BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

 Humm, yau fa akeyinta????????????????????????.

ZAFAFA BIYAR

INAYAH
MamuhGee

GURBIN IDO
Safiya Huguma

SANADIN LABARINA
Hafsat Rano

FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)

BABU SO
Billyn Abdul

Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: Typing????

  *_❤‍????BABU SO....!!❤‍????_*
             _(Miya kawo kishi?)_



          *_Bilyn Abdull ce????????_*

BABU SO????????AREWABOOKS

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

74

…….Dariya kawai yake dannewa dan sarai duk ya gama fahimtar inda ta dosa. Sai dai shi yasan a yau bawai zai iya haƙuri bane gara ya maidata ƴar hannu a wuce wajen. Amma a zahiri ya basar tamkar bai san mitake ba. Dan koda ya kammala shan shayin toilet ya shiga ya dauro alwala. Shafa’i da wutiri yayi sannan ya hawo gadon bayan ya fita ya leƙa tsakar gidan ta windows ɗinsa na falo. Ganin babu wani damuwa ya dawo bedroom ɗin shima ya hau gadon ya kwanta. A hankali ya kwanto bayanta yana mai ɗaga duvet din da taja har saman kanta.
       “Bana faɗa miki ni ba’a juyamin baya a gado ba?”.
    Shiru tai ita ala dole tayi barci. Yaji a jikinsa pretending ne kawai, dan haka ya fara mata cakulkule. Duk yanda taso fiskewa hakan ya gagara, dole ta fara dariya da ture hanunsa. Bai bartaba har sai da yaga ta juyo yanda yake bukata. Ya haɗe goshinsu waje guda yana murmushi. “Ni na rasa miyasa kika rainani”.
          “Saboda kana mun mugunta mana”. Ta faɗa tana murmushi.
  “Kin cika tsokana ne shiyyasa”.
Hanunsa da yake cusawa jikinta ta mintsina. “Ouch!!”. Ya faɗa batare daya janye ba. Murmushi tayi zata kauda kanta ya riƙo fuskar. Duk yanda taso ƙwacewa babu damar hakan. Dan wani salo ya ɗauka wanda yasha banban da karatun farko daya koya mata. Cikin kankanin lokaci ya sakata sakin masa jiki ya fara yanda yake so. Tafiya tayi tafiya sun gama cakuɗa juna yanda suke so ya ɗauka babban hanyar garden. Ai tuni mutuniyar taku ta fara sakin magiya da roƙo amma ya nuna mata sam yau babu ɗaga ƙafa garden zai sake komawa ziyara. Hankalinta bai kara tashi ba sai da taji yana ambaton addu’a…
      Wiya kam dai yau ma ta shata, duk da dai ba irin ta farko bace dan babu ma haɗi, dan yau ya bita a hankali kamar yanda Dr Bilkisu ta gargaɗesa. Yau din ma dai harda kukanta. Amma baiyi nisaba kamar na waccan ranar. Tasha albarka kala-kala tare da daɗaɗan kalaman da suka sanyaya mata rai raɗaɗin taji ya raguma. ya taimaka mata ta shiga ruwan zafi kafin su dawo gadon ya bita da tukuycin tausar data sakata yin barci. Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi da sake sakar mata kiss a lips da idanunta yana faɗin, “ALLAH yay miki albarka”. Daga haka shima ya rungumeta suka lula duniyar barcin tare..

    WASHE GARI

  
Rashin sabon ɗaukar gabaran gida kafin fita aiki yasa saida taimakonsa dana Aysha suka shirya fita akan lokaci, gashi sai langaɓewa take wai jiya ya wahal da ita. Shi dai nashi murmushi kawai, itako tana faman tura baki da tsuke fuska. Kamar kullum tayi ƙyau cikin kayan hidimar ƙasa, sai dai ta ɗaura Abaya yau a sama sannan ta naɗa veil ɗin abayar a kanta. Ƙin fitowa tai har saida ya shiga sashen Fadwa sukai sallama ya fito sannan ta fito suka wuce. A hanya take tambayarsa yaushe zata fara koyan tata motar. Shiru kamar bazaice komai ba. Sai da ya kaucema mai napep ɗin dake neman shiga masa hannu sannan ya ɗan dubeta bayan yaja tsaki da yima mai napep ɗin daƙuwa.
“Mu bari weekend, idan kuma Fadwa ta koya miki to?”.
Baki ta tura gaba sai dai batace komai ba. Hakan yasashi fahimtar zancen nasa bai amsu ba. Ya girgiza kai kawai ransa fal mamakin kishin matan nasa. Ita kanta Fadwan daru ya barta tanayi akan fitar tashi da Anaam. Wai sai dai idan ranar girkintane kawai zasuke tafiya tare. Amma ranar nata bata yarda ba. Itama baice mata komaiba yay fitowarsa, to ga Anaam ɗin ma yace Fadwa ta koya mata mota ta nuna bata so.
Ita ya fara saukewa, da gargaɗi mai girma akan Yaseer sannan yay gaba. Ya samu tarba ta musamman a wajen staffs nashi. Inda sukai ƴar gajeriyar walima lokacin break acewarsu tunda ba’ai ta aure ba. Kasancewar ya samu aiki da yawa Khaleel ne yaje ya maida Anaam gida, shiko sai bayan isha’i ma ya kona gidan. Sanda ya iso ya iske komai yanda yake buƙata, dan dawowar Anaam ɗin tayi amfani sosai.
Yau ɗin ma dai yasha sharafinsa, inda mutuniyar tasa taita masa raki, baibi takanta ba, amma yabita a sannu gudun ɓaro aiki. Washe gari har wani farin ciki takeji zai koma wajen Fadwa ta huta, duk da dai kishinsa na zaune daram a ranta babu sassauci. Safiyar talata sai dai yayma Fadwa ƙaramin hauka akan fitarsa da Anaam sannan suka samu dai-daito, dan ta dage bazai ɗauka Anaam ba dan ranar girkintane. Amma ganin ya juye mata yanda bata kauna dole tai shiru, ya fita ya barta tana rusar kuka

    Haka kwanaki suka cigaba da tafiya, tun Anaam na masa raki a duk ranar girkinta harta fara zama ƴar hannu, duk salon da yazo mata da shi zata amsa kuma ta bashi haɗin kai yanda zai samu farin ciki. Babu abinda ya dameta da sabgar Fadwa, abinda ke gabanta kawai takeyi, sai dai kuma bata ragawa idan Fadwan ta shiga shirginta. Dan kuwa saita tsefeta tas ake samun zaman lafiya a gidan. Shareff yayi kurarin yayi masifar akan tsiwarta amma a banza, dan tace in ba'a shiga gonartaba bazata shiga ta mutum ba. Ita kuma Fadwa tsokanar magana ne matsalarta. Komai ta gani saita tanka. Duk kankantarsa sai tayi magana ga Shareff ɗin ko ga Anaam. Sauki ɗaya aka samu ta rage kai ƙararsa wajen iyaye, koda yake yanzu fa itada Mommy babu wani mutunci, dan kuwa ranar daya kaisu gidan su duka domin gaishesu Anaam tasha kallo, Mommy ta dinga yamutse-yamutse, abibda ya bata dariya Fadwa zata fara iyayi ita masu Mommy, mommy ta gwaleta. Aiko ta fita baki gumtse tana danne dariya. Tuni ta gudu gidansu wajen Mamie, inda ta ruƙunƙumesu harda kukanta wai tayi missing nasu. Suma sunyi missing nata matuƙa, amma sai suka dinga lallashinta. lokacin da Fadwa da Shareff suka shigo gaida su Abie ɗin kowa yayi mamaki Fadwa, dan yau babu rashin kunya ta gaishesu da girmamawa saboda tsoron butsutsun Shareff, dan kafin su taho ya buga mata warning bana wasa ba akan su Abie ɗin. Sai kuma abinda Mommy tai mata a gaban Anaam ya sake dagula mata lissafi.

 Zuwansu gidan da kwana biyu maganar auren Bibah da Shareff ta fito, dan kuwa a kwanakin nan dama sunata bugawa ne tsakaninsa da su Mommy, ta kuma tabbatar masa idan yana fa son zama da matansa sai ya auri Bibah, a gefe kuwa burinta ita da Gwaggo ya auri Bibahn su fidda Fadwa da Anaam kuma a gidan dan sun ɗau alwashin bazasu barshi zama da su ba. 

  Wannan maganar aure itace ta tada gagarumar ƙurar data tada hankalin kowa a family guda biyu, dan kuwa sarƙa-sarƙar tayi yawa ai. Saboda Shareff na ɗan gatan duniya sai a dinga haɗa masa ƴaƴan dangi yana aure dai. Mamie da Abie dai basu ce komai ba, sun kuma yima Anaam nasiha akan koda a fuska karta nunama Shareff komai. Taji ciwo a ranta, sannan taci kuka amma sai tabi maganar iyayenta.
 A ɓangaren Gwaggo Halima kuwa sabon yaƙi ne ya tashi tsakaninta da su Mommy, nanfa aka shiga ƴar tone tonen asiri ta yanda har akaima Shareff asirin daya nisantashi da su Abie. Abubuwa dai babu daɗi, dan tsabar takaicinsu Daddy har sai da yaji ƙwalla sun cika masa ido. Gwaggo Halima tace sai Fadwa ta koma gida babanta yace ƙarya haramun, idan Fadwa ta rrabuda Shareff ta nema wani uban bashi ba. To itama dai tana son mijinta, duk da kuwa maganar zai ƙara aure yake, kuma da kawarta data san sirrikanta.
  Ruguntsumin masifa akeci na haƙiƙa a wannan gaɓa tsakanin Fadwa da Bibah, Gwaggo Halima da su Mommy da maman bibah. A gefe kuma ga shirye-shiryen bikin Aysha, sai kuma Khaleel da tasa budurwar shima. Sosai hankalin Shareff ya kasu. Ga company, ga rikicin Mommy da Gwaggo data noƙe tabar Mommy na raba hali. Ga rikicin Fadwa, Dan ita Anaam da sauƙi. Bata fasa komai da take masa ba amma yabar ganin murmushinta gaba ɗaya itama. Dama zuwa yanzu da motarta take fita wajen aiki kasancewar ta ƙware, dan bai kulla sati biyu yana koya mataba da yake ta saka kanta sai gashi ta iya, idan zasu fita yana gaba tana biye da shi, komuma tana gaban yana biye da ita duk dai dan ta ƙara sanin hanya.
  An shiga shagalin bikin Aysha ne cikin ruguntsumin maganar Bibah, amma hakan bai hana Shareff sharɗantama matan nasa zuwa taron bikin ba. To Anaam ma basai an sharɗanta mata ba. Bikin Aminiya ya wuce tace bata zuwa, hakama Yaya Khaleel. Dan haka tun ranar kamu tace masa zata koma can gidan gaba ɗaya har sai biki ya tashi. Da farko yace bai amince ba, tako saka masa kuka. Da farko shareta yayi, sai dai ganin kukan nata bana kare bane yace taje cikin fushi. Sai kuma jikinta yay sanyi.
  Yayi zaton zai taso aiki ya tarar ta wuce, sai ya samu tana gida babu ma niyyar tafiyar tare da ita. Ganin kallon da yake binta da shi ya sata tunzura baki gaba ta ɗauke kanta gefe.

Baki ya ɗan taɓe, “Motar ce babu mai komi?”.
“Ni na fasa”.
Ta faɗa idonta na cikowa da ƙwalla.
“Dalili?”.
Kuka ta fashe masa dashi. “Toni ya kake so nayine dan ALLAH Yaya. Taya zanje wani waje kana jin haushina. Salon kawai kasa ALLAH ya sakani a wuta”.
Ɗan murmushi yayi da girgiza kansa yana furzar da huci. “Ni bance ina fushi dake ba kar kimun sharri, kune dai kuke fushi dani akan abinda na tabbatar muku nima bana ra’ayinsa. Mi zanyi da wata Bibah can da har zamu zauna kuna dagula min lissafi. Kun haɗe kai ku a dole bakwa son kishiya. Kun san tun yaushe ake maganar nan ina ta yaƙin ganin bata fitaba? amma kuke ɗaukar laifi kuna ɗauramin. Koda yake ke nagama kamar baki damu da zuwan amaryar tawa ba, dan kwanakin nan wata ƙiba kikeyi da haske ƙyawu na musamman na fita a fuskarki, kamar wata black American”.
Throw pillows ta ɗauka ta fara jefa masa. Ya shiga karewa yana dariya. Ganin haka ya sata mikewa ta haye kansa tana cigaba da kai masa kananun duka da pillow. Dariya yake mata da son kwace filon yana karewa, har dai ALLAH ya bashi sa’a ya damƙe hanun ya mirgina ta koma ƙasa yana a sama. Turesa ta farayi shi kuma yana kai mata kisses a wuyanta zuwa ƙirji. Kukan shagwaɓa ta fara masa ya koma mata cakulkule dole ta fara ƙyarƙyala dariya. Daga haka labarin ya canja aka koma neman lada. Dama a kame yake kwanakin nan ko nauyi bai iya saukewa saboda zafin da kansa ya ɗauka matuƙa…………✍

ZAFAFA BIYAR

INAYAH
MamuhGee

GURBIN IDO
Safiya Huguma

SANADIN LABARINA
Hafsat Rano

FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)

BABU SO
Billyn Abdul

Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: BABU SO
Chapter 77
77

……..Kaɗan ya rage zuciyar Fadwa yin tsale ta fito, jikinta na rawa tace, “Wlhy ƙaryane, munafukar tsohuwa da bazataga MANZON ALLAH ba”.

  Saukar mari taji lafiyayye daga Mahaifinta. Gwaggo ta jinjina kanta cike da jin daɗi, “Nagode Sadiqu. Ba laifinta bane uwace bata moraba. Yo dama yaushe Halima taga wata tarbiyya balle ta bata. Ai bakai dace da mata ba wlhy”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button