BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

Hannayensa duk biyu ya dafe da bangon tana a tsakkiyarsa. Ƙasa tai da idanun nata da sauri tana ƙara damƙe towel ɗin data fisga tun miƙewarta ta suturta jikinta. Ƙasa ya farayi da hanun damarsa a hankali har zuwa kan makunnar shower, sai saukar ruwa kawai taji a kansu a bazata harta ɗan tsorata babu shiri ta ɗago, bazata iya jure kallon cikin idanunsa ba, dan wani irin al’amari daya girmi ƙwanyarta take hangowa a cikinsu da har suke neman sare ƙarfin gwiwarta, faɗawa tai jikinsa kawai ko hakan zai bata nutsuwa. Haka yake buƙata dama, ya saki ɗan murmushi da naɗe hanunsa duk biyu a bayanta ya rungumeta ruwan na cigaba da sauka a kansu. Kusan a tare suka saki nannauyan numfashi, cikin dabara ya janye towel ɗin da taketa faman riƙo yay ƙasa da shi, tsam ta matsesa dan bata buƙatar ya ganar mata jiki. Murmushi mai ƙayatarwa ya sake saki da ƙara matsetan shima yana saki wasu zafafan ajiyar zuciya a jere….
Gaba ɗaya ya ƙulleta da kunya, tai wuff ta fara fitowa daga toilet ɗin da alama bakin tsuwar dai ya mutu, sai dai ko gaban mirror bata kai ba shima ya fito. Tana ƙoƙarin ɗaukar hijjab dan tasa ya riƙesa, saman gado ya wurgasa tareda ɗaura mata towel ɗin hanunsa saman kai ya fara tsane mata jiƙaƙƙiyar sumarta.
“Har yanzu fushin ne dai baki huceba?”.
Tayi kamar bata jisa ba, sai dai taɗan saci kallonsa ta gefen ido fuskarta a kwaɓe.
Ya ɗan ɗalle mata lips. “Nifa bana son shariya”.
Bakin ta dafe da janye hanunsa da towel dake saman kanta zata bar wajen. “Ni karka sake kulani, kuma matarka ta daina shigomin sashe ban son gulma. Kuje can ku ƙarata kuma cinye kanku tsabar son kai”.
Dariya sosai taso kufce masa, amma yay ƙoƙarin dakewa sai dai murmushinsa ya ɗan bayyana. Shima ƙarasawa yay gaban mirror ɗin inda takai zaune saman stool tana ƙoƙarin zuba mai a hanunta. Ta bayanta ya ranƙwafa tare da ɗaura kansa a wuyanta ya dafe duk hannayensa akan katakon mirror ɗin.
“Mi matata kuma tayi? Ko zaki huce haushinnne a kanta. Faɗamin, wai BABU SO! MIYA KAWO KISHI?”.
Dakatawa tai daga shafa man datai niyyar farawa, ta ɗago idanunta dake cikin gilashi suka haɗa ido ta cikin mirror. Da sauri ta janye nata tana cuna baki gaba. “Yaya kaima kasan SO ɗin da kishin. Da zaka rarrabe munma wlhy dana biyaka”.
Murmushi ne ya sake suɓuce masa, yasa hannu ya karɓe man hanunta ya ajiye, sake ƙoƙarin ɗauka tai ya riƙe hannun. Dole ta ɗago tana kallonsa, hakan ya bashi damar da yake buƙata, ya sarƙe idanunta a cikin nasa yanda ya tilasta mata tsaiwa suka kurama juna ido, kallon juna suke irin na tsakkiyar idon nan mai ratsa jinin jiki da bargo ya sunce duk wani ƙwarin laka da jijiyoyi. A hankali lips ɗinsa suka fara motsawa…
“Kin tabbatar idan na rarrabe mikin zaki biya ni?”.
Da wani salon zamtowarta jiki a kasalance ta janye idanunta a slowly, shima janye nasan yay da wani salon lumshewa da buɗewa tare da miƙewa da ƙyau ya juyota suna fuskantar juna saboda kujerar na juyawa.
“Yayaaaa!”.
Ta faɗa a shagwaɓe.
“Yayoo”.
Ya bata amsa da sake ranƙwafowa akanta tamkar ɗazun, banbancin kawai yanzu suna fuskantar junane. Turashi ta ɗan farayi amma ko gezau, sai ma hanun daya riƙe ya ɗaura saman fuskarsa daga gefen kunne. “Idan kin isa kalla cikin idona ki maimaita abinda kika faɗa”.
“Ba buƙatar haka ai Yaya tunda nasan kaji. Aysha fa na gidan nan, kaima kuma matarka nacan na jiranka”.
“Uhmm Madam pretender ke kuma budurwa tace ko?”.
“Hu’um nayi me da kai? Kamun tsufa”.
“Yanda kikai dani daren shekaranjiya mana”.
Janye hanunta tai da ƙoƙarin juyawa tana faɗin, “Kai dai ka sani”.
Yanzu kam ƙaramar dariya ya saki mai faɗi da miƙewa sosai akan ƙafafunsa. Yitai kamar bata jisa ba taci gaba da shafa manta yana kallonta kamar ya samu tv. Saukar kiran salla a kunnensu ya sakasa kallon agogon ɗakin, ya ɗan furzar da numfashi dan yasan sai ya sake sabuwar alwala.
Binsa tai da kallo ta gefen ido, yana shigewa ta taɓe baki da miƙewa tana magana ƙasa-ƙasa. Kaya ta saka sauri-sauri kafin ya fito. Tayi ƙyau sosai dan ƙanan kaya sun zame mata jiki matuƙa, har takai komi ta raɓama ɗan jikinta sai ka ganta kamar ka sace. Kallo ɗaya ya mata ya ɗauke kansa, dan ya tabbata ya cigaba sunan alwalarsa karyayya again. Ita bama tasan yanai ba, powder take ɗan shafama fuskarta da ɗan lipsgloss, dan ko kwalli ba sakawa take ba sai Mamie ta tsaya a kanta. A ransa yake raya da kwalliyar tafi haka daya so, sai dai yasan ita ƴar darun tasa a wajenta hakan normal ne. A haka ɗinma tayi ƙyau sosai.
Ita ko sanin kaya yake canjawa yasa taƙi juyowa, harya gama shiryawa cikin wandon jeans blue da pitch shirt mai dogon hannu. Jin tsaiwarsa a bayanta ya sata ƙoƙarin barin gaban mirror ɗin, amma saiya riƙota ta hanyar saƙala hanunsa saman cikinta ya manna bayanta da ƙirjinsa duk da bata kai har can sama ba. Ɗagowa tai tana kallonsa kamar yanda shima yake kallonta. Ganin ya ɗago lipstick da dayan hanunsa ta maida idonta akai. Saman lips dinta ya ɗaura, zatai magana yace mata “shiii!”.
Shiru ta haɗiye abinda take son faɗar, shi kuma ya fara goga mata. Sai da ya gama ya juyota suna fuskantar juna, bakin ta ɗan tunzura gaba ganin yanda yake kallonta.
“Nifa shanyewa nakeyi shiyyasa bana sawa”.
“Oh really? To bara na shanye abuna kafimma ki shanye min”.
Idanunta ta waro waje da zaburowa zatai magana ya samu damar sauke lips ɗinsa akan natan. Dole ta koma tai laƙwas dan bai musu kamun wasa ba……..✍
Shareff adai rage cin amanarmu????????????????.
reeey
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: 64
BABU SO
Chapter: 64 Share:
Report
BABU SO View: 167 Words: 2K
Chapter 64 64
……..Dariya take tana masa gwallo. Fuska ya
ɓata, da harɗe hannayensa a ƙirji irin yayi
fushin nan. Yanda yay ɗin sai ya saka Anaam
shiga ƙyalƙyala dariya da faɗin.
“Kai Yaya shagwaɓa kuma?! ALLAH kamafi
ƙyau a haka fuskanka so cute”. Ta ƙare
maganar da kashe masa ido dariyarta mai
ƙaramin sauti na bayyana fararen haƙoranta.
Ta nuna lips ɗinta da kaɗa masa idanunta
dake cikin gilashi.
“Indai lipstick ɗin nan ne Yaya ba shansa
zakai ba garama ka haƙura”.
“Oh oh haba princess kiji tausayina mana”.
Yaya maganar da matsar da fuskarsa gab da
tata.
Baya taja dasa hanunta ta kare bakinta,
“Babu wani princess na daɗin baki fa Yaya,
barima kaga na shanye abuna, idan baka
ganiba ai dole ka haƙura”.
Yana ƙoƙarin riƙota ta tura lips ɗinta cikin
baki da sauri.. Idanunsa ya waro sosai yana
kallonta cikin langaɓe wuya. Ta fito da lips ɗin
tana dariya da masa gwalo. “Sai kaci abinci yanzu babu”.
“Ni ko? Yarinya zan rama ne”.
Dariyarta ta cigaba dayi ƙasa-ƙasa, shiko ya
ɗauka spoon ɗin ya cigaba da cin aincinsa
fuskarsa da ɗan murmushi.
“Nifa yaya karka cinye min abinci na”.
Idanunsa ya ɗago yana kallonta, sai kuma ya
ɗibo abinci ya nufi bakinta, “Ba marowaci bane irinki ai hahh”.
Bakin ta buɗe ba musu ya zuba mata, a
hankali ta shiga taunawa da faɗin, “Nima ai
bana rowa”.
“Kika min yanzun?”.
“Baga abincina kana ci ba”.
Murmushi kawai yayi batare da yace komai
ba. Itama bata sake magana ba, ya cigaba da bata abincin shima yana ci. Suna gab da kammalawa wayarsa tai ring, ɗauka yay ya duba, ganin Khaleel sai kawai ya ɗaga. Bata san mi’akace masa a wayarba, sai gani tai ya miƙe da kama hanunta….
Da mamaki take kallonsa zatai magana ya girgiza mata kansa. Baki ta ɗan tura dan ita dai bata ƙoshi da abincin ba, sai dai babu yanda zatai dole ta bisa. Hango Khaleel jikin wata mota mai ƙyau fara tas jingine ya sata zare hanunta cikin nasa, bai ce komai ba har suka ƙaraso. Ita ta fara gaida Khaleel ɗin, ya amsa mata fuska da murmushi sannan ya maida hankalinsa ga Yayansa. Gaisheshi yay
da girmamawa. Ya amsa masa da kulawa. “Daga ina haka mazan fama?”.
Murmushin Khaleel ya faɗaɗa dan yana son Yayan nasa ya kirasa da sunan nan. Wani ɗan ƙaramin gi! ya ɗakko a gaban motar, ya dubi Anaam dake kallon motar da ita kanta an