BABBAN YAYA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

BABBAN YAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

nanfa hankalin su yasake tashi, falon ya kaure da Kuka, musanman da basu ta6a ganin tashin hankalin dayasa Babban Yaya kuka ba Amma yau sunganshi da idonsu yana kuka, Babban Yaya yayi kan Waheeda yana cewa “Daddy zan kaita wani asbitin, ni qanwata batada komai”

Jin shiru Waheeda bata tashi ba yasa ya kalleta, Sai a lokacin ya lura ta suma 🙆🏻‍♀�

Gabansa ne yafad’i, cikin tashin Hankali yafara jijjiga jikinta “ke…. Ki Tashi…. Please kitashi ninasan bakida komai Waheeda”

Yajuya ya kalli Ummah yace “Ummah kice mata batada komai….”

Magana yake yana kuka da Idonsa, kwata kwata kamar ma baya cikin hayyacinsa

Hajiya Anty ta share Hawayen idonta tatashi tadauko ruwa a fridge ta shafa mata, da Kuka tafarka, muryarta harta fara dashewa

Babban Yaya ya zauna, yadafe Kansa da hannayensa biyu tareda rufe Idonsa, Daddy ya kalli Waheeda yace “ke zonan”

Ahankali tatashi taje gabansa ta tsugunna tana sharar hawaye, Daddy ya kalleta yace “nasan bakya ji Waheeda, kifadamin a gidan ubanwa kika Dauko mana wannan masifar?”

Wani irin kuka ne yataso mata, hawaye masu zafi suka zubo daga cikin idonta, kanta tafara girgizawa tace “wallahi tallahi Daddy bansani ba…. Ni bansan zan dauki cuta ba”

Gaba d’ayansu Sai suka maida Kallan su wajan Waheeda, Daddy yace “ni nasan akwai abinda kika aikata, kifadamin kokuma yanzu yanzun Nan namiki illa a wajannan….” ya qarasa maganar cikin tsawa

Cikin kuka tace “anta6a yimin allura da sirinjin da akayiwa Didat dashi, sannan d’azu muna hanya Huzaifa yace min Wai jinin daya Bani a Asbiti ba’ayi masa text ba, haka aka Sakamin ba tareda an gwada jinin ba”

Wani irin kishi ne yakama Babban Yaya,shi yana can yana hauka akanta ashe ita tana Nan soyaiyar ta takeyi da samarin ta.
Cikin 6acin rai yatashi tsaye yace “What….?, ashe bakida Hankali bakisan mutum ba kawai saboda wata banzar soyaiyar ku Zaki yarda ayi miki amfani da sirinjin da aka masa allura?, sannan anfad’a miki ansaka miki jini batare da text ba so yarufe miki ido kikasa daukan qwaqwaqwaran mataki akai? Kifadamin ke wacce irin mahaukaciya ce? “

Kallan sa tayi tafara girgiza masa Kai tahad’e hannunta biyu waje d’aya 🙏🏻alamun yayi haquri
Babban Yaya bai saurareta ba ya d’aga hannu ya wanke tada mari, zai qara mata wani Marin cikin sauri Uncle Usman yace”Naufal”

Cak yaja ya tsaya yafasa dukanta, Uncle Usman yace “kayi Hakuri”

Sannan yajuya ya kalli Sa’eed da Sa’ad, yace “kuje kuzo mana da Huzaifa dakuma Didat, ga doctor khamis Nan bai tafi ba, saiya dauki jininsu aga waye yasaka mata cutar acikinsu”

❤️❤️❤️
1/28/22, 20:51 – Ummi Tandama😇: GG

Daga Huzaifa har Didat, babu Wanda ya sauya Kaya daga cikin kayan da sukai fad’a d’azu 🤣
Dama kowa kamar jira yake, shiyasa su Sa’eed suna zuwa suka biyo bayansu, suka taho gaba d’aya

Uncle Usman ya kalli doctor khamis yace “dauki jininsu doctor”

Doctor yamatso jikinsa Sai rawa yake yanata had’a gumi, yad’auki jininsu, Hajiya Anty tatashi ta kalli Naufal tace “muje kasa driver yakaishi, saboda yayi sauri ya dawo karmu tsaidasu Huzaifa dayawa”

Didat sarkin kishi ya kalli hajiya Anty yayi qasa da Kansa, wato kar Asa su huzaifa jira, shi bata ambaci sunan saba, Huzaifa kawai tasani 😂

Babban Yaya yatashi, suka futo su uku, dashi da doctor dakuma Hajiya Anty,suna zuwa compound Babban Yaya yakira driver, yasa shi yad’auki doctor khamis suka tafi.

Ummi ce tashigo gidan, Babban Yaya yana ganin ta yad’auke Kansa kamar bai ganta ba, yarasa uban me yakawo ta gidan Kuma, kwata kwata mace babu aji babu kara kullum kina yawo a gidan surukanki?

Ummi ta kalli hajiya Anty ko gaishe ta batayi ba, ta shareta,Anty tayi murmushi kawai, Babban yayama ya ganta, Kuma Sarai yagani bata gaida Hajiya Anty ba, Shima bata gaishe Shiba, har Gara shi Dama yasan kar take ganinsa 😃
Amma hajiya Anty fa?🤔

Gaba d’ayansu falon suka dawo suka zauna, dasuka shigo falon ma yayi tunanin zata gaida Hajiya Anty nanma yaji shiru, Kuma yaga ta nemi kujera ta zauna ta kame, saikace yar gida, jijjiga Kansa kawai yayi, inbanda rashin Hankali tayaya zakiga family sun taru gaba d’ayansu, Amma kizo ki zauna ai daga Gani kinsan ba lafiya ba

Yanda kowa na falon yayi shiru haka ummi ma tayi shiru tana jira taga abinda yake faruwa,su doctor basufi awa d’aya ba suka dawo, yana shigowa kuwa kowa ya maida hankalin sa Kansa, Uncle Usman yace “doctor ya akayi?”

Cikin rashin damuwa yace “Alhaji naduba babu…., kowa lafiyarsa kalau acikinsu, daga Didat d’in har Huzaifa, babu Wanda yake d’aukeda HIV”

Ummi ta zaro ido😳 tareda rufe bakinta da hannunta tana sake zare ido tana Kallan ‘Yan falon taga to waye yake da qanjamau d’in? 🤔

Daga Daddy har Uncle Usman sunkuyar da kansu qasa sukai, to daga Ina wannan matsalar take? Tayaya akai Waheeda tasamu wannan cutar kenan?

Huzaifa ya miqe tsaye, ya kalli kowa da kowa na falon yace “Alhamdulillah… Tunda gaskiya ta bayyana, ni Dama temako naso yi, lokacin Dana tarar batada lafiya nad’auki jinina nabata,ashe bansaniba tunanin da kuke min daban ne, saboda tozarci mu za’a kawo a ajiye anan Ana jira aga waye me qanjamau acikinmu ayi masa ruwan bala’i saboda shine yasakawa ‘yarku cuta, to ai yanzu kunji komai, Kuma gaskiya ta futo bamune muka saka mata ba, saboda haka nikam na haqura da Waheeda…. Maganar gaskiya, bazan iya auren me qanjamau ba, duk soyaiyar danake mata….”

Tunda yafara magana gaba d’aya falon yayi tsit, kowa kallansa yake cikeda mamaki, musanman su Daddy yanda suka d’aukake shi,Babban Yaya kuwa baiji komai ba, asali ma dad’i yaji yanda gaskiya ta bayyana,sukaga halin Huzaifa na zahiri, inda ace ya fad’a musu karsu bashi Waheeda ya tabbatar babu Wanda zai saurareshi, ko d’ago Kansa baiyi ya kalli Huzaifa ba,harya gama maganar sa yafice daga falon cikin 6acin rai

Waheeda kuwa d’agowa tayi da jajayen idonta ta zubawa Huzaifa ido, ko kad’an takasa ce masa komai, yanbiyu kuwa kuka suke sosai saboda furucin huzaifa, bakajin komai Sai kukansu daya cika falon

Ummi ta Jinjina kanta tareda ta6e baki☹️

Didat yatashi tsaye ya qarasa wajan Waheeda tareda miqa mata hannu yace “Waheeda, kiyi hakuri kinji, Ina tare dake a koda yaushe, wannan shine abinda nake nuna miki, nine nake sonki ba Huzaifa ba…..”

“kakeson wa?” maganar kaka ta karad’e falon nasu, juyawa yayi yaga kakarsa da babansa a tsaye, Kai tsaye yace mata “inason ta, saboda me zan rabu da’ita dan qaddara tahau kanta?”

“to saide ka za6a koni ko ita, haka kawai yarinyar data qika tun tuni,kana bibiyarta akan ta saurareka taqi, tazabi wani a kanka, itace yanzu saboda rashin Hankali zakazo kace kanaso ka aura Bayan tagama yawon duniya takwaso qanjamau? To bada niba bada irin gidana ba, wuce mutafi kona tsinema Albarka yanzun Nan”

Hawaye Didat yafara yace “Amma Ina sonta…”

Babansa yayi ajiyar zuciya yace “kayi hakuri son, Amma nima bazan barka kana da cikakkiyar lafiya ka sauri me HIV ba”

Didat ya kalli Waheeda, itama ta Kalle shi,bayajin zai iya daina son Waheeda har qarshan rayuwarsa, tanada cuta ko bata da cuta abinda yasani shine yana qaunarka tsakani da Allah, cikin kuka yafice daga falon da sauri, iyayensa suka Mara masa baya
Hawaye kawai tsiya ya yake a’idon Waheeda,wannan shi ake kira sai masifa ta sameka ne zaka san me sonka da gaskiya, yanzu duk soyaiyar da Huzaifa yake iqrari yana mata ashe qarya ne? Ashe saboda cuta ta sameta zai iya gudunta? Didat din datake wulaqantawa shine ya tsaya tsayin daka akan yana sonta duk da haka, lokaci d’aya taji numfashin ta yana sama kamar zai d’auke, yanbiyu da Ummah da Hajiya Anty, kuka suke sosai, duk falon anrasa Wanda zaiyi magana guda d’aya

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button