BABBAN YAYA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

BABBAN YAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

“Alhaji yarinyar Nan ta wahala, dazu saida doctor ladi tayi mata dinki wallahi,anbata hutun kwana goma, saiya Bari saita warke”

Uncle yace “har kwana goma? Ke bakya tausayin Yaron ne? Shekararsa nawa babu aure? Kibawa yaro matarsa yaje yaci gaba daga inda ya tsaya, saiki ja masa kunne kawai”

“ni nace karyayi auren dawuri? Ina barinsa zaije ya lalata mata dinki, yaje yakoyi haquri”

“a a wallahi, idan yashiga wani Hali fa, ke bakyajin tausayin sane, mutum da matarsa, ai Shima yasan yanda zai lalla6ata ko”

“Alhaji, bafa zan bashi yarinyar nanba, abarta ta warke, koma me zaiyi yaje yayi, daga lalla6awa ai zai zarce, yarinya duk tayi fari ta d’ashe rana d’aya saikace Mai ciki”

“to shikkenan, Allah yabata lafiya”

Hajiya Anty tace “Amin”

Wasa wasa saida Waheeda tayi kwana Tara, Hajiya Anty takafa ta tsare babu abinda Babban Yaya yayi mata, duk wani motsinsa akan idonta yake yinsa, har so yake ta shirya ko zataje Asbiti Amma yaga shiru, ashe hutu ta dauka saboda kula da Waheeda, acikin kwanakin Nan hauka ne kawai baiyi ba, wata irin sha’awa yakeji tafitar Hankali, idan kayi masa magana ma jinka kawai yake, Amma ba fahimta yake ba😂

Ranar data cika kwana goma yana idar da sallar asuba yabar uncle a masallaci ya dawo gida, yana kwanciya yaji mararsa ta riqe, tashi yayi ya dinga zagaye Dakin har gari yayi haske, futowa yayi daga d’akin yanufi Dakin Hajiya Anty Kansa tsaye, yana shiga yaga Waheeda tana bacci, Anty Kuma tana toilet, hannu yasaka ya d’auketa cimak, tana bacci taji anyi sama da ita, cikin sauri tabude idonta, tana ganinsa ta zaro ido, hannu yasa yarufe mata baki, Bai tsaya ko’ina ba Sai dakinsa, akan gadon ya dorata, cikin sauri tatashi zaune tace “Babban Yaya….”

Kafin tayi wata maganar ya katseta, yace “nifa ba komai zan miki ba, kawai duminki zanji”

Yana fadar haka yacire jallabiyar jikinsa, Waheeda tana ganin kyakykyawar qirar jikinsa, gabanta yafadi, saboda tasan zaiyi wahala yayi abinda yafada, idonta ne yaraina Fata, tayi tsilli tsilli akan gado, shi Kansa daya kalleta tabashi tausayi sosai, to Amma Yaya zaiyi?

Gajeran wandonsa yacire, cikin sauri tasaki ihu tareda rufe idonta, qarasowa yayi kan gadon yakama hannun ta yabude fuskarta, cikin sigar rad’a yace “bazaki kalleni ba?”

Hawaye ne yazubo daga idonta, ita Kuma qaddarar ta kenan, ta auren yayanta, gashi yana mata abubuwa masu wahalar Fassara, girgiza masa kanta tayi
tareda runtse idonta, hannun sa yakai Bayan ta yacire mata Zip din rigarta, tareda cire rigar gaba daya yace “meyasa? Ni kike tsoro?”

Girgiza masa Kai tasakeyi, yace “to bude idonki ki kalli abunda yasaki kuka rannan, niba nine nasaki kuka ba, shine, yakamata kiyi masa hukunci Mai tsauri”

Cikin ranta tace nashiga uku na da wannan mutumin, ahankali tace “Babban Yaya Dan Allah kabari, Anty fa zata Iya shigowa, kabarni in tafi please, Allah tsoro nakeji”

Cikin wata irin sha’awah yace “bazata shigo ba”

Tace “Allah zata shig….” kafin ta qarasa yafada kanta, tareda hade bakinsu waje daya

Wata irin soyaiya Mai tsayawa Arai yafara nuna mata, tunawa da tayi da ranar farko yasa taqi sakin jikinta, Amma dataji yanda yake wasanni da’ita batasan lokacin data bada Kai ba, kayanta yacire mata gaba daya, yaja bedsheet yarufe su, bakinsa yad’ora akan boobs dinta ya dinga tsotsarsu tamkar wani jariri sabuwar haihuwa

Yadauki lokaci Mai tsawo yana abu daya kafin yafada cikin kogin ni’imar Waheeda, yayi mamakin yanda yaji wajan kamar ansake rufe shi, lokaci daya yasaki abinda yasaba, wato kuka 😂

Ita kanta Waheeda bataji wani banbanci ba Dana farkon

Hajiya Anty ta shirya tsaf cikin uniform dinta na Asbiti zata tafi wajan aiki, Sai a lokacin ta lura babu Waheeda a Dakin, tasan yanzu Naufal yana bacci, saboda haka may be ta zagaya gidan ne tunda kullum tana zaune adaki

Jakarta ta dauka tafuto daga d’akin, but tana futowa falon taji wani irin kuka na tashi da gurnani, gabanta ne yafadi, cikin sauri ta nufi Dakin Naufal tayi tunanin ko wani abu ne yasame shi, tana zuwa bakin kofar Dakin taji yana kuka yana fadin “wayyo Allah naaaaa….Waheee ….daaaa,dadi”

Cikin sauri tabar wajan, hamdala take cikin ranta da Allah yasa Uncle Usman baya Nan, ita kanta tasan yayi kokari a naci irinna Naufal, batabar gidan ba saida taja musu kofar falon tarufe, sannan tashiga mota ta wuce wajan aikinta

Kwana biyar suka qara a gidan Hajiya anty, wayar Waheeda ta qaraso, irin wadda takeso din kamar yanda ta fada masa, cikin satin sukai sallama da kowa suka wuce Saudia shida ita dakuma Maya

Satin su biyu a Saudia, Babban Yaya yahadawa Maya tsaraba sosai itada iyayenta, tadawo gida, shikuma ya wuce honeymoon shida amaryar sa zuwa Dubai

Satinsu biyu a Dubai Babban Yaya yana shan amarcinsa son ransa, zuwa wannan lokacin harta saba, ita kanta tafara jin dadin abun kadan kadan

Daga Dubai England suka wuce wajan aikinsa, suna zuwa gidan, jikin Waheeda yayi Sanyi, ta tuna lokacin da sukazo da ita, yanda take santin gidan alokacin yace mata idan taso zai iya zama gidanta, ganin yanda take tafiya ahankali jiki a sanyaye yayi tunanin gajiya tayi, Dan haka yasaka hannu ya sureta sukai cikin gidan, nanma suna shiga falo tatuna da Didat, wancen zuwan da tayi dashi ta dinga waya tana bashi haquri dakuma fahimtar dashi akan Babban Yaya yayanta ne,suna zuwa daki suka zube akan gadon, Waheeda tasake tunawa yanda sukai ta birgima akan gadon ita dashi wancen zuwan, alokacin Gani take babu ya Huzaifa, rayuwa kenan Dama hakane, zakayi samari kalakala ma banbanta, Amma bakasan dawa zakayi rayuwar aure ba, Babban Yaya ne ya katse mata tunanin ta, yace “Baby nagaji dayawa, wanka zakimin, dama yau baki minba, baki wanke abarki ba yau”

ya qarasa maganar yana murmushi dimple dinsa na lotsawa

Cikin shagwa6a tace “Naga takaina ni Waheeda Wai Dan Allah Babban Yaya waye yafada ma wannan maganar ne? Nide nasan dagani Sai Maya, dakuma Ummah mukadai mukasan maganar, Kuma nasan sude bazasu fadama ba”

Murmushi yasake yi yace “Ina ruwanki da Wanda ya fadamin, Nima bazan fada ba, tunda alokacin ko gidan Nan zai zama shaida saida na tambaye ki laifin me ki kaiwa Ummah, Amma kikace min ba komai”

Cikin shagwa6a tace “to Naga alokacin Kai Yaya nane, tayaya zan fadama”

“yanzu Kuma fa? Ni menene?”

Shiru tayi taqi bashi amsa, Sai wani kallo datake watsa masa na soyaiya

Tashi yayi yacire kayansa, yashige toilet zaiyi wanka, yana shiga itama tacire kayanta ta daura wani Dan qaramin towel , taje wardrobe tasaka kayan, tana kokarin rufewa idonta ya sauka akan dairy din Babban Yaya, Wanda tafara karantawa kwanaki, dauka tayi, ta zauna abakin gadon tabude tafara karanta wa

Gaba daya shafin farko Dana Gaba, tarihin rayuwar gidansu ne tun kafin ahaifeta, Sai kuma lokacin da aka haifeta da yanda ta sauya komai na rayuwar sa, yanda yake fuskantar matsala idan ya ganta da wasu mazan, da yanda ya baiyana tsananin yanda yake sonta acikin zuciyar sa, tausayi yabata, lokaci daya hawaye ya wanke mata fuska, tana karatu Amma hawaye yana d’isa akan paper, batasan yafuto daga toilet dinba, saijin maganar sa tayi akanta “idan kin gama karatun nafuto”

Tana d’ago kanta data ganshi, tatashi da sauri ta rungume shi tareda fashewa da Kuka, Shima qwalla ce tafuto daga Idonsa, ahankali yace “menene abun kukan to?”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button