BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

Sabon kuka ta ɓarke da shi tana zayyana mata
abinda ya faru, harda kiran Mommy datai
amma ta yanke mata waya…
“Kan ubancan, mi Nafi ke nufi Share! ya
mareki ya mari banza?. A to lallai idan tace wannan layin zamubi ni da ita bazatai mana ƙyau ba. Ai dama su Malika sun tabbatar min abinda yafi hakama zai iya faruwa saboda Nafi maciji ce da fuskar tana. Aiko zan tabbatar mata Share! bai mareki a banzaba dan wlhy saina rama miki”. Ta yanke wayar.
★Sai da Gwaggo ta gama sauraren Mommy data isa sashenta a rikice tsaf sannan ta saki murmushi irin nasu na tso!in makirai. Domin kuwa anzo gaɓar da ta jima tana jira kenan. Kallon Mommy tai da dafa kafaɗarta. “Nafisa Halima zata iya fiye da haka domin wannan ƴar tata. Jikina ya fara sanyi da al’amarinta tun lokacin zubewar cikin Fadwa. Karki manta itace ta fara kawo shawarar a sami malamin dazai aiki akan Mustapha da yarinyarnan ta wajen Usman. Abinda yasa naƙi yarda a lokacin na tabbatar idan muka biye mata wataran zata haɗo wani abin a bama Share! yaci a zuwan dan ana son rabashi da Zuwaira ne. Ki tuna Halima ƙudace, domin samun biyan bukatarta rai ba’a bakin komai yake ba.

Tunda kuma ta haɗa kai dasu Malika to komai zai iya faruwa da Mustapha ciki harda rabashi da ke kanki uwarsa, dan kuwa ke shaidace, nice na haɗa auren Halima da Sadiqu, amma gashi nan babu mai cin dukiyarsa daga ita sai ƴaƴanta sai wanda ta zaɓa a dangi. Gasu Muhammadu nan ƴan uwanta tasan yanda zata samesu gefe ta kalallame ta dawo wajenmu tana nuna mana tana tare damu. Kin dai san duk son da Halima zatamana bai kai ya na ƴan uwanta ba tunda ba haihuwarsu nayi ba. Kuma kodan wannan dukiyar dake zagaye da Mustapha ai Halima bataso zaunawa ba tunda tasan yanda ta mallake Sadiqu dolene itama ƴarta ta mallaki Mustapha yanda koke kanki bai isa yaji maganarki ba, danni tawa mai sauƙice kwana nawa ya rage ALLAH na tuba”.
Kalaman Gwaggo ba karamin hautsuna zuciyar Mommy sukai ba. Gaba ɗaya tama rasa ina zata kama ta riƙe a wannan gaɓar. Shigowar kiran Gwaggo Halima ya saka tunaninta katsewa. Ta dubi Gwaggo, “Itace fa take kirana”.
“Ɗaga muji mizata faɗa, nasan dai ƴar tata ta kirata itama ai”.
Dagawa Mommy tayi, ta saka hansfree yanda itama Gwaggo zata iya ji. Daga can Gwaggo

Halima dake a wuya muryarta a shaƙe ta fara
magana batare da ko gaisuwa ba. “Yanzu
Fadwa ke kirana Share! ya mareta, tace kuma
ta kiraki ta sanar miki amma bakice komaiba
kin yanke waya. Kome hakan ke nufi kenan?”. A harzuke Mommy ta maida mata murtani.
“Abinda duk zuciyarki ta baki Halima. Nifa
bazan ɓoye miki ba na gaji da yawan kai ƙarar
Fadwa. Ita kullum bazata iya haƙuri da miji ba
saita kawo kararsa. Ko haka taga wani a
cikinmu nayi? Sannan kin tambayetama mita
masan ya mareta? Taya zata kai masa ƙawaye
ɗakinsa na sirri su gyara saboda rashin sanin
ciwon kai. Ni yamun dai-dai, kinga gobe idan
ta sake saiya mata dukan tsiyama ba mari ba.
Sannan Halima ki sani, dukkan ƙulle-ƙullen
da kukeyi ke da su Malika naji kuma na
sani……”
“To idan kinji kin sani ɗin sai yaya Nafi? Kin
goya bayan ɗanki akan marin da yay yarinyata ma, to wlhy ki sani da hannuna zan rama mata marin da yay mata, idan shi ɗin mahaukacine zan maidosa hankalinsa kuwa. Kuma karki manta duk wani ƙulli da tuggunki a tafin hanunna suke, ko dama wanzami baya son jarfa ne, yanda kika mallakemin ɗan uwa kike tunanin ke naki ɗan bazai mallaku ba. Hhhhh Nafi idan kikace wannan layin zamubi

ni da ke akan Share! da Fadwa wlhy muje
zuwa ɗan halak ka fasa….”
“Halima idan kin isa ke tujararriyace mu
zuba ɗin dan ALLAH, ni dake za’aga mai iko akan wannan auren. Shiyyasa dama ni tun farko ban so wannan haɗin ba kika katsatstsare ke da Gwaggo sai anyisa. Bayan nasa ƴarki bata da tarbiyya ko misƙala zarratin..”
“Matsalarkuce kuma wannan, ni nagama dake kuma muje zuwa ɗan halak ka fasa”. Gwaggo Halima ta faɗa da yanke wayar. Wani jijjiga Mommy tai zata maka wayar da ƙasa Gwaggo ta riƙeta.
“Kefa daɗina dake baki da hankali idan ranki ya ɓaci, ki nutsu, har mi akai kai Halima ne ma. Ai wannan yaƙin namune gaba ɗaya, shiyyasa naita nuna miki ki kwantar da hankalinki akan haukan da kike na tsinema Mustapha a banza saboda farin cikin Halima da ƴarta. To gashi nan tun ba’aje ko’inaba sun fara nuna miki halinsu”.
Kukan takaici da baƙin ciki Mommy ta fashe da shi………..
Ashe haka duniya take ƙafar kazace. Aminai biyu ya hakane ? Yanzune fa wasan na ainahi zai fara, dan za’ai yunwa muga cikin

kowa .
Next Chapter
Leave a comment
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: 70
BABU SO
Chapter: 70 Share:
Report
BABU SO View: 283 Words: 2K
Chapter 70 70
……..Wasa farin girki wai amarya da tuƙa

tuwon tiya goma. Ashe rikici a waya tsakanin Mommy da Gwaggo Halima somin taɓi ne. Dan kuwa ba’a rufa awa guda cikakkiya ba sai ga Gwaggo Halima tazo gidan. Hakan yayi dai- dai da dawowar Daddy daga wajen aiki gidan shima. Yay sagade yana kallon Gwaggo
Halima data ƙaraso garesa tana huci. “Halima lafiya kuwa da magribar nan?”. “Inafa lafiya Yaya, Share! ya buɗe ƙwanji ya
shashsheka ma Fadwa mari amma saboda
son zuciya irin na matarka ta goya bayansa
saboda itace ta haifesa”.
Da mamaki sosai yace, “Mari fa dai? Ya
ALLAH mike damun Share! haka? Wannan ba
maganar nan bace shiga ciki nafara zuwa salla
kafin su Abubakar su dawo”.
A maimakon sashen Mommy ko Gwaggo da
da idan tazo gidan take shiga yau sai ta nufi sashen Mom…..
____
Rashin fitowarsa har aka kira sallar magrib yasaka Anaam kasa zaune ta kasa tsaye. Tana son zuwa dubashi tanajin tsoro. Gani take kamar itama ɗin marin nata zaiyi. Harga ALLAH tana matuƙar tsoron duka a rayuwarta. Koda wani taga ana duka firgicewa take. Ballema har abada bazata taɓa iya

manta dukan dayay musu ba ita da Aysha. Da sauri ta juyo jin motsin buɗe ƙofa. Sukaima juna kallon cikin ido ita da shi, ita ta fara janye nata tana sauke ajiyar zuciya dajin shakkar
kallon fuskarsa dake a matuƙar tsuke. “Ki tashi kiyi salla”.
Ya faɗa a taƙaice da juyawa zai fita. Harya kama handle ɗin ƙofar zai fita ya tsaya cak, juyowa yay a hankali yana kallonta saboda ganin yanayinta. Sai dai baice komaiba ya juya ya fita. Numfashi ta saki a hankali da miƙewa ta shiga toilet domin ɗauro alwala.
Bai dawo gidan ba sai bayan sallar isha’i, kai tsaye kuma sashenta ya zarto. Tunda ta idar da salla ta kasa tashi a wajen, babu abinda ke mata kaikawo, haka kawai marin nan na ɗazun da yay ma Fadwa ya matuƙar tsaya mata a rai, duk da kuwa ƙararsa kawai taji bawai yinsa akan idonta ba. Harya ƙaraso gabanta bata san da shigowarsa ba, ya kai tsugunne gabanta, tare da ɗago haɓarta. Cikin idanunsa ta zuba raunannun nata da babu gilashi, bata ganinsa fes yanda ya kamata, amma hakan bai hanata tsaidasu a
tsakkiyar nasan ba… “Mike damunki?”.
Ƙoƙarin janye idanunta tai a cikin nasa ya hana hakan, taso kauda kanta gefe nanma ya

hana, saita ƙara tsuƙe fuska da tura baki. A karon farko ya saki murmushi, tare da kai yatsansa ya ɗalli lips ɗin nata. “K wai baki san shekarunki sun girmi wannan taɓaran ba Autar mata?”.
Hanunsa ta ture zata tashi, yay saurin
damƙota yana dariya, jikinsa ta faɗa, dan
haka suka zube ƙasa gaba ɗayansu. Ƙafarsa
ɗaya ya kwanta, tare da jawota ya kwantar a
cinyarsa ita kuma. Ya tokarar da ɗayar ta
jingina kanta. “Nayi laifi ne wai?”.
Hanunsa dake kan cikinta ta kamo, ta saka
babban ɗan yatsan a bakinta ta ciza. “Wai wai
shiii! Wace mugunta ce muka wannan?”.
Dariya ta ƙyalƙyale da shi. “Noorie muguntafa
babu ƙyau sam sam”. Ka ɗan ta murguɗa
masa baki “Punishment ɗin mai yawo ne ai”. “Shi kuma punishment ɗin mai rashin kunya
fa? yaya ya kamata ya kasance?”. “Sai an binciko a littafin shara’a”.
Ta faɗa tana ƙoƙarin mikewa ta gudu. Riƙota yay yana ƙaramar dariya. “Sarkin wayo ai ni tuni na binciko. Yanzu kuma zan ƙaddamar da shi”.
“Wayyo yaya! Wayyo ni yunwafa nakeji, tun safe banci komai ba.”
“Nima ita nakeji ai”. Ya ƙare maganar da manne lips ɗinsu waje guda. Ko sau ɗaya batai ƙoƙarin hanashi ba, saima gudunmawa

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button