BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

game da ɗaure-ɗauren fuskar tasu. A hanun

kujerar da take kwance ya zauna,

“Tashi kisha. Kimmaci abinci kuwa?”.

Sai da ta ɗan saci kallon gefen Fadwa sannan

ta ɗan tura baki da narke fuska. “Ni banajin

ci”.

“Uhhm baƙya son ci, yarinyar nan ki ragetaɓaran nan naki, yanzu abincin ma sai kin

nuna masa hali? Yanzu dai kinga ba’a shan

magani sai da abinci, faɗamin mi zaki ci?”.

Kallonsa ta ɗanyi da juya ƙwayoyin

idanunta, sai kuma ta narke fuska da girgiza

kai. “Da gaske bana son ci, barci nakeji kawai”.

“Uhm-uhm fa, bana son zama da yunwa

sam! Ki dai sha ko fruits ɗin can ne idan Aysha

ta kawo. Zakisha ko?”. Ya ƙare maganar da

ranƙwafowa kanta yana sinsinar wuyanta. Ta

gefen ido ta saci kallon Fadwa, sai taga su

take kallo fuskarta ciɗin-ciɗin kamar zata

fashe har wani jajaja takeyi na alamar ɓacin

rai abunka da fari. Murmushi tai mai sanyi

dakai hannu ta shafi fuskar tasa a ranta tana

faɗin (Ashe kin san akwai ciwo ni kike yi masa

kiss a gabana, zan koya miki iya zaman

duniya). Hanunta da take neman janyewa ya

cafke da sauri yana maidashi akan tattausan

gashin kumatun nasa. “Kin yarda zaki sha?”.

“Ni dai ɗan kaɗan”.

Ta faɗa a shagwaɓe.

Da ƙyar ya iya jan numfashi, dan shagwaɓar

tata ba ƙaramin susutashi take ba. “Good

girl”.

Murmushi tayi da janye hanun. Riƙeta yay, ta

marairaice masa. “Nifa fitsari zanyi”.

“Okayy to ana buƙatar abokin rakkiya?”.Ta faɗa da zille masa tana ƴar dariya.

Bedroom ɗinsa ta nufa batare da ko sashen

Fadwa ta kallaba. Tana shiga ta zube a

gadonsa dan babu wani fitsari dama. Kawai

dai taba Fadwa space ne. Domin rama abinda

tai mata bashike nufin bazata mata adalci ba.

Kuma koba komai yanzu kawai ta nuna mata

cewar alwashinta tabbatacce ne akan mantar

da Yaya MM ita in har tana a tare da shi.

Shiko daga can da kallo ya bita har saida ta

shige, a hankali ya haɗiye murmushi kan

fuskarsa. Miƙewa yay kamar zai bar falon.

Tasan idan tai wasa da wannan damar zatafi

haka shan wahala. Kamar yanda Mama

(Gwaggo halima) ta faɗa mata ba haka ake

buƙata ba, taje ta shirya dashi kodan

kasancewar gobe ne zata amshi girki, suna

buƙatar tai aiki da wasu fitinannun maganin

mata da aka kawo dominta tun daga ƙasar

sudan.

“Dan ALLAH kayi haƙuri” ta faɗa da sauri

tana ƙoƙarin haɗiye hawayen da tun ɗazun

take son su zubo ko zata samu sassauci.

Ratseta yay zai wuce tai azamar riƙosa. Bai

juyoba amma ya dakata. Ta share hawayenta

hanunta riƙe da nasa. “Dan ALLAH kayi

haƙuri, nasan nayi kuskure. Amma wlhysharrin shaiɗanne”.

Ransa a ɓace ya dubeta da wani mugun kallo

daya matuƙar neman gigitata. Saurin sakinsa

tai da girgiza masa kai. “Nasan nayi kuskure

amma dan ALLAH kayi haƙuri haka bazata

sake faruwa ba”.

“Tashi kibar min falo”.

“Please Soulmate dan ALLAH”.

Sallamar Aysha ce ta sakashi haɗiye maganar

bakinsa, ya koma ya zauna da amsa mata.

Itama hawayenta ta shiga sharewa idonta na

satar kallon ƙofar bedroom ɗinsa, dan

zuciyarta raya mata take Anaam na wajen

laɓe tana saurarensu. Sosai takejin raɗaɗi da

ɗacin hakan, amma taci alwashi komi zai faru

a yanzu ɗin bashi ne Anaam ɗin zataci itama

zata rama.

Aysha ta dire tray ɗin hanunta a gabansa,

fuskarta da murmushi ta gaida Fadwa da taƙi

kallonta saboda kar Aysha ta fahimci tayi

kuka. Kanta kawai ta jinjina mata. Ayshan

bata damu ba, dan tasan halin Fadwa wani

lokacin itama akwai yarfi. Hankalinta ta

maida akan Share!, “Yaya a zuba?”. Kai ya

girgiza mata alamar a’a, sai kawai tai musu

sallama ta fice a ranta tana ayyana akwai

matsala gaskiya, sai dai rashin ganin Anaam

yasa taji wani iri.

Kusa da shi ta taso ta dawo, “Soulmate……Hannu ya ɗaga mata a fusace. “Fadwa! leave

me alone. Tashi ki fita”.

Idanu ta tsura masa zuciyarta na mata

raɗaɗi, tasan a cikin fushi yake, kuma shi baya

son yanke ma mutum hukunci cikin fushi. Jiki

a saɓule ta tashi ta fice wasu hawaye masu

zafi da jin matuƙar tsanar Anaam na ƙaruwa a

ranta. Dan a ganin duk an mata hakane

saboda Anaam, ta kuma tabbatar ba haka

iyayen Anaam suka bar Share! ɗin ba kamar

yanda Mama ta sanar mata yanzun.

Ya jima zaune a wajen zuciyarsa na masa

raɗaɗi da ƙuna, baya son ɓacin rai da

damuwa, yama rasa ina zai kama da halin

matan nasa. Ya samu ita Anaam ɗin ta sakko

ya fara samun kwanciyar hankali ita kuma

Fadwar na neman rikita masa lissafi. dole ne

ya musu sabon shiri na zama da kowacce da

halinta. Yasan duk abinda Anaam zatai tana

yinsane a karan kanta sannan bata da ɓoye-

ɓoye. Fadwa kam ya fahimci akwai zugar

mutane baibaye da ita, dan tun zuwan Anaam

gidan ya fahimci ta ajiye wasu halayenta na

zahiri ta aro waɗansu daban, idan bai tashi

tsaye a kanta ba zasu iya laɓewa a bayanta su

tarwatsa masa farin cikin gidansa, shi kuma

harga ALLAH yana sonta itama. Ya furzar da

numfashi mai ɗaci, tunawa da Anaam dakecikin bedroom ya sashi miƙewa ya nufi

bedroom ɗin. Da mamaki yake kallonta

kwance a gado har tayi barci, ya tsugunna

saitin fuskarta yana sakin murmushi da kai

hannu ya shafa kanta. “Dama fitsarin ƙarya ne

kenan?”.

Idanu ta buɗe a hankali dan dama barcin

baiyi nisa ba, sai kuma ta maida zata lumshe

da ture masa hannu. Hannun nata ya riƙo

cikin nashi, fuskarsa gab da tata, “Tunda kin

tashi muje kisha fruit ɗin”.

“Ni na ƙoshi barci nakeji Yaya”.

“Ni kuma ban yarda ba idan kika sha sai kiyi

barcin”.

“Uhhum-uhhum”. Ta faɗa tana noƙe

kafaɗarta. Miƙewa yay yana murmushi, ya

ɗagata gaba ɗayanta. Watsal-watsal ta farayi

da ƙafafunta. “Wayyo Yaya! Wayyo Yaya ni ka

saukeni na ƙoshi”.

“Wayyo Aunty! Wayyo aunty ni bazan

saukeki ba sai kinsha”. Ya faɗa dai-dai suna

kaiwa falon………

End of book
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: BABU SO
Chapter: 67

………Da ƙyar ya iya lallaɓata tasha fruit salad ɗin, dan da gaske barcine a idonta sosai. Ganin tanata faman lumshe idanu dole ya barta. Itama sai ta miƙe tana ɗaga masa hannu. “Yaya good night”.

  Kafin ya samu damar cemata komai tabar falon da hanzarinta dan bata buƙatar yace zai dakatar da ita. Shima baiyi yunƙurin dakatar da itan ba. ya dai bita da kallo. 

    Kamar yanda ya saba bayan gama duk wata al’adar rayuwarsa yay shirin barci. Yaso yin kwanciyarsa anan amma zuciyarsa taƙi aminta da hakan. Ya fito a nutse yana kulle ƙofar. Sashen Fadwa ya fara nufa dan bazaiƙi sauke nauyin da ALLAH ya ɗaura masa ba komi sukai masa na laifi. Yayi mamakin samunta a falo bata kwanta ba. Sai dai hankalinta gaba ɗaya yana akan waya ne. Ta mugun shagala a yin editing video da zatai posting, wanda ɗauka ce mara daɗi, dan kuwa faɗa suke da wata mai suna Teema. Faɗan kuma ya samo asaline akan ita Teema ɗin ta ɗaura hoton Shareff a shafinta tana bin waƙar soyayya. Sai wasu a cikin followers ɗinta suka ɗakko videon suka dinga tagging Fadwa da gaba ɗaya a yau bata buɗe data ba sai da yammar nan, dan tashin hankalin Anaam ya saka a kwana biyun nan ta rage yin posting akai akai kamar da da arana takan ɗora videos sama da uku. Sima itace ta fara kiran Fadwa ta sanar mata lokacin fitowarta a sashen Shareff kenan. To shine fa tun ɗazu ɗin ake tafka rigima tsakanin Fadwa da mabiya bayanta su Sima. Itama Teema da nata magoya bayan sunama Fadwa izgilin Teema zata shigo itama ata uku kafin shekara ta ƙare. (????gsky naso ace kuje tiktok kuga rigimar nan guys????????).

   Tsaiwarta a kusa da ita ta sakata wani mugun zabura, daka ganta kasan ta firgita. Ta kife wayar akan kujera a daburce take masa sannu. Idanu ya tsira mata cike da mamaki matuƙa, dan baiga abin zabura ɗin ba anan. Ya maida dubansa ga wayar da take faman ja tana turawa ƙasan throw pillow, zuciyarsa ta ɗarsu a karo na biyu game da ganinta da ɗaukar hankalinta da waya keyi, sai dai na yau yafi ƙarfi dan ƙarara alamun rashin gaskiya sun bayyana akan fuskarta. Komai baice mata ba ya juya ya fice.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button