BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

      Lahadi da yamma mijinta ya dawo hanunta, ya gama kwanakinsa a wajen Fadwa. Da taimakon Aysha suka haɗa abincin dare na gaba daya kamar yanda ya sharɗanta. Ta nufi sashensa domin gyarawa Aysha kuma ta gyara mata nata duk da ma babu wani datti mai yawa kasancewar babu yara ba kuma wasu jama’a ne da yawa ke shiga da fita ba. Duk kaiwa da kawowar da Anaam keyi a sashen Shareff a idon Fadwa ne dake leƙe ta window ɗin falonta. Kai tsaye tasan wannan rawar jikin na Anaam wai za’a tarba miji ba basirarta bace Aysha ce. Tai ƙwafa da cije lips, a ranta tana ayyana yarinya ni dake mu zuba a nan gidan. Oho bama tasan tanaiba, dan koda ta kammala rufo sashen tai harda saka key saboda ya bama kowacce key. Batare data ko lura da Fadwa ba ta nufi sashenta dan ta samu tai wanka tunda tasan a koda yaushe zai iya dawowa gidan tunda ba aiki ya fitaba. Yaje can gidane Mommy ta kirashi duk da a cikinsu babu wadda tasan da hakan. Yadai ce musu zai fita kawai. 

        ★Ransa fes ya iso gidan domin jiya ma yazo ya gaishesu kuma shida Mommy babu wata damuwa. dan koda ya bata haƙuri akan duk abinda ya faru tace masa komai ya wuce a gareta kawai. Yaso yaji kamar ba haka bane a ransa, amma saita kore masa dukkan tantama ta hanyar sakin jiki da shi sukai hira da suka jima basuyi irinta ba. Kuma abin mamaki ko sau ɗaya bata kawo maganar Anaam ba ko abinda ya shafi aurenta. Hakama Fadwa. Sun tattaunane kawai akan auren Aysha da kuma komawar Maheer wajen aiki a yau.
     Sai da ya shiga dukkan sashen mutanen gidan ya gaida kowa sannan ya nufi sashen Mommy a ƙarshe. Tana falonta zaune Hussaina na haɗa mata ƙwaɗon zogale ya shigo. Fuskarta da murmushi ta amsa masa sallamarsa. Ya kai zaune shima fuskar tasa da murmushi.
      “First love daɗi zakici haka?”.
Murmushi tayi mai nuna haƙora. “Ai gaka kaima kazo sai muci tare ko?”.
    “Harma na fiki lauma”.
Dariya tayi daga ita har Hussaina dake yin tata a ƙumshe. Ya gaida Mommyn, Hussaina ma ta gaishesa sannan tabar falon bayan ta kawo masa ruwa. A kwano ɗaya sukaci zogalan da Mommy cike da nishaɗi. Suna tsaka da cinne Gwaggo ta shigo.
          “Ja’iri kazo zaka cinye mata ɗan zogalan bayan acan na baka kaƙi ci”.
  Murmushi yay da taɓe baki, “Naki kin saka ƙuli ne itako gyaɗa ta saka shiyyasa”.
    “Oh, da gyaɗar da ƙulin duk ba abu ɗaya bane?”.
    “A wajena ni dai da banbanci”.
Mommy dai dariya take musu kawai.

       Sai da suka kammala Gwaggo da Mommy suka dubi Shareff ɗin cikin komawa serious da ƙyau. Hakan daya ganine ya sashi nutsuwar shima ya maida hankalinsa garesu.
    Gwaggo ce ta fara magana. “Mustapha abubuwa da yawa sun faru waɗanda basai mun zauna lissafi akansu ba ko sake maimaita batunsu anan gurin. Sai dai waɗanda suke faruwa a yanzu sune abun dubawa. Kayi haƙuri munyi kuskuren tilasta maka auren Fadwa ba’a san ranka ba, sai dai mu munyune domin ƙarfafa zumincin ALLAH. Amma ashe zuciyar uwarta cike take da tsatsa. Tunda har a matsayinka na ɗan ɗan uwanta zata iya neman asiri taba ƴarta ta zuba amaka a abinci ko abinsha ya tabbata zata iya kasheka wataran domin farin cikin ƴar tata. Mudai bazamuce dole sai ka saki Fadwa ba. Amma ka zauna kayi tunani mizai iya zuwa ya dawo nan gaba. Dan hatta cikin datai ɓari kwanaki mun fara zargin yarinyar nan zubar da shi tai tana akan sani”.
A matuƙar razane Mommy da Shareff suka dubi Gwaggo. Har Mommy ta kasa haƙuri….
“Gwaggo miyasa zakice haka a ina kikaji wannan maganar kuma?”.
Baki Gwaggon ta taɓe, “Yo Nafi abin duniya na ɓuya ne, kawai nayi shiru ne ban faɗa mikiba. Amma a jiyyarta da nai asibiti na karanci abubuwa da yawa game da yarinyar wlhy. Sai dai ban tabbatar ita ɗin ta zubarba. Amma Mustapha kaje kayi bincike harka tabbatar da gaskiya. Sai dai kayi komai a sirrance basai ka faɗa mataba a yanzu dan karta toshe duk wat hanyar gaskiyarka. Abu na gaba akan aurenka na biyu ne, mudai ba son auren nan muke ba sam, amma munga kai kamar kana so. Dan haka mun yanke shawarar barinka da matarka ku zauna. Sai dai da sharaɗin zaka ƙara aure. Kuma munma zaɓa maka wadda zaka aura yarinyar kirki da tasan mutuncin kanta, idan ƙyau ne kuma duka matan naka ta fisu. Mun tabbatar zakaji daɗin zama da ita insha ALLAHU duk wani ƙuncinka zata ƙwaranye akan waɗan nan ƴan iskan yaran”.
Sosai ya tsurama Gwaggo ido ko ƙyaftawa bayayi, babu abinda zuciyarsa keyi sai luguden daka. Ya haɗiye yawu da ƙyar. Harshensa na rawa yace, “Aure kuma gwaggo?”.
Mommy ta amshe da “Eh aure Babana. Shine zai baka kwanciyar hankali muma kuma ya bamu, dan nidai kasan matarka ta biyu ba zan taɓa sonta ba, amma na haƙura in har kabi umarni na a yanzuma zan barka da ita. Idan kuma ka bijire su duka biyun zaka sakesu ka ƙara auren kuma koda bada zaɓina ba. Dan wlhy itama Fadwa ta fitamin arai. Ko kaunar jin sunan yarinyar nan banayi yanzu. Kuma ina nan saina tabbatar da nunama uwarta kai ɗin jinane ni na haifi abuna kuma. Dan haka kaje kayi shawara daga kwana daya har sati guda muna jiranka. Duk abinda ka yanke sai mu sani.”
“Amma First love……”
“Bana son jin komai Shareff. Kaje kawai kayi tunani kafin ka yanke hukunci, yarinyar da muke so ka aura itace Bibah ɗiyar Luba na san dai ka santa”…………✍

ZAFAFA BIYAR

INAYAH
MamuhGee

GURBIN IDO
Safiya Huguma

SANADIN LABARINA
Hafsat Rano

FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)

BABU SO
Billyn Abdul

Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: Typing????

  *_❤‍????BABU SO....!!❤‍????_*
             _(Miya kawo kishi?)_



          *_Bilyn Abdull ce????????_*

BABU SO????????AREWABOOKS

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

73

………Innalillahi…. Kawai yake jerawa a cikin zuciyarsa har ƙarshe. Ya kafe Mommy da Gwaggo da idanu ko ƙyaftawa bayayi.
“Katashi kaje kar magriba tayi, gashi kace gobe zaka koma aiki kana da buƙatar yin wasu kimtse-kimtse. Dan bana ma son Daddynku ya dawo ya ganka a gidan nan”.
Kansa kawai ya iya jinjinawa, ya miƙe jiki a saɓule ya fice idonsa har wani yaji-yaji yakeyi. Da farko maganar Fadwa ta zubar da ciki ce ta dakesa. Sai dai maganganunsu na gaba sun goge na farko dan a ganinsa Gwaggo ta kawo zancen Fadwa ce ta zubda ciki domin baƙantata su sami damar shigo da zancen auren Bibah, amma kuma zuciyarsa taƙi daina masa wasiwasi. Bashi da wani ra’ayin zama da mata ko biyu tun ful’azal. Sai dai ƙadararsa ta zama haka. A yanzu kuma bayajin duk wuya duk rintsi zai iya rabuwa da Fadwa da Anaam. Dan kowacce da irin kalar soyayyar da yake mata a cikin zuciyarsa. Yama rasa ina zai kama ya riƙe ne a zancen nasu……
Koda ya shigo gidan tsabar yanda zantukan su Mommy suka rikita masa lissafi baibi takan kowa ba tsakanin Anaam ɗin mai karbar girki, da Fadwa mai fita. Kai tsaye sashensa ya nufa. Sai bayan sallar magriba mmn abu ke sanarma Fadwa kamar fa taga motar Shareff. Da mamaki tace “Yaushe ya dawo gidan ban sani ba?”.
“Inaga lokacin kina ciki ne kina wayar nan”.
Ɗan jimm Fadwa tai na wasu mintuna, sai kuma ta shiga bedroom ta dan karo turare ta fito. Kai tsaye sashen nasa ta nufa. Cikin taɓe baki take bin ko Ina na falon da kallo tana mai shaƙar daɗaɗan fresheners da Anaam ta baza ko’ina tare da turaren wuta. Bedroom ɗinsa ta nufa dan baya a falon. Fitowarsa a wanka kenan, ya juyo yana kallonta. Taku take cikin gayu da yanga, sosai kwalliyar tata ta fita da ƙyau dan ko makaho ya shafa yasan ita ɗin gwanace wajen zaman zanawa. Ji yay kaso ashirin bisa ɗarin damuwarsa sun ragu. Ya sauke numfashi a hankali tare da buɗe mata hannayensa alamar tazo gareshi. Da sasaarfa ta karasa ta shige. Suka sauke ajiyar zuciya a tare. Sumbatar gefen wuyanta yayi, muryarsa a sanyaye ya raɗa mata “Kinyi ƙyau Babie na”.
Ajiyar zuciya ta saki da murmushi, ta ɗago tana mai kallonsa, sai kuma ta manna masa kiss a ƙirjinsa. “Nagode Soulmate barka da dawowa”.
Kansa ya jinjina mata, ya kai hannu ya ɗan shafi fuskarta. Murmushi ta sakar masa da janye jikinta a nasa. Baice komai ba ya karasa gaban mirror domin shafa mai. Itama sai takai zaune a bakin gado tana faɗin, “Kayi wani iri kamar mai damuwa. Ko wani abu ya faru ne?”.
Ta cikin Mirrorn ya kallota. Ya ɗan fesar da numfashi a hankali. “Babu komai na gajine kawai”.
“Ayya kona maka tausa?”.
“A’a karki damu nagode wannan aikin ƙanwarki ne ai ko”.
Har cikin rai taji zuciyarta ta sosu, amma saita danne tai ɗan murmushi da mikewa. “Uhhm hakane na shafa’a ne kawai. Kasan idan ina a tare da kai mantawa nake da komai da kowa kai kaɗai ɗin kawai nake iya gani”.
Murmushi yayi mai sanyi yana mai kallonta ta cikin mirror ɗin. “Ngd ƙwarai da gaske Sweety na. ALLAH ya barmu tare har abada”.
“Cikin matuƙar jin daɗi tace amin”.
Itace ta taimaka masa ya shirya, ta rungumesa bayan ta feshesa da turare. Lips dinsu ya haɗe waje guda yana mai mata wani irin fresh kiss da ya nema zautar da ita. Sai da ya tabbatar ya samu wata nutsuwar sannan ya barta suka koma sauke numfashi. agogo ta kalla zuciyarta na raunana ganin lokacin fitarta girki yayi. Dan kuwa ya tabbatar musu daga 6 na yamma ne. Jitai inama ta jawo mintunan su koma baya, dan wata irin matsananciyar buƙatarsa takeji saboda ya sakata a cakwakiya. Sanin komai zai iya faruwa ta fita da sauri tana faɗin tana zuwa. Murmushi yayi har hakwaransa na bayyana ya bita da kallo……

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button