BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

   Duk yanda mmn Abu ta lallaɓata akan ta koma ciki ta kasa motsawa, dan haka harya dawo gidan tana a wajen zaune ita bamai rai ba ita ba sumammiya ba, har yanzu kuma su Gwaggo halima basu kiratanba. Bai shigo ciki da mota ba, dan haka har ya ƙaraso bata san da shi ba. Yay tsaye yana mata kallon mamaki ganin hawaye share-share akan fuskarta dan ma wasu sun jima da bushewa…

   “Baki da lafiya ne?”.

Ya faɗa yana kaiwa tsugunne gabanta da ɗago fuskarta daya riƙo haɓarta da hanunsa na dama. Maimakon amsa sai kawai ta sakar masa sabon kuka. Sosai hankalinsa ya tashi, dan zuciyarsa ta fara ayyana masa ko wanine ya mutu ma. 

      “Ya salam, wai mike faruwa? Wani ne ya mutu ina magana kin mun shiru?”.

   Hanunsa tai ƙoƙarin turewa zata miƙe ya maidata ya zaunar. “Fadwa….!” 

ya faɗa aɗan tsawace

   “Ni ka ƙyale ni!!”.

Ta faɗa a matuƙar tsawace itama da fisge duka jikinta ta shige ciki a fusace. 

Kallo ya bita da shi ransa na sosuwa da mamakinta, shi yarinyar nan takema tsawa wai?. Kallonsa yakai ga Mmn Abu dake tsaye kanta a ƙasa idonsa cike da matuƙar ɓacin rai. “Mi’aka mata?”. 

     “Nima Alhaji ban saniba, tun ɗazun dai na sameta tana kuka anan lokacin da zaka fita da Hajiya Amarya”.

  Ɗan jimm yay na tunani yana idonsa akan Mmn Abu ɗin har yanzu. Komai baice ba yay wucewarsa sashensa yana jan tsaki. Akan kwanikan abinci da aka ajiye ya fara sauke idonsa, kenan idan lissafinsa yayi dai-dai Fadwa taga fitarsa da Anaam shine take wannan haukar. Ƙaramin tsaki yaja da girgiza kansa kawai ya shige bedroom. Bai jimaba ya fito. Sashen Anaam yaje, ya ɗauka mata abinda za’a buƙata ya sake ficewa a gidan batare da yabi takan Fadwan ba. 

    Tun a hanya ya sayo dukkan maganin, koda ya dawo asibitin har lokacin tana barci, ya ajiye kayan ya nufi office ɗin Dr Jamal. Saida suka fito yin sallar azhar ya ɗan leƙa Anaam, har lokacin barci take, dan haka Dr Jamal yasa wata Nurse shiga ta zauna da ita saboda Shareff yace masa zaije wani waje daga nan tunda yaga ba yanzu zata farka ba….

   Barci tasha sosai, sai kusan biyu da rabi ta farka. Jinta take kamar ana mammatsa mata ƙasusuwa, ga ɗinkin da akai matan nayi mata kamar a takure babu dai daɗi. Nurse ɗin nan ta taimaka mata zuwa bayi kamar yanda ta buƙata. Harda kukanta wajen yin fitsari, wani haushin Shareff na ƙara zuwa mata a maƙoshi. A daddafe ta sake fitowa da taimakon Nurse ɗin, tai salla jiri na ɗibarta na yunwa da rashin jin daɗin jiki. Ta idar da sallar tana addu’ar ya shigo da sallama Aysha biye da shi ɗauke da basket, Aunty Mimi a bayansu. Batai niyyar ko kallonsa ba, sai dai jin muryar Aunty Mimi da Aysha ya sakata ɗagowa da sauri………✍

End of book
Leave a comment

Post

Comments

106395735749763123617
Hehhee Ina masu cewa Shareef fyade ya yiwa anam to kuzo kusha kallo????ga ruwan love

14 hours ago

112061044133690897194
Karshen tonan asiri kuwa,anam taji maza,an kashe bakin tsiwan

14 hours ago

umarfaruk
Mr sherif tonon asiri kayi ma Anam kenan Dama dai Aunty Mimi tace babu so Miya kawo kishi to ga so nan ya tabbata harda kwanciya a gadon asibiti

14 hours ago

Contact Us
Arewa Books Publishers

WhatsApp: 09031774742

Email: arewabookspublishers@gmail.com

Navigation
Home
About
FAQ’s
Legal
Privacy Policy
Terms of Service
Social
Facebook
Instagram

Copyright 2021, Arewa Books | ALL RIGHTS RESERVED | Powered by thinkcrypt.io
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: BABU SO
Chapter 60
60

…….Cikin nasa idanun suka shiga, sakamakon kallonta yake shima. A karan farko taji hakan babban abune a gareta kallon tsakkiyar idonsa tai masa koda harara ne. Janyewa tai a kasalance ta maida ga Aysha dake kallonta fuska da damuwa duk da bata san mike damu ƴar uwar tata ba. Dan ita dai tana gida ya kirata a waya wai ta ɗakko kaya kala ɗata ta fito ta samesa an kwantar da Anaam asibiti. Ya kuma mata gargaɗin karta sanarma kowa, Mommy ma tace mata zataje waje Fadwa ne. Hakaɗin tayi shine ta sami damar fitowa dan itama Mommyn na buƙatar aje mata gidan Shareff ɗin duk da tasan ba lallai ta sami abinda take so ga Ayshan ba. Amma tasan ta inda zata dinga binta tana jin koma ai. Amma sai ta kasa kallon aunty Mimi da itama kallonta take duk da bata san mike damunta ba, ya sanar mata dai kawai Anaam babu lafiya, sai dai bai son su Mamie su sani.

    Matsowa Aysha tai suka rungume juna, idon Anaam cike da ƙwalla. 

 “Blood mike damunki?”.

Ɗan satar kallonsa tai shi da aunty mimi, idanunsa ƙyam a kansu, Hawayenta ta share da girgiza mata kai kawai alamar babu komai. 

    “Blood ba’a zuwa asibiti ai babu komai, dan ALLAH ki faɗamin”.

   Katse Ayshan yay da faɗin, “Idan kinji maganin mi haka zai miki?, malama tashi ki bata abinci ban son surutu mara amfani”.

   Badan Aysha taso ba dole tai shiru. Aunty Mimi ta ƙaraso ta zauna saman kujera, gaba ɗaya Anaam ta kasa kallonta, idanunta a rissine tace “Ummi good afternoon”.

   “How are you feeling?”.

  Kasa amsawa tai sai hawaye data matso. Aunty mimi tai murmushi, “Mamana har yanzu baki san kin girma ba, shagwaɓa dai shagwaɓa dai why?” nanma batace komai ba, aunty mimi da zuciyarta ke ɗan hasko mata wani abu ta kalla Shareff, shima kansa yay saurin kaudawa gefe yana shafo bayan ƙeyarsa da hannu. “Humm” tace kawai. Itace ta taimaka mata ta koma saman gadon. Aysha kuma ta fara zuba mata abinci. Takowa yay daga inda yake tsaye ya zauna kusa da ita a gefen gadon. Jitai kamar ta makesa sai dai babu dama. Koda Aysha ta gama zuba abincin shine ya amsa, sake gyara zamansa yay yana fuskantarta da ƙyau, sai dai taƙi yarda koda wasa su haɗa ido. 

  “Ko zaki sha tea ne kafin kici abincin?”. Ya faɗa idonsa a kanta. Girgiza masa nata kan tayi, murya a shaƙe tace, “Bazanci komai ba na ƙoshi”. 

     Komai baice mata ba, ya ɗibo abincin zuwa bakinta yana faɗin, “Hahh!”. 

Sosai ta ƙwaɓe fuska, ta ɗan ɗago cikin marairaicewa tana kallonsa, sai kuma ta saci kallon gefen aunty mimi. Ganin basu take kallo ba ta ɗanji sassauci kaɗan. Kanta ta girgiza masa “Banajin cin komai ALLAH”.

   Ƙasa-ƙasa yace, “Gashi kuma dole sai kin ci! In ba haka ba kuma…..” ya ɗage mata gira ɗaya batare daya ƙarasa faɗaba. Dole badan taso ba ta buɗe bakin ya fara bata abincin da tun a ɗanɗanon farko ta gane girkin Mamienta ne. Kasa ɓoyewa tai. 

   “Yaya wajen Mamie ka amso min abinci?”.

  Kansa ya jinjina mata da kai babban yatsansa ya goge mata mai daya taɓa gefen bakinta. Sai taji kunya ta kamata kasancewar Aunty mimi da Aysha a ɗakin. Shiko babu alamar hakan ya damesa ma ya sake miƙa mata wani daya ɗibo a spoon. A haka Dr Bilkisu ta shigo ta samesu yana bata abincin, a ranta ta ayyana (Maza ga zaƙi ga harbi kenan). A zahiri kam idonta akan Anaam tana murmushi. “Masha ALLAH my patient jiki yayi daɗi”.

   Cikowa idanun Anaam sukai da hawaye, ta girguzama Doctor kanta. “Har yanzu inajin ciwo a wajen”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button