BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

        ★Yini guda ƴan dubiya nata leƙowa jefi-jefi, sai dai babu Gwaggo babu Mummy, Aysha ma satar hanya tai ta biyo su Mom da zasu zo tazo ta duba Anam ɗin. Dan Mommy ta hana yaran ɗakinta duka. Shareff dai bai sake leƙowa ba sai kusan takwas na dare, da alama daya tashi aiki sai da yaje gida sannan ya dawo nan dan jallabiya ce a jikinsa. Yanzu ma Anaam yitai kamar bata san ALLAH yayi ruwansa ba, shima kuma daga gaisuwa da yay da Aunty Mimi da wata ƴar uwar Mamie data zo duba Anaam ɗin yaja bakinsa ya tsuƙe. Aumty Mimi suka fita zataima baƙuwar rakkiya aka barsu su biyu. Shiru ɗakin ya ɗauka kamar babu masu rai, sai ƙarar iskar fanka kawai kakeji, taƙi yarda ko sau ɗaya ta kallesa sai faman cin apple ɗinta take da aunty mimi ta yanka mata hankali kwance. Idanu ya ɗan tsura mata amma duk da haka ta ƙi ta nuna tasan da zamansa….
      “A tunaninki wannan rashin kunyar taki zaisa ki samu biyan buƙatar taki?”.
    Shiru babu alamar tama jisa tanata dai cin apple ɗinta, ransa ya ƙara ɓaci, cikin jin zafi da ɗacin da muryarsa ta kasa ɓoyewa yace, “Oh ga mahaukaci na magana ko? K! Ki shiga hankalinki wlhy, inba hakaba zakisha baƙar wahala a banza stupid kawai”.
        Babu ko ɗar a cikin idanunta ta ɗago ta zuba masa su duk da suna cikin gilashi, “Yaya Shareff ALLAH bazai baka damar bani wahalar ba kuwa, dan hanyar jirgi daban ta mota daban. Aure ne dai nace bana so kuma komi za’amun bazan so ba dan inada wanda nake s……”
    Ji kake “bumm!” akan bakinta, sam batama lura da sanda har ya taso ya iso gareta ba. Ya ture hanunta da take ƙoƙarin ɗaurawa saman lips ɗinta ya maye gurbinsa da nasa yatsun biyu, cike da baƙar mugunta ya shiga murzasu. Duk da dukan da take kaima hanun nasa bai janye ba sai da ya tabbatar ya murjesu san ransa sannan ya saki. “Karki fasa rashin kunya, nima bazan fasa ɗaukar mataki akanki ba”. Ya ƙare maganar gab da fuskarta har yana busa mata numfashinsa da iskar bakinsa dake ƙamshin mouth freshener na banana.
      Kuka ke son taho mata amma tanata ƙoƙarin dannesa dan taci alwashin bazata sake barin hawaye akan fuskartaba game da wannan auren, zata ƙwaci kanta da ƙarfinta kuma duk abinda za’ai mata sai dai ai mata bazata zauna zaman aure da shi ba. Shima baibi takanta ba dan harya fice ma abinsa rai ɓace. Taja wani shegen tsaki da ɗaga gilashinta ta share ƙwallar da suka taru a fatar idon dan ta danne sauran ta hanasu tasiri. Koda aunty Mimi ta dawo bata tambayeta ina Shareff ɗin ba, da alama dai sun haɗu a waje ne.
      Daga ita har shi haka suka kwana rai a ɓace. Washe gari ma shine ya fara zuwa asibitin, sai da yaje wajen doctor ya biya komai ya basu sallana sannan ya iso ɗakin. Da aunty Mimi kawai yau ma ya gaisa, ƴar darun tasa na kwance ta juyama ƙofa baya baima san idonta biyu ko barci take ba. Shine ya sanar ma aunty Mimi an sallamesu, tai godiya ga ALLAH sannan ta miƙe ta fara haɗa kayansu. Ya ɗauki kayan ya fita da su, ita kuma ta tada Anaam da dama idonta biyu ta taimaka mata ta shirya sannan suka fito bayan doctor ya shigo sunyi sallama. Tsaye suka samesa a jikin motarsa yana waya da alama a cikin su Daddy ne. Ƙin yarda tai ta kallesa duk da shi tana jin nasa idon a kanta. Aunty mimi zata sakata gaba ta tirje akan ita dai baya take so, kokuma subi napep.
       Faɗa aunty Mimi ta fara mata dan ta kaita wuya kuma, shiko kamarma bai san sunai ba ya shige motar abinsa bayan ya gama wayar tasa. Dole dai ta shiga gaban bisa tursasawar aunty Mimi……..✍????

ZAFAFA BIYAR

INAYAH
MamuhGee

GURBIN IDO
Safiya Huguma

SANADIN LABARINA
Hafsat Rano

FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)

BABU SO
Billyn Abdul

Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107

ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: Typing????

  *_❤‍????BABU SO....!!❤‍????_*
             _(Miya kawo kishi?)_



          *_Bilyn Abdull ce????????_*

BABU SO????????AREWABOOKS

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

35

ASSALAM ALAIKUM DEARIES … BARKAN KU DA KOKARI .. KAMAR KODA YAUSHE. WANNAN KARON MA MUNA BARAR ROKON KU WAJEN TEMAKAWA CHANNEL DIN SUDEIS DAKE MANHAJAR YOUTUBE

YARO NE DAYA TASHI DA SON KARATUN ALQURANI ME GIRMA. YA KE KUMA KWADAYIN GADON ME SUNAN SA SHEIKH SUDEIS. DAN ALLAH A TEMAKA A DANNA MASA SUBSCRIBE. A KUMA YI VIEWING DA LIKING. A TEMAKA DA SHARING MA… JAZAKUM ALLAH KHAIRAN AS YOU DO…????

Assalamualaikum dear sisters and brothers.

Welcome to ummu sudais YouTube channel????
A channel where the Holy Quran is been recited from different Angles.
Click on this link and listen to the Beautiful recitation that will melt your heart
https://youtu.be/Lafgc749sK8

Your subscription to our channel is of Great important. Please help us grow our channel by subscribing and liking our videos fisabilillah.
Thank you so much


……….Cak numfashin Fadwa ya ɗauke daga ƙirjinta, idanunta suka fara ganin duhu-duhu, tai baya luuu zata faɗi dan wani irin mugun hajijiyace ta lulluɓe ganinta da jinta saboda maganar tazo mata ne tamkar saukar nokiliya…. Laɓɓanta matuƙar rawa suke na alamar sonyin magana, amma bushewar yawun dake taimakawa maƙoshinta ya hanata damar hakan. Sai faman raba idanu take a tsakanin Mommy dake tsaye tamkar bajimar zakanya taga abin farautarta da Shareff da alamu suka nuna shima yayi ƙamewar wucin gadi ne saboda wani dalili na mamakin furicin Mommy ɗin ko wani abu daban da bata hasaso ba…..
     Shigowar Daddy ɗakin tamkar an jehosa ta maido Shareff a tashi sumar tsaywar jinin data riskesa tabbacin hasashen Fadwa, dan shima dai jinsa da ganinsa a take suka rabu da gangar jikinsa baki ɗaya, sai idanunsa ne kawai tsaye ƙyam akan Mommy na tabbacin bashi da maraba da sumamme.
        “Bazan hanashi bin umarninki ba, sai dai nima a nawa umarnin, wlhy! Wlhy! Wlhy!! Idan har Al-Mustapha ka saki Mamana! Nima zan saki uwarka dai dai da adadin sakin da ta sakaka ka rubuta!!…….”
    “Dana haɗa jini da Usman da Ai’sha gara na barka har abadan abidina Muhammad!!”. Mommy ta tari numfashin Daddy a tsawace.
“Okay fine! Haka kikace ko?. Kai Al-Musta……….” Shigowar Abba da Dr Jamal ta hana Daddy ƙarasa faɗar abinda ke bakinsa, sai dai wani irin mugun kallo da yake bin Mommy da shi, har cikin ranta yake ratsata, sai dai zuciyarta tayi bushewar da take jin zata iya ɗaukar koma minene daga garesa akan wannan auren da rabashi shine kawai samun nutsuwar ruhi a gareta. Gwaggo ta riƙo hanunta tana faɗin, “Altine kina lafiya kuwa? Kai Muhammadu karka sake cewa komai kumuje gida”.
       Mommy ta fusge hanunta daga riƙon da Gwaggo taimata. “Wlhy Gwaggo babu inda zanje sai Al-Mustapha ya saki yarinyar nan, dan bana buƙatar auren nan ya sake minti guda a kansa!!”.
        Dr Jamal da gaba ɗaya ya rikice cikin roƙo yace, “Dan ALLAH Mommy kiyi haƙuri, bara na basa sallamar sai aje gida wannan maganar bata nan bace ba”. Kafin tace wani abu Gwaggo taja hanunta suka fice, ganin shima Daddy ya fita ya sata yarda ta bita. Abbah ya kama Shareff shi da Doctor Jamal. Wata Nurse kuma ta kama Fadwa da har yanzu babu alamar ta dawo hayyacinta…….

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button