BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

rayuwu, ta kuma riƙe kambunta na ɗiya mace. A

kwanakin da nayi biyar a gidan nan, na karanci

abubuwa masu dama a cikinsu, zan kuma fara

sharar fadata da su domin samun damar shimfiɗa

mulkina batare da wani datti ya sha gaban cikar

burina ba”.

“Woow vary interesting my blood. Haka nake

sonki dan ALLAH. Ki haukata mana Yaya Share”, ki

kuma dawo mana da Fadwa hanya tabar bin

karatun su Mommy, ta zama mai ra’ayin kanta”.

Anaam ta ƙyalƙyale da dariya, zuciyarta fes

tamkar an sauke mata dukkan wani nauyi da

ƙuncin da takeji a yau a yanzu yanzu. Basai

amfaɗa ba, da ni da mai karatu duk zamu fahimci

hakan nada nasaba da abinda taci karo da shi

wannda a baya bashi take kallo a fuskar Share”

ba. Sun ƙara tattaunawa sosai akan wasu

abubuwan da dama da Aysha kafin ta miƙe ta

koma sashen Share” domin gyarawa bisashawarar Aysha.

Bata jin daɗin jikinta saboda ɗinkin da akai mata

na sakata jinta tamkar a takure, ga tafiyarta har

yanzu bai zama normal ba kamar da. Amma haka

ta jure a daddafe na rashin sabon da wahala ta

gyara ko’ina na sashen nasa, sauƙin ma babu datti

mai yawa. Sai da ta tabbatar ko’ina ya mata da

kamshi sannan ta rufe ta fito. Baki ta saki tana

kallon yanda Aysha ta ƙara gyara sashenta itama.

Ta saki murmushi da harar Ayshan dake tsaye tana

karanta mata taje tayi wanka ta ɗauki ado dan

Yaya Share” na gab da dawowa. Akwai tsoro

tattare da ita na abunda ya faru, amma gargaɗin

likita akan Share” ya bata ƙwarin gwiwar

tabbatarma kanta babu wani abu tunda ko dai

baya cikin hayyacinsa ai baya nema wani abu daga

garetaba zaren ɗinki na a jikinta. Da wannan

tunanin ta faɗa wanka. Koda ta fito tsareta Aysha

tai wai sai ta mata kwalliya. Badan taso ba dole ta

tsaya kuwa Aysha ta zaneta tsaf dasu jaja leɓe da

barbaɗa kumatu na zamani. Turare kuwa har ji

take yana hawa mata kai dan khumras nata sun

sami haɗine na musamman daga hajiyar sudan,

ga kuma *_YERWA INCENSE AND MORE +234 809

521 5215 da miss xoxo tayo mata haɗi da sai ƴar

gata ke samunsa

!

_*. Hakama na kanti duk masu

tsadane da ƙamshi na musamman da aka zuba a

lefe. Ƙanan kayan nata taso sakawa, sai dai Ayshata hanata hakan, acewarta kayanmu na gida sunfi

mata ƙyau. Dole badan taso ba ta haƙura ta shirya

cikin skirt da riga na lass daya zauna mata a jiki

tamkar ka saceta ka gudu. Aysha tai mata ɗauri na

zamani daya saka ita kanta kasa rufe baki sai

faman kallon kanta takeyi a mirror da ƙyalla

hotuna da wayarta…..

A gajiye ya iso gidan bayan idar da sallar isha’i. Ya

fiddo ledojin daya shigo da su na fruits kashi biyu.

Sashen Fadwa ya nufa, ya sameta zaune a falo

ƙafa ɗaya kan ɗaya tanata cika da batsewa. Kallo

ɗaya yay mata ya ɗauke kansa dan ko sallamarsa

bata amsa ba. Ledar ya ajiye batare daya ce ko a

ba yay ficewarsa yana ƙwafa. Dan a yanda ta masa

ya bashi tabbacin tana kan sani taƙi ɗauka masa

wayarsa. Sashen Anaam ya nufa da ɗayar ledar

yanata faman furzar da hucin ɓacin rai……

_

#

Shike nan an shiga tsakaninmu da

Soulmate

$

, dolene mu koma gidan…. Basai na faɗa ba.
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: jimawa, Anaam dafe da kanta dake mata ciwo

saboda kukan da tasha ɗazun, ga jikinta har

yanzu sam baya mata daɗi irin na shiga

sabuwar rayuwar da ba’a saba ba. Aysha ce ta

amsa masa sallamarsa, ya ƙaraso ciki idonsa

akan Anaam. Ya miƙama Aysha dake masa

sannu ledar hanunsa.

“Ita wannan lafiya kuwa?”.

“Kanta ne ke mata ciwo, nayi-nayi tasha

magani kuma taƙi”. Zaune yakai kusa da ita,

ya janye hanunta dake dafe da kanta. Kasa

kallonsa tai, dan haka kawai take jin wani irin

matsanancin kunyarsa. Shiko ya matuƙar

shagala ne a kallon kwalliyar dake zane akan

fuskarta, a kasalance yakai hannunsa kan

haɓarta ya ɗago fuskar da ƙyau, hakan sai ya

tilasta mata ɗago nata idanun dake cike da

ƙwalla ta kallesa. Ba ƙaramin jarumta yay

wajen jawo numfashinsa dake neman

kufcema ƙirjinsa ba, ya matsota jikinsa tare

da ɗaura hanunsa saman goshin nata.

“Wannan idon naki kinyi kuka da shi, ko

muje asibiti ne?”.

Ya faɗa a hankali cikin kunenta. Kanta ta

girgiza masa da ƙara lafewa a jikin nasa har

hakan ya so bashi mamaki. Dan yasan dai

koshi ya ringumeta turesa take kota janye

jikinta, amma yanzu ga saɓanin hakan yanagani, koda yake tunda abin nan ya faru ya

fahimci ta zama wata shiru-shiru, tsiwar taɗan

ragu kaɗan ko likimo ne, mata sunji maza

kenan. Fitowar Aysha ta sakata janye jikinta,

shima sai ya miƙe yana faɗin, “Bara na watsa

ruwa sai a samo miki magani”.

Baki ta ɗan tura masa da kaiwa kwance. “Ni

basai nasha magani ba fa”.

Juyowa yay daga niyyar barin falon da yayi,

“Oh tunda hakane tashi na fasa barinki anan

ɗin”.

Dole badan taso ba ta miƙe, dan ya tsuke

fuska babu alamar wasa, duk da dama dai

tunda ya shigo babu fara’ar tattare da shi.

Aysha da tuni ta koma kitchen yay kira. Fitowa

tai da sauri tana amsawa.

“Gyaramin fruits ɗin nan”.

“To Yaya. Ko’a haɗa salad?”.

“Duk yanda kikai is ok”.

Kanta ta gyaɗa masa, shi kuma ya kama

hanun Anaam suka fice. Ta bisu da kallo

murmushi bayyane akan fuskarta. Tana fatan

ALLAH ya hana su Mommy raba wannan

auren har abada. Dan sun kasance abin

birgewa best couple ever matuƙa”.

Koda suka iso sashen nasa a falon ya zauna,

ya riƙota saman cinyarsa ya zaunar. Yanzun

ma cikin mamaki yaga ta lafe a jikinsa. Ya ɗan

murmusa da shafar fuskarta idonunsa na binfuskarta dake ƙwaɓe alamar rashin jin daɗi

da kallo.

“Kodai har yanzu garden ɗin na zafinne?

Noorie!?”.

Kanta ta sinne a ƙirjinsa da riƙo hanunsa

dake kaiwa jikinta, dan zuwa yanzu ta fahimci

mi yake kira garden ɗin. “Yaya Please ka

daina”.

“No Aunty babu wannan zancen”.

Ya faɗa cikin kwaikwayon muryarta.

Murmushi ya kufce mata tare da ƙara cusa

kan nata cikin jikinsa. Dan yanda yay maganar

ya matuƙar bata dariya. Shima murmushi yay

da kaima wuyanta kisses. Tsoro ne ya kamata,

tai ƙoƙarin jan jikinta baya amma ya hana

hakan.

“Wayyo kaina zai fashe Yaya”.

Dakatawa yay daga ƙoƙarin cusa hanunsa

cikin rigarta. Ya riƙo kannata. “Ayya. Sorry,

sorry”. Sake langaɓewa tai kamar gaske. A

ƙasan ranta kuwa dariyace ke taso mata tana

dannewa. Da gaske kan nata na ciwo, amma

yanda takeyi ɗin yanzu harda pretending. Yin

hakan kuma shine mafita a gareta saboda

ganin yana neman sakin layi, itako a yanzu in

ba giyar wake tasha ba mizai kaita sallama

masa ya kasheta. Ai anyi kenan babu ƙari

tunda abun azaba kawai akesha a ciki. Ita jiya

tunaninta gaba ɗaya akan tayaya wasu matanke iskanci a cikin wannan wahalar? Ko kuwa

su basajin abinda taji da bazata taɓa

mantawaba har duniya ta tashi.

Zaunar da ita yay a kujerar ya shiga bedroom

ɗinsa. Dai-dai nan Fadwa tai sallama. Anaam

tai kamar bazata amsa ba sai kuma ta amsa

ciki-ciki. Sam Fadwa bataji an amsa ba, sai dai

sanin halin mai sashen da kuma halin da suke

ciki na fushi da juna ya sata shigowa a ganinta

kobai amsa ɗin ba zata shigo. Turuss ta ɗanyi

na ganin Anaam, sukaima juna kallon cikin

ido kowacce ta janye da takaicin ƴar uwarta

da tsagwaron kishi.. Basuyima juna magana

ba, Fadwa ta nema waje ta zauna.

Fitowarsa ta saka Fadwa ɗaga kai tana

kallonsa, shima ita ɗin yake kallo da mamaki

a ƙasan zuciya, sai dai a fuska babu ko ɗigon

hakan sai ma janyewa da yay cikin halin ko’in

kula ya nufi Anaam dake kallonsu ta ƙasan

ido. Ita dai bata san sunada wata matsala ba a

gidan. Dan haka bata kawo komai a ranta ba

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button