BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

WASHE GARI.
Sai wajen takwas yabar gidan zuwa asibiti batare da yabi takan Fadwa ba, tun da suka baro asibiti jiya suke tafka rigima da ita, dan kuwa ya mata tatas akan abinda taima aunty mimi, ya kuma tabbatar mata inhar ta ƙara sai ya mata abinda bata taɓa zato ko tsammani ba daga garesa.
Gargaɗinsa ya sakata kwana kuka, ta kira gwaggo halima kuma ta hanyar wayar mmn Abu data kira wayar cikin masu aikinsu aka haɗata da maman, zayyane mata komai tayi, suka haɗu sukaita zagin su aunty Mimi wai asiri ne ke cin Shareff ɗin. Amma zata ɗauka mataki ta saurareta.
Ya iske Anaam ɗin na toilet tare da Dr Bilkisu tanayi sit bath. Yana iya jin rakin da take zubawa daga nan, ya girgiza kansa kawai da kaiwa zaune a bakin gadon yana murmushi. A haka Aysha ta shigo hanunta ɗauke da flask ɗin tea. Gaisheshi tayi, ya amsa yana kallon flask ɗin.
“Daga ina?”.
“Yaya gidan Dr Bilkisu mukaje amso ruwan zafi anan cikin asibitin”.
Bai sake cewabkomai ba akan hakan. Itama saita ajiye flask ɗin.
“Kunyi barci dai babu wata matsala ko?”.
“Eh Yaya. Ai da yake a magungunan nata kamar akwai masu saka barci harma makara tayi sallar asuba.”
Bai samu damar bata amsa ba suka fito Anaam na tafiya da ƙyar. Suna haɗa ido ta dalla masa harara dan duk wannan dai bala’in shine yaja mata ai. Shi dai kallonta kawai yake murshi na neman suɓuce masa, tana tafiya kamar wata ƴar kaciya. Doctor ce ta katsesa daga kallon nata. Ya ɗauke kai suka gaisa. Baƴani ta ƙara masa na cewar zatama sallamesu amma sai zuwa anjima kaɗan dai haka akwai abinda zata ɗan jira a kawo mata da zata bama Anaam ɗin.
A taƙaice ya mata godiya yana maida hankalinsa ga Anaam daketa faman sauke ajiyar zuciya daga kwancen da take ta juya masa baya. Tai musu sallama ta fice tana faɗama Aysha taba Anaam ɗin abinci amma ta fara da tea mai zafi. Kamar jiya dai koda Aysha ta haɗa abincin shine ya karɓa. Cikin bada umarni yace ta tashi zaune. Taso sharesa, sai dai a yanda yay maganar ya tilastata tashi dole bakinta a sama. Yi yay kamar bai ganta ba. Ya miƙa mata shayin ta amsa kamar zata fasa ihu. Sai da ta gama shanye tea ɗin tas sannan ya miƙa mata abincin, amma sai tace ta ƙoshi. Bai saurareta ba ya fara ɗiba yakai bakinta, ta kalesa kamar zatai kuka.
“Nifa Yaya nace na kos…”.
Ta kasa ƙarasawa saboda kallon daya wulla mata cikin tsakkiyar ido. Idanunta ta lumshe tsigar jikinta na tashi, dole ta buɗe bakin ya zuba mata. A dai-dai nan Dr Jamal ya shigo. Da alama ma shigowarsa asibintin kenan. Sun gaisa ya tambayi mai jiki, bai jimaba ya fita yanama Shareff dariya da shaƙiyanci da ido. Bai dai kulasaba shi dai.
Karfe kusan sha ɗaya aka basu sallama. Zuwa lokacin yaje office ɗin Dr Jamal ya dawo. Aysha ta tattare kayansu shi kuma ya kama Anaam ɗin da taso botsare, sai dai ya hana hakan ta hanyar tabbatar mata zai ɗauketa. Dole ta nutsu tana tura masa baki. Yay murmushi kawai da sumbatar wuyanta. Mintsininsa tai ya dafe wajen yana ɓata fuska shima. Sai ta saki dariya da masa gwalo………✍
????????Za’a koma filin wasa????????
ZAFAFA BIYAR
INAYAH
MamuhGee
GURBIN IDO
Safiya Huguma
SANADIN LABARINA
Hafsat Rano
FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)
BABU SO
Billyn Abdul
Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k
YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107
ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: Menu
Dashboard
My Library
Create Story
Home
About us
FAQ’s
Privacy Policy
Terms of service
Logout
BABU SO
Chapter: 63
Share:
Report
BABU SO
View: 432
Words: 2.3K
Chapter 63
63
………Tsaf ya shanye jambakin, zaune takai tana sauke numfashi, shima barin wajen yay da ɗan hanzari, tanaji ya buɗe toilet amma bata iya ta ɗago ba. Babu jimawa ya fito da alama wata sabuwar alwalar ya sakeyi. Ƙofa ya nufa batare daya yarda ya sake kallonta ba yana faɗin, “Ki tashi kiyi salla”.
Iska ta furzar mai ƙarfi da dagowa tana kallon kanta ta cikin mirror, sai kawai ta samu kanta da kai hannu ta shafi lips ɗin nata da sakin murmushi. “Fitinanne”. Ta faɗa a hankali tana mikewa. Itama alwalar ta ɗauro, bayan ta gabatar da salla samun kanta tai da komawa gaban mirror ta sake gyara fuskarta da ƙyau cikin simple kwalliya. Kwalli, lipstick ɗin daya saka mata ta ɗan gyara girarta siririya da ƙara powder. Ita a karan kanta sai da ta tsaya kallon kan nata dan wani ƙyau taga ta kara, tai guntun murmushi da ɗaukar turare ta ƙarama jikinta..
Ana idar da salla ya dawo gidan, saboda makara salla daya nema yi bai shiga sashen Fadwa ba ya wuce, yanzu kam daya dawo sai ya fara nufar can, wannan ƙa’idarsace, akowace salla in har yana gida sai ya tabbatar da mace tayi hankalinsa ke kwanciya, ko yana office yakan ƙokarta ya kira domin tambayar kinyi salla, hakan ya ƙara ƙarfafa Fadwa domin waya takan ɗauki hankalinta ta kasa tashi yin salla akan lokaci kafin zuwanta gidansa matsayin mata. A bedroom ya sameta ta idar da salla fuskarta duk babu walwala. Ya ɗan tsura mata ido na wasu sakanni kafin ya ƙaraso ciki sosai. Sau ɗaya ta kallesa ta janye idonsa da masa sannu ciki-ciki.
“Wani abu ya faru ne?”.
Ya tambaya a maimakon amsa mata sannun da tai masa. Batai magana ba, sai dai ta sake ɗan tsuke fuska.
“Nasan kin jini fa”.
Kamar bazatai magana ba sai kuma ta ɗago idanunta dake tara ƙwalla tana kallonsa, “Soulmate karka juyamin baya dan kayi aure, maƙiya zasu iya yimin dariya”.
Mamaki shinfiɗe akan fuskarsa yake kallonta. “Juya baya kamar ya? Anyi wani abu ne?”.
“In ma ba’aiba ga hanyar yi nan an ɗakko ai. Tunfa da matarka ta dawo gidan nan yau baka sake leƙoni ba, kana ganin hakan adalci ne? Yaufa ko zuwa kacemin na tashi nai salla bakayi ba, kuma tun ɗazun kana’a sashenta ita dan daga can ka wuce massallaci, gaka nan harda canja kaya alamar yin wanka”.
“Dama kin saka a ringa miki gadina ne? Ko kuma shiga sashen nata ma akwai wata ƙa’ida ta mintunan da zanyi na fito? Ni da matata kuma kina tuhumata dayin wanka kamar wanda ya ajiye wata karuwa”.
“Niba haka nake nufi ba, amma dai koyaya ai sai kana adalci. Jiya yini guda kuna tare a asibiti, hakama yau tun fitar safe da kai kuka dawo tare kana a sashenta”.
Sosai ɓacin rai ya bayyana akan fuskarsa, idanunsa daya tsareta da su har suna canja launi. “Okay ke da sokike na watsar da ita kenan a asibitin nazo na tare a wajenki bayan nine sanadin zuwanta can. Ko kuma dan kar ranki ya ɓaci bazanyi wanka a sashenta ba?. Look Fadwa idan kikace zaki ɗaukemu zuwa wannan layin bazaki taɓa shan lalai a wajena ba. Idan kin manta bara na tuna miki, Juwairiyya matata ce, idan yanzu na shiga inda take ta rayamin kasancewa da ita zan samar da wannan farin cikin nai wanka na fito koda anjima hakan zai ƙara bijiromin idan ma wannan kikema zagaye-zagaye zargin nayi. K da ita duk abu ɗaya kuke a wajena, ina fatan kuma tsaida adalci akan kowaccenku. Duk wacce take da wani tuggu nason rinjayata gareta ita kaɗai na cutar da ƴar uwarta ALLAH ya hanata wannan damar ko wacece a cikinku. Abu na ƙarshe dazan gaya miki shine daga yau ki sani Ina son Juwairiyya! bawai cushenta akai minba kamar yanda na fahimci ke tunaninki ke kaiki. Yanda na aureki domin so bisa jagorancin iyaye haka itama na aureta, kuma koda ace iyayenmu basu ɗaura mana aure ba ni da kaina Zan nema aurenta, dan hakan burina ne, hatta wannan gidan da sunanta aka ginashi itama, kema shaidace tunda sashe biyu kika tarar. Kinga sai ki sakama zuciyarki salama, ki nisanta kanki da zama mai fuska biyu a gareni, dan bazan daina kasancewa da ita ba domin farin cikin. Sannan ita bata taɓa nuna damuwa da kasancewata a wajenki ba abinda ke gabanta takeyi, mtsoww stupid har kina faɗamin wai na dinga adalci”. Ya juya ya fice a fusace.