BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAFAFA BIYAR
INAYAH
MamuhGee
GURBIN IDO
Safiya Huguma
SANADIN LABARINA
Hafsat Rano
FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)
BABU SO
Billyn Abdul
Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k
YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107
ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: Typing????
*_❤????BABU SO....!!❤????_*
_(Miya kawo kishi?)_
*_Bilyn Abdull ce????????_*
BABU SO????????AREWABOOKS
56
………Bai shigo ba sai da aka idar da sallar isha’i. Ya kwashi ledojin daya bari a mota. Na Fadwa ya fara ɗauka ya nufi sashenta. A falo ya sameta zaune cikin kwalliya da waya a hannu. Ga tv a kunne tana faman aiki. Yana mamakin yanda a koda yaushe waya bata barin hanunta, tun baya maida hankali akan hakan har ya fara sosa ransa, sai dai bazaiyi maganaba a yanzu sai anzo gaɓar data dace.
Fuskarta ƙawace da murmushi ta taso garesa. Rungumesa tai da manna masa kiss a kuncinsa na dama. Ya sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi dan babu abinda yafi buƙata kamar ɗumin matarsa a yanzu. Ya sani ba ƙaramar jarumta yayi ba, dan rabonsa da Fadwa kusan sati uku kenan cikin na huɗu. Hanunta saƙale a wuyansa fuskarsu gab da juna. Bakinsu take son haɗewa amma ya kauda kai kaɗan dan ya tabbata ya biye mata bazai iya ƙyaleta ba kuma hakan ba daidai bane ba tunda akwai haƙƙin wata a kansa bayan ita ɗin.
Cikin son basar da ita ya janye hanunta dake saƙale a wuyansa yana faɗin, “Ki shirya abincin”. Jiki a sanyaye ta gyaɗa masa kai, harya nufi ƙofa ta kasa haƙuri. “Har yanzu baka huceba ko? Kana ganin laifi na!”.
Tsayawa yay, sai da takai aya ya waiwayo yana kallonta. Tai ƙasa da kanta zuciyarta na sake raunana dan da gaske abin ya dameta. Shima ɗin ta bashi tausayi, dan shi shaida ne Fadwa nada tsoro da tsananin gudun ɓacin ransa, wannan halin nata na ɗaya daga cikin abinda ya saka masa sonta. “Zan iya miki uziri ana yau, amma ki kiyaye dan anan gaba makamancin haka ta sake faruwa ni kaina ban san irin matakin dazan iya ɗauka ba har asu kansu, dan bazan ɗauka wulaƙanta matata da hanani zaman lafiya ba a gidana”.
Bai jira cewartaba ya fice. Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi, zuciyarta na rage cinkushewar da tai……
Idar da sallarta kenan takai bakin gado, muryar Mamie take son ji duk da sun gaisa ɗazun da safe. Maimakon normal kira saita ji sha’awar kiranta video call. Tana ƙoƙarin yin hakan da ɓare lollipop sweet takai baki ya shigo ɗakin. Ɗagowa tai suka haɗa ido, tai saurin janye nata dan wani irin matsanancin kunyarsa ta tsinci kanta a ciki saboda abinda ya faru ɗazun da shi ta yini cikin rai. Inda taken ya ƙaraso ya zauna kusa da ita gab. Batare data sake iya ɗagowa ta kallesa ba tace, “Barka da dawowa”.
“Uhhumm”.
Ya faɗa a miskile idonsa nabin jikinta da kallo. Kaya ƙanana ne da sukai matuƙar kama ɗan jikinta komai ya fita fili tamkar an zana. Ya janye a kasalance dan dama acan ɗin ma kwalliyar Fadwa ba karamin tasiri tai a ransa ba. Ya yarda matan nasa duk ƴan gayu ne, sai dai Fadwa tafi Anaam son ƙyale-ƙyale, dan da wuya kaga fuskar Fadwa babu kwalliya hakan kuma na matuƙar burgesa. Saɓanin Anaam da zai iya cewa bai taɓa ganin kwalliya ba a fuskar tata ba, sai dai idan ya manta. Idan son samune itama zai so ta dingayi ɗin dan yana da tabbacin zata mata ƙyau.
“Da rana mi kika ci?”.
Ya jeho mata tamyar idonsa na kallon bakinta dake juya alawar a ciki batare data riƙe tsinken ba. Yanzu ma bata iya ta kallesa ba, ta damƙe wayarta da take juya a hanunta da ƙyau. Muryarta can ƙasa tace, “Noodles”.
Ɗan jimm yay da tunanin taya ta dafa. “Dami kika dafa to?”.
Ɗagowa tai ta dubesa da mamaki. “Kamar ya?”.
“Nasan baki da gas ai”.
“Nayi amfani da electric ne”.
Ajiyar zuciya ya sauke na samun nutsuwa, dan gaba ɗaya ya shafa’a ne ma, dama yau yaso a siyo mata gas ɗin a kuma haɗa mata tvn ta.. Duk yanda yaso basar da abinda ke tsikararsa ya kasa. Ƙara matso jikinsa yay a nata sosai da riƙo hannayenta duka numfashinsa na sauka a gefen wuyanta. A take tsigar jikinta ta tashi, taja jikinta baya zata matsa ya rungumota, kallonsa tai fuska a marairaice, sai dai bazata iya jurewa ba tai ƙoƙarin rissinarwa amma sai ya hana hakan ta hanyar tallafo haɓarta..
“Yanzu tsabar rowa bazaki sammin sweet ɗin ba?”.
Wutar kan Anaam neman ɗaukewa tai, tsigar jikinta ta tashi har tana ƙoƙarin yadda alawar babu shiri. Gaba ɗaya yanayin nasa da muryar dayay amfani wajen mata maganar ya matuƙar rikitata, dan bata taɓa jin irin muryar tare da shi ba. Hannu takai jiki a mace zata zare alawar a bakinta ya riƙe hanun tare da matsota suna kallon juna cikin ido.
“A haka nake son sha”.
(Ya ALLAH) ta faɗa cikin zuciyarta, a zahiri kam tuni idanunta sun fara marmarin firgici da tsantsar mamakinsa. Ya kashe mata ido ɗaya da sake kusanta fuskarsu, baya ta ƙara jan jikinta ya bita, ta ƙara matsawa shima ya matsa, ta ƙara ya ƙara, sai kawai ta zube a gadon da ƙokarin tufo alawar waje kawai a ganinta hakan shine mafita gareta.
Murmushi ya saki a karo na farko, shanyayyun idanunsa da launinsu ya canja gaba ɗaya na bin fuskarta da kallo, ya ɗauka alawar ya saka a bakinsa ya ɓalla kaɗan. “Ni ban iya rowa ba zan sammiki” ya faɗa tare da ɗage mata gira ɗaya yana matso da bakinsa gab da nata.
“Ba gashi nan na baka ba”. Ta faɗa a hankali kamar mai raɗa.
“A cikin bakinki nake son sha ni”. “Ban yarda ba”.
“Ba sai kin yarda ba dama tunda nawa ne”.
“Naka? Yaushe ya zam….” Ruff ya rufe bakin tare da tura mata sweet ɗin a nata bakin, ya haɗa da harshenta ya fara tsotsa. Wani irin miƙewa illahirin gashin jikinta sukai, takai hanunta saman ƙeyarsa da nufin janye masa kai hakan ya gagara. Domin wani irin salo yake mata mai narkar da ita, dole ta lumshe idanunta a hankali ta fara bashi gudunmawa. Sai da suka shanye alawar tas a cikin bakinta sannan ya janye. Kanta ta kauda gefe wata irin kunyarsa mai girma na ratsata. Sassanyan murmushi ya saki da leƙa fuskartata, tai saurin ɗaukar fillo ta ɗora tana murmushi itama. Ƴar dariya yayi da ƙoƙarin tashi tsaye. “Ga tsoro ga tsiwa, kona dawo mu shanye sauran?”.
Da ƙyar ta iya fisgar numfashi ta haɗiye, ta bude idanu hannunta dafe da ƙirjinta. Dariyarsa ya danne da ƙyar yana gyara rigarsa da jifanta da wani kallo daya sata janye nata idon akan sa, “Oya tashi muje cin abinci”. Ajiyar zuciyar ta ƙara saki, batare data yarda ta kallesaba ta girgiza masa kanta. “Ni na ƙoshi fa”.
“Amma kin san zan iya ɗaukarki daga nan har can kuma akwai Matata”.
Har cikin rai maganarsa ta soketa, to ina ruwanta wayace ba matar tasa bace. Ta murgiɗa baki a zahiri da ɗauke kai gefe tana ƙunƙuni. (Wani yace ba matarka bace balle ka mana burga). Sarai ya jita, amma sai baice komai ba ya ɗan matso kusa da ita. Zabura tai gefe tana tura baki. “To bana tashi ba dai”. Hanya ya nuna mata. Hijjabin sallarta ta zara dayin gaba tana kumbura fuska, ya biyota a baya yana murmushi dan ya gama yanke shawarar ayita ta ƙare kawai ya tabbata haka shi zai kawo masalaha ta ƙarshe da zuciyarsa ke tabbatar masa..