BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

        ★★★★

  Duk da bata ɗauki gargaɗinsa da muhimmanci ba sai ta kasa sakewa da Yaseer gaba ɗaya yau. Kullum shike fita da ita su ciyo abinci a inda yasan za’a samu abinda take iya ci. Amma yau saita ɓoyema ganinsa. Daga salla ta maƙale a massallaci taƙi fita. Sai ma ta ɗauka alkur’ani tahau karantawa.
       Sai da ta daidaici lokaci yaja sosai sannan ta fito. Kamar jira tana fitowar wani abokin aikinta yazo ya sanar mata tana da baƙo. Da mamaki take kallonsa dan bata tunanin wani zai iya zuwa wajenta a yanzu. Daga Muzzaffar har Dr Jamal bata tunanin ganin wani anan, garama Muzzaffar yakan zo idan ya daidaici sun tashi yace zai ɗauketa sai dai bata taɓa yarda ba. Kamar bazata je ba sai kuma taga gara taje dai taga wanene.
        Turus tayi lokacin data iso taga mai kiran nata, zaune yake a cikin mota sai dai ƙafarsa ɗaya na waje dan ƙofar a buɗe yake……….✍????

ZAFAFA BIYAR

INAYAH
MamuhGee

GURBIN IDO
Safiya Huguma

SANADIN LABARINA
Hafsat Rano

FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)

BABU SO
Billyn Abdul

Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
0913484810_ZAFAFA BIYAR_

INAYAH
MamuhGee

GURBIN IDO
Safiya Huguma

SANADIN LABARINA
Hafsat Rano

FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)

BABU SO
Billyn Abdul

Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107 ko

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: Typing????

  *_❤‍????BABU SO....!!❤‍????_*
             _(Miya kawo kishi?)_



          *_Bilyn Abdull ce????????_*

BABU SO????????AREWABOOKS

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

19

………. Ɗagowa yay daga latsa wayar da yake yana kallonta, dan ƙamshin turarenta da takunta ya sanar masa da zuwanta duk da ta kasa magana. Idanunta ta ɗauke daga kallonsa tana faɗin “Good Afternoon”.
           “Ni kike ma gaisuwa kina juyar da fuska?!”.
    Juyowa tai Idanu cike da ƙwalla tana kallonsa. “Ni wlhy Yaya ban san mina maka ba duk kabi ka tsaneni ka takura ni. Komai nayi a duniyar nan a wajenka ban iyaba”. Ta ƙare maganar da sakin siraran hawaye.
         Kallonta kawai yakeyi ko ƙyaftawa babu. Ji tai kallon ya sake saka mata jin haushinsa, juyawa tai da nufin barin wajen…..
     “Kika bar wajen nan sai ranki ya ɓaci”. 
    Idanunta ta rumtse tana jin wasu zafafan hawaye da sukafi na farƙo na neman kufce mata. Ita kam ta rasa mita tsarema bawan ALLAHn nan a duniya, tana fatan watanin nan bakwai da suka rage mata su maza suzo ta kammala abinda ya kawota tabar ƙasar nan, dama tun farko abinda ta gujemawa kenan amma su Mamie suka kasa fahimtarta. Haɗiye hawayen tai batare data barsu sun zubo ba sannan ta juyo garesa, yana a yanda yake har yanzu, sai dai idanunsa masu kwarjini da kaifin dake hana ƙarfin halinta tasiri na nan tsaye kanta ƙyam har yanzu. Kasa jurar kallonsa tai, tai ƙasa da nata, shima sai ya janye nasan, juyawa yay kujerar gefensa ya ɗakko ledar dake ajiye. Miƙa mata yay kansa tsaye.
     Ledar ta fara kalla tare da hanunsa dake ɗaure da agogo da zoben azurfarsa da ya jima yana birgeta, har addu’ar damar sace zoben ta taɓa yi a zuwa na karshe da tai kafin wannan…. Saurin ɗagowa tai tana kallonsa jin ya kamo hanunta cikin nasa, ya wani sake ƙanƙance idanu cike da salon kallon da a duk sanda ya jefeta da shi yake firgitata, ta fara son zame hanun a hankali dan gaba ɗaya lakar jikinta neman daina aiki takeyi, kanta ta fara juya masa tamkar mai ciwon wuya, tana son zare idanunta daga cikin nasa amma yaƙi bata damar hakan nan ma, sai kawai ta sakar masa kukan karya.
    Hanun nata ya saki a hankali bayan ya saka mata ledar, kamar wadda ake control da remote fitt ta ɓace a wajen. Tsabar sauri har tintiɓe tayi ALLAH dai ya taimaketa bata faɗi ba ta dafe gate.
           Murmushi ya saki mai ɗan sauti daga ƙirjinsa yana kauda kansa. Ya maida ƙafafunsa cikin motar tare da rufeta yabar wajen.

    Itama koda ta shiga sai da ta samu jikin wata mota ta huta tare da share hawayen ƙaryarta sannan ta buɗe ledar. Shawarma ce da ice-creem sai yogurt da robar ruwa. Haka kawai sai kuma ta samu kanta da sakin murmushi. A fili tace, “Ga rashin mutunci ga kirki idan yaso”. Dariya ta sake ƙyalƙyalewa da shi dan haka kawai drama ɗin tasu ta yanzu take maimaita kanta a zuciyarta tana saka mata nishaɗi. 
   Yau kam tayi aniyar kozai daketa bazata yarda tabi motarsa ba, dan haka kawai ragwantakar data nuna ɗazun a gabansa ke hanata sukuni, sai dai murmushi ya kasa barin fuskarta har Yaseer sai da ya kasa haƙuri ya tambaya. Ƴar dariya kawai ta masa batace komai ba. Ana tashi itace farkon fitowa, bata son bin Yaseer ɗin badan tana jin tsoron tabbatar hukuncin Yaya Shareff ba, ba kuma ta buƙatar shiga tasa motar shima gara ta hau napep. Sai dai kuma cikin rashin sa'a tana fitowa taci karo da motar tasa a wajen gate, kuka kawai ya rage ta fasa ta huta, tai tsaye ta kasa matsawa ga motar har tsahon wasu sakani. Sauke glass ɗin da dariyar Khaleel ta sata sakin ajiyar zuciya, dan tunda ta fito idonsa a kanta. “Ai ba mai motar bane sai ki taho mu tafi farar kura kawai”.
 “Humm ALLAH Yaya bazaka ganeba. Shi Yaya Shareff ɗinne ya cika takura da hana mutane sukuni suji daɗin rayuwa”.
      “Maybe yana tsare mutuncin kayansa ne kar kiga laifinsa”.

Bata wani gane mi Khaleel ɗin ke nufi ba, saboda da hausa yay maganar ta buɗe ta shiga tana dariya kawai. Shima yasan bata gane ɗin ba dan haka ya dara.


    Tun daga waccan ranar Anam ta sake kafa wasan ɓuya da Yaya Shareff, motar Khaleel ta samu matsala, sai kawai ta koma bin school bus na yaran gidan. Kasancewar suna fitar sassafe kafin Shareff daya tsiri zuwa gidan da safe ya iso har sun wuce. Ana tashi kuma zatai wuff ta fito ta tari napep. Motar Yaseer ma dai ta daina shiga duk da yata bibiyarta da son jin ba'asi tana tabbatar masa babu komai.
 Samarinta biyu da sukafi takurama rayuwarta taga sun rage manne mata. Dr Jamal da Muzzaffar. Kowannesu kuma yanada gurbi na musamman data ajiyesa dan koba komai suna sakata nishaɗi a wasu ɓangatorin na rayuwa. Sai dai ta gagara neman jin dalilin kowannensu akan ɗan janye mata da yayi, garama Muzzaffar sukan ɗanyi waya jefi-jefi ko chart wasu ranakun.
   A gidan nasu kuwa bata da wata damuwa sai su Hussaina wataran, dan idan rashin kunyarsu ya tashi sukan mata sai dai bakinsu nashan bugu dan bata ɗaga musu ƙafa. Ta daina zuwa gaida Mommy da Gwaggo sai in ta ritsa sun haɗu a hanya taita sinne kai wajen gaishesu. Ko kallonta basayi, dan a ganinsu ma ƙin zuwa gaishesun ta taimakesu koba komai sukan manta da wanzuwarta a gidan. Hakan baya damunta, takan wataya tsakanin sashen aunty amarya da Mom abinta. Ita da Aysha da sauran yaran gidan kuwa sai sambarka. Hakama Daddy da Abbah a koda yaushe cikin bama rayuwarta kulawa suke fiyema da yaransu, dan kullum da tsarabar da waninsu zai kawo mata gidan da kuma mata nasihar tsare mutuncinta suke.
    Kusan kwanaki goma kenan basu haɗu da Shareff ba, sai a yau da akai sa ranar auran Maheer da sam bata san da zancen auren ba sai da taga akwatina a sashen Mom akace na auren Maheer ne yau za'a saka rana da kai akwatinan. Tayi mamaki sai dai batace komai ba, sai daga baya Aysha ke bata labarin ai Maheer ɗin baya son auren Mommy ce ta takura kamar yanda ta takurama Shareff shima. Auren zumincine da ɗiyar ƙanwarta. Sosai Anam taita mamakin hali irin na Mommy, a ganinta ta cika takurama ƴaƴanta a gidan, musamman Yaya Shareff da Yaya Maheer ɗin. Gashi suna mata matuƙar biyayya fiye da duk sauran yaranta, dan tasha ganin Mommy nama Aysha da su Hussaina faɗa suna ƙunƙuni. Itace ma kema Aysha faɗa da nuna mata illar hakan ga iyaye. Sai kuma gashi masu mata biyayyar sunfi shan wahala a hanunta fiye da su Ayshan da sai abinda suke so sukeyi.
   Batabi takan duk hayaniyar da ake a gidan ba, kasancewar ma a sashen Mom baƙin da zasuje kai kayan suke isowa, saita fito domin wucewarta sashen aunty amarya ta huta dan asabar ne. Kamar ta juya taji, lokacin dataga motarsa na ƙoƙarin yin fakin gab da sashen Mom ɗin, amma sai ta dake ta fuske zata wuce abinta.
   Siririn tsakin da taji anyi dai-dai zata gitta ya tilasta ta juyowa, dan sam baiyi kama da tsakin Yaya Shareff ba. Fadwa ce a tsaye cikin shigar madam getzner shadda da taci uban aiki sai walwali take, tabbas tayi ƙyau sosai. Anam ta sakar mata wani murmushin ƙularwa da kashe mata ido ɗaya ta cigaba da tafiyarta. Kusan ɗan cin karo sukai da Shareff daya zagayo waya manne a kunensa yana magana. Shima dai sanye yake cikin shaddar fara tas datai masa ƙyau da fiddosa a asalin bahaushensa ɗan arewa dan harda hula. Ta ɗan ja baya yayinda shi kuma ya tsaya cak dan gaba ɗaya hankalinsa akan waya yake baima san wainar da suke toyawa da Fadwa ba. Kallonsa tai tana wani ƙyaƙyƙyafta idanu, sai kuma ta tunzura baki gaba ganin kallon nata da yakeyi shima tamkar idanunsa zasu cinyeta. “Good morning”. Ta faɗa tana gittasa da ƴar sassarfa.
  Cikin basarwa ya cigaba da wayarsa, hakan sai yayma Fadwa data tsaresu da idanu daɗi harda matsowa zata rungumesa ya kauce mata yana nuna mata sashen Mom. Cikin shagwaɓa tace, “Ni dai ka gama mu shiga tare ALLAH kunya nake ji”. 
Sarai yasan ƙarya takeyi, amma sai baice mata komai ba har ya kammala. Gaba yay ta bisa a baya....

   Bata buƙatar zaman tunanin abinda ya shafi waninsu, dan haka tai connecting bluetooth ɗinta ta manna a kunne. A hankali takai kwance bisa grass carpet dake a ɗan ƙaramin garden ɗin dake bayan ɗakin aunty amarya tana lumshe idanunta cike da nishaɗi, dan waƙar da take saurare tana matuƙar sonta, mawaƙin ɗan ƙasar malaysia ne, waƙar ma anyitane da yaren malay sai dai an cakuɗa da turanci. Tayi nisa sosai wajen sauraren waƙar fuskarta shimfiɗe da murmushi, ga idanunta a lumshe sanyin inuwar wajen na ƙara girmama nishaɗinta, bakinta sai motsawa yake a hankali alamar bin waƙar takeyi....
   Jin ƙamshinsa ya ƙara ƙarfi cikin hancinta ya sata kasa cigaba da jurewa ta buɗe ido a hankali batare da tabbacin mai ƙamshin bane a wajen. Sai dai kuma cin karo da shi ɗin tsaye ya sakata ɗauke numfashi na wucin gadi. Da sauri ta tashi zaune duk tana jinta a daburce, hijjab ɗinta dake gefe ajiye ta ɗauka ta rufama jikinta dake sanye da wando three quarter da top ƙarama, zafine ya isheta ta sakasu kasancewar a ɗaki take, sai da taji hayaniyar mutane zasu dameta ta sako hijjab kawai ta fito, ganin babu kowa anan ya sata cirewa ta ajiye dan ta samu iska mai ƙyau ta shigeta. 
    Rigarsa ya ɗan tattare sama ya zauna shima bisa grass carpet ɗin dake a share tas dan aunty amarya kullum cikin kulawa take da wajen saboda tsananin son garden da takeyi. Mace ce ƴar gaye mai son hutu da gudun yawan hayaniya. Duk da Anam taji wani irin da zaman nasa wajen amma sai ta dake abinta. Sai dai ta kasa cigaba da bin waƙar daketa maimaita kanta. Shima da tun zuwansa wajen baice komai ba kallonta kawai yayi na wasu ƴan sakanni, sai kuma ya kai hanunsa kunnenta ya zare bluetooth ɗin ya saka a nasa kunnen. Juyowa tai tana kallonsa da mamaki, ya lumshe idanu ya buɗe tare da kauda su a kanta yana sauraren waƙar.........✍

ZAFAFA BIYAR

INAYAH
MamuhGee

GURBIN IDO
Safiya Huguma

SANADIN LABARINA
Hafsat Rano

FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)

BABU SO
Billyn Abdul

Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
0913484810_ZAFAFA BIYAR_

INAYAH
MamuhGee

GURBIN IDO
Safiya Huguma

SANADIN LABARINA
Hafsat Rano

FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)

BABU SO
Billyn Abdul

Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107 ko
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: Typing????

  *_❤‍????BABU SO....!!❤‍????_*
             _(Miya kawo kishi?)_



          *_Bilyn Abdull ce????????_*

BABU SO????????AREWABOOKS

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

20

………“Waye mawaƙin nan?”.
Cikin shakku da mamakin ta kallesa. Ganin zai kallota tai saurin janye idanunta a kansa, ta bashi amsa cike da basarwa.
       Ɗan Murmushi yayi dan ya riga ya ganta. “Ya iya waƙa gsky, kuma cikin nutsuwa da ma’ana”.
     Itama Murmushi tai a karon farko tana dubansa. “Shiyyasa nake son waƙoƙinsa sosai nima ai. Bashi da hayaniya, sannan duk abinda zai faɗa yakan dace da furicin zuciyoyi”.
         Tsareta ya ɗanyi da idanunsa, hakan yasa ta kauda nata. “Wane furucine ke dacewa da ma’anar zuciyoyi?”.
     A yanda yay tambayar tamkar mai raɗa ya sata juyowa ta sake kallonsa, sai kuma ta janyesu har yanzu murmushinta bai ɓace ba. “Yaya bai zama lallai tunanina dana kowa yazam iri ɗaya ba ai, zata iya yuwuwa nice kaɗai ke fassara haka ko fahimta a lokacin da nakejin waƙoƙin nasa”.
      “Uhhm nice. Kinga nima sai ki turamin maybe na fahimci irin taki fahimtar ko! Ki samun duka waƙoƙin sa ta WhatsApp”.
           “To ai bani da number ka”.
     Cikin ido yake kallonta, ta risinar da nata dan bazata iya jurewa ba. Shima sai ya ɗauke nasa ya maida ga tsuntsaye biyu dake shan ruwa a ɗan kaskon da aunty amarya kan zuba dan su. “Baki so hakan bane shiyyasa baki da ita”.
     Murmushi kawai tayi, amma batace komai ba, ta dai cigaba da kallon tsuntsayen kamar yanda shima har yanzu idonsa na kansu. Shiru kusan mintuna uku, tashin tsuntsayen ya sashi katse shirun nasu da faɗin, “Zanyi tafiya zuwa China, kuma zan jima dan zan samu a ƙalla kwanaki ɗari acan ko ƙasa da hakan insha ALLAH”.
       Mamakinsa ya sata ɗagowa ta dubesa, kasancewar nasa idon na kanta ya sashi ɗan lumshewa alamar tabbatarwa… Bata da zaɓin daya wuce kaɗa masa nata kan itama. “ALLAH ya tsare hanya, ya kuma bada abinda za’aje nema mai albarka. Ya tsareka daga haramun, ya haɗaka da halal”.
     Ajiyar zuciya yaja mai ƙarfi, har takai ta sake ɗagowa ta kallesa, murmushi ya sakar mata, irin wanda zata iya rantsewa bata taɓa cin karo da shi a gareta ba. Ta ɗanyi tsammm tana kallonsa, gaba ɗaya ganin al’amarin nasa take na yau kamar almara. Lakace mata hanci da yay ya sata saurin ɗauke kai cike da kunyar kanta. Ya ɗan murmusa yana gyara zamansa. “Zaki koma gidana k da Aysha ku zauna har na dawo”.
       “What! Yaya ni ɗin?”.
   A yanda tai maganar ya sashi kafeta da idanunsa sosai. “Bazakije ba kenan?”.
     Fuska ta ɓata da tura baki gaba, “To ai ni dai kasan bama shiri da matarka”. 
     “Idan kikaje zama yanzu ai sai ku fara shirin kafin na har abada”.
Ba wani fahimtarsa tai sosai ba saboda da hausa yay maganar, amma sai ta girgiza kanta. “No bazamu taɓa shiri da matar can taka ba. Dan nama kusa fara kai mata naushi idan tana cigaba da min kallon banza. Karta ɗauka tsahonta da girman jiki zai razana ni”.
      Yanda take maganar cike da masifa da tsiwa ya bashi dariya sosai. Ya kauda kai gefe yana murmushi. Kafin ya sake juyowa fuska a haɗe yana kallonta. “Matar tawa zaki nausa?”.
    Batace komai ba, sai dai ta sake tura baki gaba. Zaiyi magana ring ɗin wayarsa ya dakatar da shi, Mommy ce, dan haka yakai kunne cike da ladab yay sallama.
     “Kana ina ne wai Shareff? Ga matarka sai amai take anan duk ta galabaita kazo kuje asibiti”.
          “Ya ALLAH!”.
    Ya faɗa a hankali yana lumshe ido. “Okay Mommy ina zuwa. Amma bara na kira Jamal kin san yau weekend ne ba lallai mu samu yanda muke so a asibitin ba”.
    “To ya hanzarta dan ALLAH”.
“Okay bara na kirasa ɗin”.
     Koda ya yanke wayar kasa haƙuri Anam tayi, dan bata san wa akace baida lafiyar ba. “Yaya waye za’a kai asibiti?”.
            Yana ƙoƙarin kiran Dr Jamal ya bata amsa kai tsaye. “Fadwa ce keta amai wai, duk ta galabaita”.
    Sosai ta nuna jimaminta kasancewarta mutum mai tausayi. “Ayya ALLAH ya bata lafiya, dama bata da lafiya kuma ka yarda ta fito Yaya?, ai da ka barta a gida tunda kowa yasan ciwo”.
         Numfashi ya ɗan furzar, rashin ɗaukar wayar Dr Jamal ɗin ta bashi damar bata amsa. “Bawai kwance take ba, yanzu ma inaga taji ƙamshin abinda bata so ne shine aman yazo”.
      Kallonsa tai cikin mamakin amsar tasa, sai dai kafin tace wani abu kiran Mommy ya katseta. Ɗagawa yay yana mikewa. “Mommy na kira bai ɗaga ba maybe baya kus… Yauwa gashi ma yana kira ina zuwa”. Yankewa Mommy tai, shi kuma ya samu damar ɗaga kiran Dr Jamal ɗin. Ya ɗan matsa da ga wajen Anam ɗin suna magana. Da kallo ta bisa, sai kuma ta ɗan ɗage kafaɗa da ɗauke kanta cikin ɗan taɓe baki. Hijjab ɗin da taketa faman ƙudundune jikinta ta warware ta sanya da ƙyau itama ta miƙe da nufin komawa sashen aunty Amarya tai kwanciyarta kawai ko ɗan chart tayi da ƙawayenta na Malaysia.
      Ya gama magana da Dr Jamal ya juyo kawai ya hangota har takai ƙofar baya ta kitchen ɗin aunty amarya. Idanu ya tsira mata harta ɓacema ganinsa. Ya ɗan ja numfashi tare da barin wajen shima.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button