinta yafi komai daukar hankalin sa, kayan sunyi mata kyau jiyake kamar yaje ya rungume ta, wayarsa ce tayi qara cikin sauri Waheeda ta juya, tana ganinsa tasaki ajiyar zuciya tace “wallahi harna tsorata”
Bece da’ita komai ba Sai falon daya koma ya zauna, ya dauki wayar cikin farinciki, dimple dinsa har lotsawa suke, yace “Anty na takaina”
Hajiya Anty tace “Sai yanzu kaga damar bude wayar kenan, Ina Waheeda?”
Kitchen din ya kalla sannan yace “gatacan tana hada mana breakfast, wallahi anty naji dadin tafiya da yarinyar Nan, kinga da, duk lokacin da zanyi girki da kaina, to Bana fita ball, saide in zauna agida, inyi shara, inyi mopping, inyi wanke wanke, in goge kwanukan, sannan na maida su kitchen, Kai Ina shan wahala fa “
Hajiya Anty tayi shiru tana mamakin yanda Babban Yaya yake cikin farinciki, shida ba gwanin surutu ba, Amma Sai zuba yake kamar kanya, ajiyar zuciya tayi tace” kaide kawai kace sakalci ne yayi Maka yawa, idan kana shan wahalar aiki Aida tuni kayi aure “
Cikin shagwaba yace”wayyo Allah Anty kidena maganar auren Nan Dan Allah, yanzu de yakike? Ina Ummah? “
“Ummanku tana nan lafiya, Nima kira nayi in tabbatar Kuna tareda Waheeda ne ko bakwa tare? “
“muna Tare Anty”
Tace” to shikkenan, kakula da’ita, zan tafi hospital Sai anjima “
Sallama sukayi, adede lokacin Waheeda ta ajiye musu abincin, tana zama taji wayar Ummah tana ringing, tashi tayi tatafi Dakin da gudu saboda kar wayar ta katse, Babban Yaya yabita da kallo yanda Hips dinta suke rawa kamar da niyya take kad’asu, wani irin yawu ya hadiye, sannan ya kunna TV danta dauki Hankalinsa
dubawa tayi taga Didat ne, murmushi tasaki sannan ta zauna abakin gado tareda daukan wayar”Yaya Didat….”
“Ina kika tafi nazo gidan akace bakya Nan?”
“wallahi Bana Nan Ina England tareda Babban Yaya”
Yace “what! mezakiyi acan? Kuma kirasa dawa Zaki tafi Saida namiji?”
Cikin rashin fahimta tace “mekake nufi?”
Kansa yadafe da hannun sa, sannan ya seta Kansa yace “kiyi hakuri Waheeda, inada kishi ne, please Wai yayanku yaushe zaiyi aure ne?”
Tace “menene hadin aurensa da soyaiyar mu?”
Wayancewa yayi yace “haba My dear, Yaya nanefa kamar yanda yake yayanki, laifi ne danna tambaya yaushe zaiyi aure? Ai abun farinciki ne”
Murmushi tasaki taji dadi yanda ya dauki yayanta, tace “yakusa aure, ansaka rana nanda wata uku, Amma ba’a tsaida date ba, Sai ankai lefe”
Wata irin wawuyar ajiyar zuciya ya sauke da yaji komai, sannan ne yasa ki ransa suka gaisa sosai, yasake fada mata takula masa da kanta, sannan sukai sallama Takoma falon suka fara break fast itada Babban Yaya
Suna gama cin abinci yafita, baidawo gidan ba har dare, haka ta wuni ita kadai, idan ankira wayar Ummah bata dauka, bataga Kiran yanbiyu ba, tasan cewa sun tafi Saudia, kamar yanda Babban Yaya ya fad’a
Kallo suke cikin kwanciyar Hankali, baya tareda wata aba Wai ita damuwa, asalima yau yabuga Ball wadda bai taba jin dadinta kamar yau ba.
Acan Nigeria kuwa, Su Hajiya Anty da Uncle Usman suna gidan Daddy, babu kowa a gidan duk sun tafi Saudia, Sai iyayen su kadai, Kallan labarai suka gama yi, Uncle Usman ya sauya Tasha, anan yaga Babban Yaya yana buga Ball yanda ransa yakeso kamar ba shine yake qunci saboda ance za’a bashi Ummi ba, Murmushi yayi ya kalli Hajiya Anty yace “kinga d’an wajanki fa”