BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

   
          ★A lokacin da Fadwa ke can tana kuka da tunanin kasancewarsu a tsakkiyar lambun fure mafi girman daraja a garesu ba hakan baneba. Anam ta jima zaune akan sofa barci na rinjayarta tsoro na fisgota, sai dai bata da wata mafita ko ƙwarin gwiwa saboda babu ɓarawo mafi iya sata kamarsa. Kujerar 1sitter ce guda biyu, hakan yasa bata samu gamsuwar kwanciyarba duk da ta naɗe dukan jikinta a kanta. Daga inda yake kwance yaka hango yanda take mutsu-mutsu tamkar magen data sha matsa a hanun mafarauta. Guntun murmushi kawai ya saki, akan laɓɓansa ya furta “Azababbiyar yarinya”. Yana lumshe idanunsa dake cike da barci. Kusan mintuna goma ya bata domin barcinta ya ƙara nauyi sannan ya miƙe a hankali ya taka gareta. Cikin dabara ya ɗagata gaba ɗayanta yakai saman gadon ya kwantar yana danne dariya. Shi baima taɓa tunanin tanada nauyin barci hakaba, hijjab ɗin ya zare mata sannan yaja mata bargo shima ya koma ya kwanta yana sauke ajiyar zuciya. Tsakanin Anam da Fadwa bai san wanene yafi wani daru ba. Itama yaso zuwa sashenta yay mata sai da safe amma tsoron abinda zai tarar ya sakashi haƙura. Bai taɓa tunanin da gaske MAZA najin shakkar matansu a irin wannan lokacin ba, dan duk yanda yake jin kansa da mazantakarsa da ƙin ɗaukar shirme sai nauyi da kunyar Fadwa ke zagaye da jininsa duk da auren nasa yazo a cikin wani kashine da yasha banban dana sauran maza mafi yawa irinsa.
Numfashi ya furzar a hankali da juyowa gaba ɗayansa yana facing ɗinta, kallon fuskarta yake a cikin wani irin yanayi mai sanyi da zungurar zuciya, ya matsar da fuskarsa gab da tata tare da saƙala hanunsa saman jikinta ya rungumota a nasa jikin sosai, kamar wadda aka isarwa da saƙo ta buɗe ido, sai dai rashin ganinsa da ƙyau ya sata jan numfashi ta haɗiye tare da nasa da yake busa mata saman fuska. Jan jikinta tasoyi baya ya ƙara matseta.
“Yay……”
Kalmar ta kasa ƙarasuwa a zahiri tamkar yanda taso furtawa sai a cikin bakinsa, ba ƙaramin bugawa zuciyar Anaam tayi ba, duk da abinda takema tsoro kenan tun farko dama hakan bai hanata jin mamaki da shiga bazata ba. Bata da wani ƙarfin ƙwatar kanta, sai ma ƙoƙarin zare mata duk wani kuzarinta da razani yake ta hanyar cigaba da sarrafata a wani salo mai kashe jiki da ruguza dukkan alwashi na duk ɗiya mace mai lafiya. Tun tana iya cijewa harta fara amsar salon nasa dan takai shekarun da gangar jikinta ke a matuƙar buƙatar fiye da hakan ma. Sosai ya fitar da ita daga hayyacinta tamkar yanda shima nashi hankalin ya barranta da gangar jikinsa da zahirin rayuwarsa……….✍

ZAFAFA BIYAR

INAYAH
MamuhGee

GURBIN IDO
Safiya Huguma

SANADIN LABARINA
Hafsat Rano

FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)

BABU SO
Billyn Abdul

Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: Typing????

  *_❤‍????BABU SO....!!❤‍????_*
             _(Miya kawo kishi?)_



          *_Bilyn Abdull ce????????_*

BABU SO????????AREWABOOKS

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

45

………Saukar hanunsa a wani sashe na jikinta ya sakata dawowa hayyacinta babu shiri, ta damƙe hanunsa da fisgar kanta baya tana sauke numfashi da sauri-sauri kamar yanda shima yake sauke nasan. Kunya tsoro da firgici suka zagaye zuciyarta a lokaci guda. Jin abin take gin-girin-gin tamkar a mafarki, bargo taja da sauri ta naɗe jikinta da juya masa baya amma sai ji tai ya riƙota, maidota yay jikinsa har yanzu yana kokawa da numfashinsa da bai gama daidaita ba. So take tace wani abu tsoro ya hanata, sai jujjuya masa kai take alamar ya barta.
       “Ni ba’a juyamin baya yayin kwanciya”.
   Ya faɗa cikin kunnenta da sake matseta a cikin jikinsa yanda bazata iya ko motsi mai ƙyau ba. Bata da zaɓin daya wuce yin shiru, dan tasan babu wani yunƙurinta da zaiyi tasiri tunda ruwa ba sa’an kwando bane. Sai dai kuma bata samu nutsuwar yin barci ba har sai da taji shi yayi..

        Rashin kwanciya da wuri baisa ta gagara tashi alokacin da sanyin asuba ya busa cikin ƙofofin fatar jikinta ya kaima jininta saƙo ba. Ta buɗe idanu a hankali tare da ƙoƙarin yin miƙa da tabbacin ta mance inda take. Rashin gani da ƙyau sakamakon duhun ɗakin ya taimakawa zuciyarta harbawa da ƙarfi irin na razana. Da sauri ta sauke hanunta kan abinda ƙwaƙwalwarta ta bata tabbacin mutum ne. Firgicin lokaci guda ya hanata damar tunawa balle yin nazari tai zaburar data farkar da shi daddaɗan barcin daya riskesa fiye dana farkon dare….
        Cikin zafin nama ya maidata jikinsa ya matse tare da kai ɗayan hanunsa ga makunnar fitila ya kunna. Tabbas badan hakan da yay ba babu abinda zai hanata wantsalawa ƙasa sakamakon gab suke da gefen gado ashe.
    “Relax!” 
  Ya faɗa cikin sarƙewar muryar wanda ya farka a barci, domin samar da nutsuwa daga mutsu-mutsun data cigaba dayi har yana iya jin yanda zuciyarta ke harbawa da sauri-sauri akan ƙirjinsa. Babu alamar zata nutsu ɗin, dan jin muryar tasa ma da alama sake hargitsata yay a dalilin ganewa da tuna komai mai alaƙa da inda take. Sarai ya fahimci yanzu ba tsoron bane, borin kunyane kawai tattare da ita, dan duk ƙoƙarin da yake na son tama buɗe ido ta dubesa hakan ya gagara, sai faman san zame jikinta take da nashi da kuma ƙoƙarin hana ƙirjinta sauka kan nasa ta hanyar tokare tsakaninsu da hannayenta. Dariya sosai ta bashi, amma sai ya gimtse baiyiba ya matsa kaɗan daga gareta. Damar data samu kenan ta wantsala gefe faɗuwar dai daya gudar mata tun farko sai gata tayita, zafin daya ratsata ya sata sakin ƴar ƙara. Yanzun kam bai iya daurewa ba sai da ya murmusa, batare da yace mata komai ba ya tashi yay shigewarsa bayi har lokacin da murmushin akan fuskar tasa.
        Sai da ta gama ƴan matse-matsen hawayenta sannan tai wuf ta miƙe jin kamar alanar zai fito, key ɗin da idonta ya gani a gadon ta ɗauka ta nufi ƙofa da sauri hijjab ɗinta a hannu da galashinta da shima ALLAH ya bata sa’ar gani. Fitowarsa dai-dai da ficewarta a ɗakin…..

       Bayan idar da salla tagumi ta zabga ranta fal takaicin abin kunyar daya faru a ɗakin Yaya MM daren jiya, ta rintse idanunta dake cikin glass tana cije lips kamar ta tariyo komai ta goge a rayuwa da zuciyarta ko zata samu sukuni. Tamkar tana a gabansa ta murguɗa baki da miƙewa, tana naɗe sallayar tana mita cikin yaren malay. “Idan kaga ma na sake kallon hanyar sashen can naka ba riƙeni na kwana ba kace har abada bazan fitoba ma mana, ko kunya bayaji yana mazurai da zare ido amma zuciyarsa saninta sai ALLAH. Toni an faɗa masa waccan shashashar matar tasa ce dake hauka akansa, mtsoww! Tana wani fiffika ita mai miji kamar ance ana son mijin natane balle ra’ayin zama da shi. Aikin ɓurr miye abin so jikin wannan mutumin mai baƙin hali, sai dai ita ɗin dan dama duk jirgi ɗaya ya kwaso su mtsoww!!”. Haka ta dinga mitar har takai kwance kan gado, kasancewar barci ne taf da idon nata cikin ƙanƙanin lokaci yay awan gaba da ita tsiwa fal bakinta daya tashi sama kamar zai taɓo p.o.p.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button