BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

   Kasancewar tayi wankanta tayi salla tun a gida suna shiga ɗakin ta faɗa kan gado tai kwanciyarta, addu’a ma sai Aysha ce ta mata tana mintsininta cikin tsokana da kiranta kasa anji sanyin ac. Hannunta ta buge, ta juya taci gaba da barcinta.

____

       “Gwaggo nifa wlhy duk kin sani a duhu. Ko kin mance wai yarinyar nan ce dana tsana ita da iyayenta fiye da komai a rayuwata”.
     Murmushi Gwaggo tai irin na makircinsu na tsoffin hannu. Ta dafa kafaɗar Mommy. “Daɗina dake gaggawa. Kema kin san bazan amince da zamanta can ba in babu wani abu a ƙasa. Dan haka kwantar min da hankalinki da safe zakiji komai…”
     “Miyasa ba yanzuba Gwaggo?”.
“Saboda idon mijinki yanzu akanmmu yake.” Kai kawai ta jinjina badan taji sauƙi a ranta ba. Gwaggo tai mata sai da safe ta fice tana murmushin da sam Mommy ta kasa fassarashi a kowane mizani….

      WASHE GARI

Shine ya musu knocking ƙofa da zai wuce massallaci da asuba, sai da ya tabbatar sun tashi sannan ya fice. Ana idarwa gida ya dawo, azkar ma sai da ya zo yayita a gida bayan ya sake tada Fadwa dake barci duk da ya tadata kafin ya fita amma bayan fitarsa ta koma ta kwanta. Tana mitar ita har yanzu kanta ke ciwo ta nufi bayi tayo alwala. Bai tanka mata ba harta zo ta kabbara salla. Bayan ta idar ta tashi ta koma gadon, a jikinsa ta lafe tare da sumbatar laɓɓansa. “Good Morning my Soulmate”.
“Good morning wife ykk ya baby?”.
Murmushi tai da kamo hanunsa ta ɗaura kan cikinta, murya cike da shagwaɓa tace, “Gashi har ya fara kewar Daddynsa”. Murmushi ya saki a karon farko, ya sumbaci laɓɓanta shima. Cikin ɗage mata gira ɗaya yace, “Nima cike nake da kewarsa shi da mamansa. Amma karya damu bazan jima ba zan dawo garesa insha ALLAH”. Rungumesa tai sosai, tare da fara bashi wasu zafafan salon da ya sashi biye mata. Bayan komai ya lafa tana kwance a jikinsa idanunsa a lumshe ya kirayi sunanta.
“Uhhyim”.
Ta amsa tana ƙara ƙanƙamesa. Cigaba yay da shafa kanta har yanzu idanunsa a rufe. “Jiya nazo da su Aysha da zasu tayaki zama. Koda wasa bana son jin wata fitina. Ki riƙe girmanki da mutuncinki. Idan naji wata fitina kezan fara hukuntawa matsayinki na babba”.
“Insha ALLAH babu abinda zai faru, Ayshan ita da Hussaina ne?”.
Kansa tsaye yace, “Da Anam”.
Baima gama rufe baki ba ta miƙe zumbur zaune. Shima sai ya buɗe idanu yana kallonta. Kai take girgiza masa hawaye na ciko mata ido… “Ni gaskiya bazata zaunamin gidaba, taje kawai Aysha ta isa”. Idanunsa ya kauda yana tashi zaune ya jingina da fuskar gadon. “Karki ɓatama kanki rai a banza. Juwairiyya da Aysha zasu zauna tare dake, shima Khaleel anan zai dinga kwana….”
“Bazai yuwu ba”.
“Sai ki hanasa yuwuwar mu gani tunda gidanki ne”. Ya faɗa a fusace yana sauka a gadon. Da sauri ta yayibi bedsheet ta sakko tana ƙudindine jikinta a ciki tasha gabansa. “Dan ALLAH ka tsaya muyi magana. Wlhy iya gaskiyata nake gayama na tsani yarinyar nan bazan iya zama inuwa ɗaya da ita ba har abadan dan zan iya halaka ta”. Sosai yake kallonta cikin tsakkiyar ido. Ya riƙe ƙugu da dukkan hannayensa yana ƙoƙarin danne fushinsa. “Zaki iya halaka ta? To sai dai in ki halakata ɗin, dan babu fashi zata zauna anan tunda ba dake na haɗa kuɗin na gina gidana ba. Ki bari mu rabu lafiya Fadwa!!..” Ya ƙare maganar cikin tsananin zafin rai ya ɗan banjajeta ya ficewarsa.
Zubewa tai a wajen ta fashe da kuka. Itakam ta shiga uku wannan shegiyar yarinya ta zamewa rayuwarta jaraba. Wayarta ta ɗauka tai kiran Mahmah, sai dai kuma a kashe, Mommy ta kira, bugu ɗaya ta ɗauka. Ko sallama babu balle gaisuwa ta fashe mata da kuka tana faɗa mata ita dai inhar da Anam zata zauna to sai dai ta koma gidan su. Sai da ta gama surutanta sannan Mommy tai magana..
“Fadwa na fiki shiga ɓacin rai da zaman wannan yarinyar anan gidan, dan a daren jiya banyi barcin kirki ba saboda baƙin ciki. Amma ina son ki kwantar da hankalinki Gwaggo tace tanada plan akan zaman nata….”
“Mommy Shi plan ɗin baza’a iya aiwatar da shi tana nan ba dole sai ta raɓu da gidana?”.
“Nima na faɗa miki ba son hakan nake ba. Amma mu saurari mi Gwaggon zatace zuwa anjima. Yanzu dai ki daure ranki ku rabu lafiya da mijinki bayan ya tafi anjima kaɗan zan zo gidan ai”.
“Mommy….!”
“Kiyi yanda nace”.
Mommy ta tari numfashinta a fusace tana yanke wayar, dan ƙara hasalata Fadwan take ma……….✍

ZAFAFA BIYAR

INAYAH
MamuhGee

GURBIN IDO
Safiya Huguma

SANADIN LABARINA
Hafsat Rano

FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)

BABU SO
Billyn Abdul

Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: Typing????

  *_❤‍????BABU SO....!!❤‍????_*
             _(Miya kawo kishi?)_



          *_Bilyn Abdull ce????????_*

BABU SO????????AREWABOOKS

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

22

………Kiran Gwaggo ne ya shigo tamkar tasan mike faruwa. Kamar bazata ɗagaba sai kuma ta ɗaga. Tai shiru taƙi magana. Ban san mi Gwaggon tace daga canba ta tunzura baki da faɗin, “Naji ina kwana”. Amsawa Gwaggo tai daga can sannan ta shiga gaya mata abinda yasa ta kirata. Ajiyar zuciya Fadwa ta saukea hankali da fara share hawayenta. Kamar tana a gaban Gwaggo ta jinjina kanta da yin ɗan murmushi tana mikewa bayan ta yanke wayar. A gurguje ta faɗa banɗaki tayo wanka, ko busar da kan batai zaman yi ba ta saka hula da doguwar riga ta fice. Kitchen ta shiga, ta dafa shayi da soya kwai ta haɗa kayan a tray. Sashesa ta nufa, dan dama jiya ya kwana a sashenta ne saboda ta ya buƙaci hakan. Babu kowa a falon, ta ajiye tray ɗin a centre table ta nufi bedroom ɗinsa. Shigowarta dai-dai da fitowarsa wanka. Yay mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa. Zuwa tai ta rungumesa tana kwantar da kanta a gadon bayansa. “Kayi haƙuri mijina na tuba, na fahimci nayi kuskure bazan sake ba”.
        Shiru kamar bazaice komai ba, dan yasan wannan ba kalaman Fadwa bane wanine ya bata su akan harshe. Sai dai kuma shi ba mutum bane mai son zurfafa zargi, dan haka ya kamo hanunta ya zagayo da ita gabansa. Idanu suka ƙurama juna, sai faman sakar masa murmushi take, shiko tasa fuskar kadaran kadahan. “Nace fa kayi haƙuri”. Ta faɗa cike da shagwaɓa tana girgiza masa hannu. Cikin ɗan turo numfashi waje yace, “Okay fine ya wuce”. Rungumesa tai, kafin taja hanunsa zuwa gaban mirror. Da kanta ta shafa masa man a jiki tana masa duk wani salon kwarkwasa dazai sashi cire komai a rai kamar yanda Gwaggo tai mata huɗuba. Ta ɗan samu ya biye mata badan komai ba sai dan yana son su rabu lafiya. Yayi ƙyau cikin kananun kaya ga ƙamshi data feshesa da shi na tashi suka fito falo. Zama yay idonsa akan breakfast ɗin data ajiye….
      “Inaga ki kirasu mu karya gaba ɗaya, dan ina son nayi magana da ku”. Kamar zatai gardama sai kuma ta haɗiye, cikin taushin murya tace, “Amma ƙwan iya naka na soya anan fa”.
       Yanda ta amsa ɗin shima ya sashi tausasa nasa harshen dan yana son su rabu lafiya. “Kiyi haƙuri ki soya musu suma, dan yau tamkar baƙi suke anan”. Maganar Gwaggo tasata amsawa, sai kuma sanin halinsa. Juyawa tai ta fita a sashen gaba ɗaya, ya bita da kallo harta fice. Mintunan da basu gaza goma sha biyar ba ta kammala soya ƙwan ta leƙa ta kirasu batare data yarda tako dubi sashen da Anam take ba. Itama dai Anam ɗin bata ko kalleta ba sai Aysha ce ta gaidata da tasowa ta rungumeta. Anam ta taɓe baki da sake juyar da kai tamkar bata gansu ba.
         Su suka fara shiga falon ita kuma tana biye da su a baya. Yana zaune a inda ta barsa, sai dai yanzu waya ce a hanunsa. Koda ya amsa musu sallama kuma bai ɗago ba.
     “A haɗa a dining ne?”. Ta faɗa tana kallonsa. Ɗan ɗagowa yay ya kalleta ya maida kansa, “No barsa mu zauna nan zaifi balance”. Kai ta jinjina masa. Aysha da Anam suka shiga gaishesa. Ya amsa musu da ɗan sauƙaƙa murya batare daya dubi kowacce a cikinsu ba. Saboda kar Anam ta zauna a kusa da shi Fadwa tai saurin jan hanun Aysha ta zaunar, sai ya zam sun sakashi a tsakkiya, ita kuma inda Anam take zaune sai yazam sunyi facing juna ita da shi. Haka kawai taji abun ya bata dariya, dan tana lura da sanda Fadwa taja hanun Ayshan. A zuciyarta tai dariya, a zahiri kam babu ɗigon fara’a a fuskar tata.
      Aysha ta haɗa mata shayin da ajiye mata gabanta dan taƙi taɓa komai, a hankali tace mata ‘thanks’. Ba wani iya cin komai tai sosai ba har yanzun, dan haka koda Aysha tace a saka mata ƙwai kanta ta girgiza mata da nuna mata bread ya isa. Ɗagowa yay suka haɗa ido, lokaci ɗaya tsigar jikinta ta tashi. A hankali ta janye idanunta daga cikin nasa, shima nasan ya janye batare da yace komai ba. Fadwa kam bama ta nuna tajisu ba, sai Aysha ce tace “K kullum a baki iya cin abu ba bazaki koyama kanki ba?”. cikin yin ƙasa da murya tace, “Ni bana sonsa ne fa”.
       “To k dama indai abinci ne ai komai bakya so”.
   Hararar Ayshan tayi, batare da ta sake cewa komai ba ta cigaba da juya cokali a shayin tana tsakurar bread ɗin. Ɗagowa kam bata sake yarda tayi ba balle ta haɗa ido da shi har suka kammala. Ita da Aysha suka tattare wajen, suka kwashi kwanikan zuwa sashinta. Kasancewar yace su aje su dawo basu ɓata lokaci ba suka koma. Fadwa suka samu zaune a jikinsa, shigowarsu kuma bai sa ta jaye ba, sai shine yay mata nunin ta zauna da ƙyau da ido. Ganin yanda fuskarsa take babu wasa yasa ta matsawa sai dai ranta bai so haka ba. Oho wadda take dan itan ma bata san tanai ba, dan koda suka shigo Anam bata yarda ta kalli ko sashen da suke ba. A ƙasa suka zauna, ya fara addu’ar da MANZON ALLAH yace muyi a duk sanda muka samu kammu a irin makamancin zama haka kafin ya ɗaura da nasiha a garesu, da ga ƙarshe ya ƙare da gargaɗi mai cike da kurarin tabbatar musu in har yaji wani abun ɓacin rai daga garesu su duka ransu sai ya ɓaci, kowacce ta kama kanta, su su girmama matarsa a matsayinta na Yaya a garesu kuma matarsa, itama ta riƙesu a matsayinsu na ƙannenta kuma ƴan uwansa. Daga ƙarshe ya rufe da jawabin zaman Khaleel a gidan, sai dai shi kwana kawai zai ringa zuwa yayi sai kuma cefane da duk wasu buƙatun gidan su nemesa. Daga haka ya sake rufe taron da addu’a yana miƙama Anam kuɗi, kamar tace a’a amma sai ta amsa tayi godiya, itama Aysha kamar na Anam ɗin ya bata. Cike da zumuɗi ta amshe abinta tai godiya, daga nan ya sallamesu.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button