BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

  Idanun ta ƙara warowa sosai “Are you ok?”.

 “I’m not…”.

Ya bata amsa a taƙaice yana danne dariyarsa dan da gaske tayi bala’in diriricewa. Tsabar son ƙureta abincin ya ɗibo yakai bakinta. Da sauri takai hannu zata kare. “Idan kikaƙi amsa ALLAH cak zan maidoki jikina sannan na baki wanda na tauna a bakina kuma a gabanta harda tsotse lipstick ɗina”.

    Yanda ta saki baki da hanci tana kallonsa ya sashi dungure mata kai yana murmushi, tana buɗe baki da nufin yin magana ya juye mata shi. Dole tai saurin rufe lips ɗinta dakai hannu ta kare bakinta. Dai-dai nan Aysha da ta wuce kitchen batare da sun sani ba ta dire babban tray data shirya abinci kamar yanda akema kowanne magidanci a saman centre table ɗin gabansu. Lokaci guda suka sauke ajiyar zuciya, Anaam ta kalleta shiko ya fiske fuskarsa na komawa normal kamar ba shine ke murmushin ba.

    Aysha na ƙoƙarin barin falon Anaam tai saurin faɗin, “Blood ina kuma zaki? Kizo muci abincin mu”. Da sauri Aysha ta shige bedroom ɗin baƙi kamar ma bata jita ba. 

  “Yaya ka gani fa ka koreta?”.

“So take ki samu ladan da mata ke samu kema, tunda garden ɗina kin haɗa baki da doctor ɗin can kar naje barruwa.”

  Maganarsa ta farko kawai ta fahimta. Dan haka cike da basarwa ta bashi amsa. “Matarka ai tana dafa maka ta samu ladan, kaga ya wadatar da kai ai”.

    Shima fahimtar hakan ya sashi juya harshe zuwa yaren Maley.

 “Ke minene naki sunan?”.

   “Kanwarka kaima da kowa an sani”.

    “Really?”.

  “Yap!”.

“Idan suka ganki da tsarabar furen garden sai su cireni a jerin Yayun naki ai ok”.

   “Kai ka san wani garden Yaya”.

“Kema kin sanshi sai dai ƙari. Ni fa janbakin nan ya tsolemun ido a bani na shanye kayana k……”

  Abincin data ɗebo ta juye masa a baki kamar yanda yay mata shima ɗazun, dole ya haɗiye sauran maganar itako ta shiga ƙyalƙyala dariya dan lauma babba ne……..✍

Next Chapter

Leave a comment

Post

Comments
No Comments posted yet

Contact Us
Arewa Books Publishers

WhatsApp: 09031774742

Email: arewabookspublishers@gmail.com

Navigation
Home
About
FAQ’s
Legal
Privacy Policy
Terms of Service
Social
Facebook
Instagram

Copyright 2021, Arewa Books | ALL RIGHTS RESERVED | Powered by thinkcrypt.io

63
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: BABU SO
Chapter 62

………A waje suka sami aunty Mimi tare da Dr Bilkisu. Khaleel ne yazo ɗaukarta ita gida zata wuce. Anaam ta shiga zazzame jikinta a nasa amma yaƙi sakinta har sai da ya sakata a mota. Ya ranƙwafo zai sumbaceta ta kauce tana faɗin “Kai yaya wai bakajin kunyar aunty mimi”. 

   Kai ya kaɗa mata da lumshe idanunsa “Ƴar kaɗan”.

 “Kake jin kunyar tata?”. Ta tambaya cikin sigar waro masa idanu. 

“Eh mana ba mamata bace. Ba buƙartar na ɓoye mata muhimmancin autar mata ai”.

    Rufe fuskarta tai da tafukan hannayenta tana murmushi. “Ni dai babu ruwana”

  Murmushi yay da sumbatar kunenta. Ƙarasowar Aunty Mimi wajen ya sakashi ɗagowa. Sai lokacin takejin batare da Aunty mimi zasu tafi ba. Fuska ta kwabe da rokonsa zatabi aunty mimi ama yaki. Sai kawai ta kama hawaye.

   ★Shiru babu mai magana a motar har suka iso gida. Har mai rake ta gani tana so amma ta gwammace tai haƙuri da tace ya tsaya ya siya mata. Itace ta fara fita a motar tun kafinma ya kashe, daga shi har Aysha suka bita da kallo. A ransa ya ayyana (Ni nasan maganinki yarinya).

  Aysha ce ta kwashi kayansu, a dai-dai lokacin Fadwa ta fito daga sashenta dama tana laɓe duk tana kallonsu tun shigowar motar gidan. Tayi ƙyau cikin kwalliya sai baza ƙamshi ake. Tai masa sannu da zuwa Aysha ta gaisheta. Itace ta taya Ayshan kwashe kayan zuwa sashen Anaam ɗin. Sun sameta kwance cikin kujera ido a rufe kamar mai barci, kuka take son tayi akan hanata bin aunty mimi amma yaƙi ya fito, shine tai luff a wajen zuciyarta na suya. Sallamarsu baisa ta buɗe idanun nata ba, har sai da Fadwa tace mata ya jiki. Ciki-ciki ta amsa mata, Fadwan ta nuna kamar bata damuba ta sake mata addu’a sannan ta fice.

   Aysha datai tagumi ta girgiza kai kawai. Tashi tai ta fara gyaran sashen duk da bawani datti bane ba. Harta kammala da falo ta koma bedrooms Anaam na’a wajen kwance, Shareff kuma bai shigo ba. Ayshar ce bayan kammala aikin nata ta fito tace mata ta tashi taje tai wanka ga ruwa can ta haɗa mata. Batare data tanka mata ba ta miƙe. “Ki fara shiga ruwan zafin kamar yanda doctor tace.”

  Kanta kawai ta jinjina mata tai shigewarta. Aysha ta bita da kallo cikin tausayi, dan ita tausayi take bata, saboda ta fahimci abinda Anaam ɗin ke gudu danta jigata a matuƙa a hanun Yaya Shareff ɗin.

  Shigowarsa ce ta katse mata tunani, yabi falon da take bazama turare da kallo, sai dai baice komai ba yakai zaune.

   Burner ɗin Aysha ta ajiye da nufar kitchen, babu jimawa ta dawo ɗauke da ruwan. Zata zuba a kofi ya karɓa goran ruwan, murfin kawai ya buɗe ya kafa kai. Bai ajiye ba sai da ya shanyesa tas, da alama ƙishin yakeji dama. Sai lokacin yace, “Tana ina?”.

  “Tana ciki yin wanka”.

Ƙofar ya kalla na wasu ƴan sakanni, sai kuma ya miƙe. “Ki shirya zuwa anjima saina maidaki gida”.

  Da to ta amsa masa. Shi kuma ya shige corridor ɗin bedrooms ɗin Anaam. Tana faman ƙunƙunin ruwan da Aysha ta zuba mata na sit bath yayi zafi da yawa ya shigo, cikin sauri ta juyo kuma a rikice dan babu komai a jikinta. Daburcewa tai gaba ɗaya tama rasa ina zata saka hannu ta rufe, yi yay tamkar bai ganta ba, ya ƙaraso cikin toilet ɗin. Ruwan da take sirkawa ya sakama hannu, ya ɗago yana kallonta. Juyar da kanta tai gefe da ƙara tsuke fuska. 

   “Humm” 

Kawai yace ya fara ƙara ruwan zafin. 

 “Yayi zafi fa da yawa”.

Ta faɗa da sauri kamar zatai kuka. Dai-dai nan ya ɗago dan ya masa yanda yake buƙata, da sauri ta yunƙura zata fice ya damƙota, ƙoƙarin ture hanunsa ta shigayi tana wani ciccijewa ita a dole bata wasa bace. A karon farko ya saki murmushi, hannun nata ya saki ya damƙe towel ɗin, ta ɗago a matuƙar firgice tana kallonsa. Ido ɗaya ya kashe mata da cije gefen lips ɗinsa shima, dole ta kauda kanta dan salon nasa saida tsigar jikinsa ta tashi. Matsota yay tare da ranƙwafowa bakinsa saitin kunnenta. 

   “Bakin ya mutu ne ƴammata?”.

Fuskarta ta sake kaudawa gefe da son ƙwace hanunta. Sai kawai jitai ya since towel ɗin nata. Ruɗewa tai, tai ƙasa zata duƙe ya ɗagata cak ya dire a ruwan zafin. Azabar data ratsata ta zafin ruwan ta sakata sakin ƙaramar ƙara mai kama da kukan shagwaɓa. Matso da fuskarsa yay gab da tata, saukar numfashinsa akan tata fuskar ya sata ɗan buɗe idanunta dake rufe, dai-dai lips ɗinsa na sauka kan nata, sai kawai jikinta ya hau rawa. Ya cigaba da binta a wani salo daya saka jikinta saki lokaci guda, sai dai bai samu haɗin kanta ba kamar yanda yake buƙata. Bai damu ba ya cigaba da sarrafata a hakan tunda dai saƙonsa na isa kamar yanda yake buƙata. Nisan tafiyar ya sakata tuna azabar da tasha a daren shekaranjiya, ga gargaɗin doctor na ta kiyaye har sai ciwonta ya warke. Kota warke ɗin ba buƙata take ba balle yanzun. Laushin da gaɓɓansa sukai ne ya bata damar janye jikinta, ta miƙe zumbur jikinta na ɓari. Bashi da zaɓin daya wuce shima miƙewar, ta nane da bango tana girgiza masa kai ganin ya ɗago idanunsa da sukai matuƙar canja launi yana zuba mata.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button