BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

★★★
A sashen Mommy Fadwa sai sake langaɓewa take ganin yanda Mommy da Mamah suka rikice. Dan itama Mamah (Gwaggo Haliman) tazo wajen saka ranar ta Maheer. A haka ya shigo ya samesu zagaye da ita. Sai kawai ta fashe masa da kuka tana miƙa masa hannu wai itafa yazo zata mutu. Cijewa yay yayi kamar baiga hanun da take miƙo masa ba, koba komai ai sa raga dan iyayensu. Sannu yay mata tare da zama yana gaida Mahmah. Cikin kulawa ta amsa masa itama. “Dama bata da lafiya ne haka Babana?”.
Ɗan duban Fadwan yayi ya janye idanunsa. “No Mamah bawai tana kwance bane, kawai dai idan taji ƙamshin abinda bata so ne take amai, amma baima taɓa kaiwa kamar na yau ba”.
Kallon juna Mamah da Mommy sukai, kowanne zuciya cike da son ƙarin bayani, sai dai sun san ba lallai su samu daga Shareff ɗin ba bara kawai su jira zuwan Jamal. Babu ko wani jimawa Jamal ya iso, Shareff ɗinne ya fita ya shigo da shi. Bayan ya gaishesu ya ɗan yima Fadwa tambayoyi tana amsa masa da ƙyar. Da ga ƙarshe ya bata tsinken gwaji.
“Inaga yi amfani da wannan mugani ko abinda nake zargi ne. In ba shi din bane sai na ɗeba jininki”.
Mommy ce ta amsa, ta kamata suka shiga toilet ɗin nan cikin falo. Bayan wasu mintuna suka kawo masa tsinken kamar yanda ya bukata. Murmushi ya saki yana mai kallon Shareff cikin ido, ya ɗauke kansa da maidawa gasu Mommy. “To inaga ma basai ta kaimu da gwajin jininba a yanzu-yanzun, dan abinda nake zarginne dai. Ko zuwa monday zata iya zuwa asibiti ta sameni ALLAH ya inganta ya ƙara lafiya. Bara na bata wannan maganin zai sa ta ɗan samu nutsuwa daga galabaitar da tai nayin aman”.
Sosai bakunan su Mommy yake a washe, yayinda su Hassan suka cika falon da ihun murna suna faman rungume Fadwa. Shi dai uban gayyar tuni sun fice shi da Dr Jamal, sai dai har cikin ransa yaji daɗi duk da ya jima da zargin hakan a ransa. Dr Jamal ya sake masa Congrat, cikin tsokana yana faɗin, “Lallai abokina ka zama namijin duniya, irin wannan bugu na daga kai sai mai tsaron gida haka. ALLAH ya inganta mana”.
“Ɗan iska kaji da shi dai. Yanzu ina ka nufa?”.
“Gida ya kamata na koma, amma tunda ka kawoni nan nima bara naima tawa flower ɗin barruwa”. Ya ƙare maganar yana laluben number Anam. Sarai Shareff ya fahimcesa, dan haka baice komaiba sai ma basar da zance yay kamar baiji ba. Kusan sau uku yana kira ba response, ya ɗan ɗage kafaɗa yana duban Shareff. “Musty inaga yarinyar nan bata kusa da wayar. Bara kawai na wuce na dawo taɗin dare. Yaushe ne tafiyar taka jibin?”.
“Zan wuce da safe ne dan zan fara shiga Abuja, da ga can zan wuce”.
“Okay to da yamma zan shigo gida insha ALLAH”.
Sallama sukai ya wuce, shi kuma ya koma wajen su Mommy da suka dasa sabuwar tarairaya ga Fadwa.
Dawowar ƴan kai kaya da saka rana ta sake baje labarin cikin Fadwa a gidan. Kowa sai sambarka da fatan saukarta lafiya yake. Gwaggo harda ƴar rawarta. Shi dai Shareff tuni yama bar musu gidan, sai yamma ya dawo suka fita salla da su Daddy. Bayan sun dawo ma tare da su yaci abinci. Ya ƙara tattauna batun tafiyarsa da su, daga karshe suka sakko masa zancen matarsa fa? Nan zata dawo da zama ko gidansu tunda dama ba daɗin jikinta take ji ba dan suma labarin ciki har yazo musu.
Ajiyar zuciya ya ɗan sauke. Kansa a rissine yace, “Da dai tayi zamanta kawai acan ɗin, nayi magana da Khaleel zai koma kwana acan, Aysha da Anam sai suje suma su tayata zama tunda bawani abu suke anan ɗin ba”.
Abba dake murmushi yace, “Hakan ma yayi to. ALLAH ya baka sa’ar abinda zakaje dominsa. Ya kuma dawo mana da kai lafiya”.
Da amin suka amsa shi da Daddy. Daga haka suka cigaba da tattauna wasu batutuwan daya shafesu da kuma tafiyar tasa.
★★★
Anam bata san mike faruwa akan komawarsu gidan Yaya Shariff ba sai washe gari, dan bata wani bama maganarsa ta jiya muhimmanci ba. Koda taji batun cikin Fadwa kuma batace komai ba. Tadai saka albarka a sa ranar Maheer da akace wata huɗu.
Da yamma ta dawo aiki Mom ke sanar mata ta haɗa kayanta ita da Aysha zasu je su taya matar Shareff zama kafin ya dawo. Cikin waro idanu da mamaki take duban Mom. “Mom ni kuma? Kin san fa yanda matar nan tabi ta tsaneni ga Gwaggo da Mommy da Mamah a gefe…”
“Anam duk na kawoma Abbanku irin wannan misalin, amma ya nuna min sun riga sun gama yanke hukunci. Kinga sai kibi umarninsu kawai ALLAH ya kaɗe fitina”..iyayenmu????????????ZAFAFA BIYAR
INAYAH
MamuhGee
GURBIN IDO
Safiya Huguma
SANADIN LABARINA
Hafsat Rano
FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)
BABU SO
Billyn Abdul
Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k
YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107
ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: Typing????
*_❤????BABU SO....!!❤????_*
_(Miya kawo kishi?)_
*_Bilyn Abdull ce????????_*
BABU SO????????AREWABOOKS
21
……Sosai Anam taji kamar ta fashe da kuka. Sai dai bata iya jayayya ba. Dan haka tabi umarnin Mom bayan tayi wanka taci abinta ta haɗa kayan da basu wuci kala bakwai ba, sai abinda ba’a rasa ba. Dan tanajin da wahala zamanta yay nisa a gidan basu kwashi ƴan kallo da Fadwa ba. Aysha ce ta shogo, ganin ƴan kayan data haɗa tace bata isaba. Canja jakkan kayan tai zuwa babban akwatinta, ta dinga ɗibo kaya a wadrobe tana zubawa, duk da dakatar da ita da Anam keyi taƙi saurarenta, dan harda kayan da aka ɗinka mata da ko sakasu ta kasa farayi har yanzun. Aysha da taƙi saurarenta taja a kwatin tana faɗin, “Yaya har yazo, kiyi maza ki kammala kin san sa da azalzala”.
Harara ta wulla mata batare data amsaba. Aysha ta fice tana dariya. Dole itama ta miƙe ta karasa kimtsa abinda ya rage mata. Sannan ta fito yima Mom sallama.
A can ɓangaren Mommy sai yanzu tasan harda Anam za’a zauna gidan Shareff. Ranta ya ɓaci, dan haka kai tsaye tace bata aminceba in har itace ta haifi Shareff. Shi dai baice komai ba, sai Daddy ne yace bata isaba, idan kuma tai wasa zai matuƙar ɓata mata rai ne. Ganin sunata cacar baki Aysha taje ta sanarma Gwaggo duk da tasan itama ɗin dai sai a hankali ce. Dandanan ko sai gata tazo, da yake Aysha ta faɗa mata abinda ke faruwa koda tazo sai ta goyi bayan Daddy akan tabar Shareff ɗin ya wuce dasu Aysha dare nayi, ai zaman Anam ɗin acan ba komai bane. Rai ɓace kuma cikin mamaki Mommy take duban Gwaggo. Gwaggo ta kyafta mata ido alamar kartaji komai ta sallama. Shiru tayi kawai amma har sannan ranta na mata suya, sai dai tama ƙagara su tafin taji dalilin Gwaggon nayin haka.
“Kai tashi ka ɗaukesu ku wuce dare nayi”. Daddy ya faɗa yana duban Yaya Shareff da kamar bashi a falon. Mikewa yay kuwa yay musu sallama. Aysha tabi bayansa suka fice. Bai shiga kowane sashe ba, dan zai dawo da safe musu sallama kafin ya fice tunda bada sassafe zai wuce ba Khaleel ne ma zai kaishi airport. Suma su Ayshan dan yana son suje tun a yau ne ya haɗasu da Fadwa yay musu gargaɗi tunda yasan da gaske za’a dinga samun saɓani ne tsakanin Anam da Fadwa. Aysha ce ta shiga ta kirawota.
Doguwar riga ce jikinta mara nauyi, sai ƙaramin veil data yana a kanta. Tana riƙe da ƙaramar jakar data haɗa kayanta na ciki da Aysha bata kwaso ba saboda sauri. Ta gaida sa batare data kallesa ba. Ɗauke kansa yay yana amsa mata, tare da buɗe motar ya shiga. Aysha tai wuff ta shige baya, zata shiga itama ya hararesu. “Dalla malamai ni drivern ku ne?!”.
Aysha ta tura Anam dake ƙoƙarin shigowa. “Blood kefa na barma can ki shiga”. Baki ta buɗe zatai magana ya juyo a fusace. “Bana son shashanci fa, kuna ɓatamin lokaci”. Hararar Aysha dake mata gwalo tayi, batare da tace komai ba ta zagaya ta shiga gaban ta zauna. Motar yayma key ya fice bayan sunyi sallama da maigadi.
A hankali yake driving ɗin kamar baya so, motar shiru babu mai ko motsin kirki. Dan ita Anam ma har ta fara gyangyaɗi kasancewarta mai barcin wuri musamman idan waje da sanyi. Yanzu kam sanyin acn ke ɗibarta dama ga gajiyar aiki. Karatun alkur’ani ya kunna har suka iso, gidan shiru kamar babu kowa, sai maigadi dake sauraren taskar labarai a redio. Yayma uban gidansa sannu da zuwa bayan ya buɗe masa gate.
Shi da kansa ya fiddo musu akwatinsansu a booth, Aysha taja ɗaya tana turama Anam ɗaya. Hamma tayi cikin ɗan layin barci ta jingina da motar tana dafe akwatin. Ita da akwatin yayma kallo ɗaya ya ɗauke kai, batare da yace komai ba ya sama motar lock da key ya ja akwatin yay gaba. Baki taɗan tunzura sannan tabi bayansu cikin ɗan layin barcinta.
Basu sami kowa a falon ba, hatta da tv a kashe take, Aysha ta kallesa cikin zumuɗi tana faɗin, “Yaya Aunty Fadwa fa?”.
Gitta ta yay kamar bazai amsa ba, sai da ya kai akwatin ƙofar ɗakin da zasu zauna ya juyo. “Maybe ta kwanta, na barta kanta na ciwo”.
“Ayya ALLAH ya bata lafiya”.
Amin ya faɗa kan laɓɓa idanunsa akan Anam data zauna a hannun kujera ta kwantar da kanta dan da gaske barcin takeji. “Ki tadata kuje ku kwanta kuma kawai”.
“Okay Yaya sai da safe”.