BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

rayuwu, ta kuma riƙe kambunta na ɗiya mace. A
kwanakin da nayi biyar a gidan nan, na karanci
abubuwa masu dama a cikinsu, zan kuma fara
sharar fadata da su domin samun damar shimfiɗa
mulkina batare da wani datti ya sha gaban cikar
burina ba”.
“Woow vary interesting my blood. Haka nake
sonki dan ALLAH. Ki haukata mana Yaya Share”, ki
kuma dawo mana da Fadwa hanya tabar bin
karatun su Mommy, ta zama mai ra’ayin kanta”.
Anaam ta ƙyalƙyale da dariya, zuciyarta fes
tamkar an sauke mata dukkan wani nauyi da
ƙuncin da takeji a yau a yanzu yanzu. Basai
amfaɗa ba, da ni da mai karatu duk zamu fahimci
hakan nada nasaba da abinda taci karo da shi
wannda a baya bashi take kallo a fuskar Share”
ba. Sun ƙara tattaunawa sosai akan wasu
abubuwan da dama da Aysha kafin ta miƙe ta
koma sashen Share” domin gyarawa bisashawarar Aysha.
Bata jin daɗin jikinta saboda ɗinkin da akai mata
na sakata jinta tamkar a takure, ga tafiyarta har
yanzu bai zama normal ba kamar da. Amma haka
ta jure a daddafe na rashin sabon da wahala ta
gyara ko’ina na sashen nasa, sauƙin ma babu datti
mai yawa. Sai da ta tabbatar ko’ina ya mata da
kamshi sannan ta rufe ta fito. Baki ta saki tana
kallon yanda Aysha ta ƙara gyara sashenta itama.
Ta saki murmushi da harar Ayshan dake tsaye tana
karanta mata taje tayi wanka ta ɗauki ado dan
Yaya Share” na gab da dawowa. Akwai tsoro
tattare da ita na abunda ya faru, amma gargaɗin
likita akan Share” ya bata ƙwarin gwiwar
tabbatarma kanta babu wani abu tunda ko dai
baya cikin hayyacinsa ai baya nema wani abu daga
garetaba zaren ɗinki na a jikinta. Da wannan
tunanin ta faɗa wanka. Koda ta fito tsareta Aysha
tai wai sai ta mata kwalliya. Badan taso ba dole ta
tsaya kuwa Aysha ta zaneta tsaf dasu jaja leɓe da
barbaɗa kumatu na zamani. Turare kuwa har ji
take yana hawa mata kai dan khumras nata sun
sami haɗine na musamman daga hajiyar sudan,
ga kuma *_YERWA INCENSE AND MORE +234 809
521 5215 da miss xoxo tayo mata haɗi da sai ƴar
gata ke samunsa
!
_*. Hakama na kanti duk masu
tsadane da ƙamshi na musamman da aka zuba a
lefe. Ƙanan kayan nata taso sakawa, sai dai Ayshata hanata hakan, acewarta kayanmu na gida sunfi
mata ƙyau. Dole badan taso ba ta haƙura ta shirya
cikin skirt da riga na lass daya zauna mata a jiki
tamkar ka saceta ka gudu. Aysha tai mata ɗauri na
zamani daya saka ita kanta kasa rufe baki sai
faman kallon kanta takeyi a mirror da ƙyalla
hotuna da wayarta…..
A gajiye ya iso gidan bayan idar da sallar isha’i. Ya
fiddo ledojin daya shigo da su na fruits kashi biyu.
Sashen Fadwa ya nufa, ya sameta zaune a falo
ƙafa ɗaya kan ɗaya tanata cika da batsewa. Kallo
ɗaya yay mata ya ɗauke kansa dan ko sallamarsa
bata amsa ba. Ledar ya ajiye batare daya ce ko a
ba yay ficewarsa yana ƙwafa. Dan a yanda ta masa
ya bashi tabbacin tana kan sani taƙi ɗauka masa
wayarsa. Sashen Anaam ya nufa da ɗayar ledar
yanata faman furzar da hucin ɓacin rai……
✍
_
#
Shike nan an shiga tsakaninmu da
Soulmate
$
, dolene mu koma gidan…. Basai na faɗa ba.
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: jimawa, Anaam dafe da kanta dake mata ciwo
saboda kukan da tasha ɗazun, ga jikinta har
yanzu sam baya mata daɗi irin na shiga
sabuwar rayuwar da ba’a saba ba. Aysha ce ta
amsa masa sallamarsa, ya ƙaraso ciki idonsa
akan Anaam. Ya miƙama Aysha dake masa
sannu ledar hanunsa.
“Ita wannan lafiya kuwa?”.
“Kanta ne ke mata ciwo, nayi-nayi tasha
magani kuma taƙi”. Zaune yakai kusa da ita,
ya janye hanunta dake dafe da kanta. Kasa
kallonsa tai, dan haka kawai take jin wani irin
matsanancin kunyarsa. Shiko ya matuƙar
shagala ne a kallon kwalliyar dake zane akan
fuskarta, a kasalance yakai hannunsa kan
haɓarta ya ɗago fuskar da ƙyau, hakan sai ya
tilasta mata ɗago nata idanun dake cike da
ƙwalla ta kallesa. Ba ƙaramin jarumta yay
wajen jawo numfashinsa dake neman
kufcema ƙirjinsa ba, ya matsota jikinsa tare
da ɗaura hanunsa saman goshin nata.
“Wannan idon naki kinyi kuka da shi, ko
muje asibiti ne?”.
Ya faɗa a hankali cikin kunenta. Kanta ta
girgiza masa da ƙara lafewa a jikin nasa har
hakan ya so bashi mamaki. Dan yasan dai
koshi ya ringumeta turesa take kota janye
jikinta, amma yanzu ga saɓanin hakan yanagani, koda yake tunda abin nan ya faru ya
fahimci ta zama wata shiru-shiru, tsiwar taɗan
ragu kaɗan ko likimo ne, mata sunji maza
kenan. Fitowar Aysha ta sakata janye jikinta,
shima sai ya miƙe yana faɗin, “Bara na watsa
ruwa sai a samo miki magani”.
Baki ta ɗan tura masa da kaiwa kwance. “Ni
basai nasha magani ba fa”.
Juyowa yay daga niyyar barin falon da yayi,
“Oh tunda hakane tashi na fasa barinki anan
ɗin”.
Dole badan taso ba ta miƙe, dan ya tsuke
fuska babu alamar wasa, duk da dama dai
tunda ya shigo babu fara’ar tattare da shi.
Aysha da tuni ta koma kitchen yay kira. Fitowa
tai da sauri tana amsawa.
“Gyaramin fruits ɗin nan”.
“To Yaya. Ko’a haɗa salad?”.
“Duk yanda kikai is ok”.
Kanta ta gyaɗa masa, shi kuma ya kama
hanun Anaam suka fice. Ta bisu da kallo
murmushi bayyane akan fuskarta. Tana fatan
ALLAH ya hana su Mommy raba wannan
auren har abada. Dan sun kasance abin
birgewa best couple ever matuƙa”.
Koda suka iso sashen nasa a falon ya zauna,
ya riƙota saman cinyarsa ya zaunar. Yanzun
ma cikin mamaki yaga ta lafe a jikinsa. Ya ɗan
murmusa da shafar fuskarta idonunsa na binfuskarta dake ƙwaɓe alamar rashin jin daɗi
da kallo.
“Kodai har yanzu garden ɗin na zafinne?
Noorie!?”.
Kanta ta sinne a ƙirjinsa da riƙo hanunsa
dake kaiwa jikinta, dan zuwa yanzu ta fahimci
mi yake kira garden ɗin. “Yaya Please ka
daina”.
“No Aunty babu wannan zancen”.
Ya faɗa cikin kwaikwayon muryarta.
Murmushi ya kufce mata tare da ƙara cusa
kan nata cikin jikinsa. Dan yanda yay maganar
ya matuƙar bata dariya. Shima murmushi yay
da kaima wuyanta kisses. Tsoro ne ya kamata,
tai ƙoƙarin jan jikinta baya amma ya hana
hakan.
“Wayyo kaina zai fashe Yaya”.
Dakatawa yay daga ƙoƙarin cusa hanunsa
cikin rigarta. Ya riƙo kannata. “Ayya. Sorry,
sorry”. Sake langaɓewa tai kamar gaske. A
ƙasan ranta kuwa dariyace ke taso mata tana
dannewa. Da gaske kan nata na ciwo, amma
yanda takeyi ɗin yanzu harda pretending. Yin
hakan kuma shine mafita a gareta saboda
ganin yana neman sakin layi, itako a yanzu in
ba giyar wake tasha ba mizai kaita sallama
masa ya kasheta. Ai anyi kenan babu ƙari
tunda abun azaba kawai akesha a ciki. Ita jiya
tunaninta gaba ɗaya akan tayaya wasu matanke iskanci a cikin wannan wahalar? Ko kuwa
su basajin abinda taji da bazata taɓa
mantawaba har duniya ta tashi.
Zaunar da ita yay a kujerar ya shiga bedroom
ɗinsa. Dai-dai nan Fadwa tai sallama. Anaam
tai kamar bazata amsa ba sai kuma ta amsa
ciki-ciki. Sam Fadwa bataji an amsa ba, sai dai
sanin halin mai sashen da kuma halin da suke
ciki na fushi da juna ya sata shigowa a ganinta
kobai amsa ɗin ba zata shigo. Turuss ta ɗanyi
na ganin Anaam, sukaima juna kallon cikin
ido kowacce ta janye da takaicin ƴar uwarta
da tsagwaron kishi.. Basuyima juna magana
ba, Fadwa ta nema waje ta zauna.
Fitowarsa ta saka Fadwa ɗaga kai tana
kallonsa, shima ita ɗin yake kallo da mamaki
a ƙasan zuciya, sai dai a fuska babu ko ɗigon
hakan sai ma janyewa da yay cikin halin ko’in
kula ya nufi Anaam dake kallonsu ta ƙasan
ido. Ita dai bata san sunada wata matsala ba a
gidan. Dan haka bata kawo komai a ranta ba