BABU SO HAUSA NOVEL

BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

data fara bashi, burinta kawai taga ya huce
daga fushinsa. Cikin ƙanƙanin lokaci ta gama
hautsina masa kwanyar kansa, tun yana binta
a salon jarumta harya fita a hayyacinsa ya
ɗauka wata hanya da ban da karatun da ya
kasance mai girma ga Anaam. A yanzu kam ita
ya nema gigitawa, yayinda shi tuni ya fita
hayyacinsa har baya gane ita ɗinfa ƙanwarsa
ce. Sunyi matuƙar shagala a farantama
junansu ring ɗin wayarsa ya shammacesu. Da
ƙyar Anaam ta iya janye jikinta dake rawa
gefe. Shima nashin rawar yake fiyema da tata,
sai dai jarumtar ƴan mazan ta ɓoye haka, ya
rimtse ido da ƙarfi ya sake buɗewa saboda
ganin mai kiran. Ko’a turu a kwantosa bai isa
ɗaga wayar nan ba, dan babu makawa sai
Daddy ya gane halin da yake a ciki. Haka ya
barta harta tsinke wani kiran ya ƙara shigowa.
Yanzun ma kasa ɗagawar yay har saida ta
yanke, da ƙyar ya samu iya ɗan dai-daita
kansa bayan wasu mintuna sannan yay kiran
Daddyn Back.
Koda Daddy yaji muryarsa a shaƙe a zatonsa
duk ɓacin rai ne, dan kuwa yasan wanene Share! idan yay fushi. “Ka sameni a gida yanzun nan kai da Fadwa”. Bai jira cewarsaba ya yanke kiran. Shima ɗin baice komaiba ya koma kwance tare da mirginawa jikin Anaam

data juya masa baya ya rungumota da ɗaura
kansa a gefen wuyanta yana shinshina, ga
sanyin tiles na ratsasu dan harya huda
sallayar tana iya jinsa a jikinta shima haka.. Jin saukar hanunsa a ƙirjinta tai saurin
riƙewa. “Yaya kirankafa Daddy yakeyi”. Iska ya ɗan hura mata cikin kunne da ture hanunta ya ɗaura a inda yay niyya tun farko. “Koratama kikeyi kenan?”.
“Eh mana, Daddy ba abin wasa bane ai,
umarninsa yana sama da muradanmu”. Sassanyan murmushi ya saki da sake
ƙanƙameta a jikinsa, a hankali ya furta Ina ƙaunarki da yawa”. Sosai tsigar jikinta ta yamutsa saboda yanda yay furucin a cikin wani irin wahalallen sauti. Taja numfashi mai kauri da cije gefen lips ɗinta sakamakon saukar kiss ɗinsa saman wuyanta. Bata iya ta ɗago ta kallesa ba harya fice daga ɗakin. Ta sauke sassanyar ajiyar zuciya da sake kananneɗe jikinta waje guda wani abu mai girma na tsikarar ƙasan zuciyarta….
A sashen Fadwa kan duk da yaji a ransa itace takai ƙararsa wajen su Daddy bai mata magana ba, umarnin kawai ta samesa a mota ya bata ya juya ya fita abinsa. Taja wasu mintuna kafin ta fito dan har ya kunna mota

ma.
Tafiya suke amma kowanne fuskarsa na gefe,
ita tana kallon mutane shi kuma titi har suka iso. baiyi mamakin samun Gwaggo Halima ba, Fadwa ta nufeta ta rungumeta tana sakin kuka. Lallashinta ta shigayi tana shafa bayanta da fuskarta wai tana neman tabon marin. Abin sai ya girmi kan kowa amma babu wanda yay magana sai Mommy ce taja tsaki da taɓe baki. Share! kam zama yay ƙasa a tsakkiyar ƙafafun Abie da Abba. Kansa a ƙasa batare daya kalla kowa ba ya gaishesu. Haka kawai yakejin tsananin kunyar Abie da Mommynsa fiye da kowa a wajen.
Abba da yaga mulmular da Gwaggo Halima kema Fadwa na neman yin yawa ya magana a kausashe. “K Fadwa tashi ki zauna da ƙyau bama son shashanci”.
Tashin tai zaune, sai a sannan kuma take
gaidasu. Iya su mazan kawai suka amsa.
mommy da Gwaggo babu wanda ya tanka.
Gwaggo Halima tai ƙaramar ƙwafa da ayyana
(Zanyi maganinku) a zuciyarta.. Abie ne ya
buɗe taron da addu’a, kafin ya maida
hankalinsa ga Share! cikin serious matuƙa. “Al-Mustapha miya haɗaka da matarka
harda mari? Bayan wannan ba ɗabi’ar dakaga wani a cikinmu nayi a gidan nan bane?”.

Ƙasa Share! ya ƙarayi da kansa, cikin
matuƙar girmamawa. “Kuyi haƙuri Abie nayi
kuskuren aikata hakan, sai dai saida na
umarceta ta tashi tabar inda nake dan bana
son yanke hukunci cikin fushi, amma taƙi yin
hakan har takai nayi marin”.
“Amma banda abinka Babana ai kai
babbane, da taƙi tashi sai kai ka tashi ka bata
waje tunda kasan baka iya controling kanka a
yanayin fushin. Su mata haƙuri ake dasu a
kowane hali, domin hangenka da nasu sam ba
ɗaya bane ba, sai dai sunada sauƙin sha’ani
kuma ba koda yaushe ake cizawa a kansu ba”. “Hakane Abie, insha ALLAHU hakan bazata
sake faruwa ba……”
“Tama sake faruwar mana. Wlhy da kaina zan
rama mata mara mutunci kawai. Kai yanzu
dan baka da kunya Share! har kanada hanun
ɗagawa ka daki Fadwa a gidanka?”. “Yaya Halima! Ya kamata kiyi shiru abi
komai a sannu”.
“Wane kuma sannu Abubakar, bayan kanaji
yana lallaɓashi saboda ba ƴarsa aka mara ba”. Murmushi Abie yay da girgiza kansa. Cikin
dattako da nutsuwar da kowa ya sansa da ita ya fuskanci Gwaggo Halima. “Ba haka bane Yaya Halima. Da Share! da Fadwa da Anaam duka su ɗin ƴaƴanmu ne, bazamu taɓa sakaci da cutuwar ɗayansu ba ai. Da kinyi haƙuri zan

kai inda kike buƙata nima ai”.
Baki ta taɓe da juya kai gefe. Nanma
Murmushin Abie ya saki kawai ya sake maida
hankali kan Share! da ransa ya ɓaci. “Babana
ina jinka miya haɗaku takai ga mari?”. “Ban taɓa fatan dan na samu matsala da
wata a cikinsu sai munzo gabanku ba. Amma
tunda ita tafi zaɓar hakan a koda yaushe fine.
Fita nai a gida tun safe ina wajen matsalar can
data taso a company, na dawo kawai na samu
ta cikamin sashe da ƙawayenta wai suna min
gyara. A yanda suke komai kai tsaye ya
tabbatar min ba yau ce rana ta farkon hakan
ba. Korarsu kawai nai na ƙyaleta domin ita
tasan bana son yanke hukunci cikin fushi,
amma saita biyoni bayan nace ta ƙyaleni a
yunƙurin farko da tai. Taya zata kawomin
wasu ƴan iska sashe, ta san adadin abubuwan
dana ajiye masu muhimmanci a ciki? Ko
bamma ajiye komaiba ita bazatai tunani da
hankalinta rashin dacewar kai wani can ɗin”. “Inafa zata san abinda ya dace tunda a nuna
mata barbaɗa magani shine kawai zaman aure”.
A harzuƙe Gwaggo Halima ta dubi Mommy
mai maganar. “Nafi wlhy ki iya bakinki domin
zai kaiki ya baroki allura ta tono galma”.
“Yo ta tono mana dan ubanta, abu mai sauƙi

bayan ta tono ita galmar ta turbuɗata cikin
ƙansa yanda ko mayen ƙarfe ƙaryarsa sake
ganinta”.
Aifa nan take falon ya harmutse da hayaniya
tsakanin Mommy da Gwaggo Halima. Mamaki al’ajab sukabi suka sanya Share! cikin madaukakin imani. Yau kuma aminai biyune kema juna tujara haka akan abinda suke ganin shine mafi ƙololuwar alkairi a garesu idan suka ƙulla. Kai duniya ina zaki kaimu ne haka?. Da ƙyar su Daddy suka samu sukai shiru. Gwaggo kam tayi kamar bata a falon tai muƙutt da cuno baki gaba ita a dole takai maƙurar ɓacin ran abinda su Mommyn ke aikatawa. Acan ƙasan ranta kuwa dariya taketa kwasa. Yanzu kam Abba ne ya amshe da zancen yana mai fuskantar Fadwa.
“K shashashar inace da zaki bama ƙawaye damar shiga ɗakin mijinki? Haka kikaga iyayenki na mana? Wace irin mace ce ke da baki kishin mijinki? Ai wannan jama kanki rainine ma wajen su ƙawayen naki da shi kansa mijinkin. To saurara ki jini, daga rana mai kama irin tayau, hakan ta sake faruwa ni da kaina zan hukuntaki sannan shima nasa ya hukuntaki tunda koba aure tsakaninku
Yayanki ne.. Kinaji na da ƙyau?”.
Hawaye ta ta share tana jinjina kanta. “Zan

kiyaye Abba insha ALLAHU. Amma Abba dama fa haushina yakeji, dan dama a kwanakin nan banda wulakantani babu abinda yakeyi saboda ya ƙara aure. Baya ganin kowa a gidan sai ita ƴar gwal…..”
“Shiyyasa kuka dage boka da matsubbata ke
da uwarki domin sabautamin ɗa. Su Malika na
kawo miki barbaɗe-barbaɗe kina faman zuba
masa dare da rana. To wlhy babu lallai babu
dole tun kan ai nisa sai ya datse igiyar auren
tunda bake kaɗaice mace ba a duniya……” “Dan ALLAH Nafisa idan baki sakashi ya
datse igiyar aurensu ba baki cika uwarsa ba,
kuma shi din bai haifuba a cikinki…” “Haka kikace?”.
“Eh na faɗa. bandama ƙaddara mi Fadwa
zatai da wani Share! can. Ko dama kun ƙulla
a haɗasu aure dan ku dinga maidamin yarinya
baiwarku”.
“Hahaha yo baiwa kuma ta nawa Halima.
Sai dai wata kuma dan ita kam ta riga ta gama zama labari”.
Ƙara hargitsewa falon yay, da ƙyar yanzu kam Abie da Abba suka sakasu yin shiru, dan Daddy dai ya mugun shaƙa zuciyarsa har wani zallo takeyi, gata tokare a maƙoshinsa kamar yay amanta ya huta………….
End of book

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button