BABU SO COMPLETE HAUSA NOVEL

Anaam da bata san da dawowarsa ba ta fito a toilet daga yin alwalar sallar magrib ya shigo. Sannu da zuwa ta masa. Idanunsa kafe a kanta ya amsa mata. Sosai itama tata kwalliyar ta wuce da nasa imanin. Yaji daɗi har cikin ransa ganin yanzu tana kwalliya. Shiyyasa ya hana Aysha wucewa dan yasan koba komai zata taimakama Anaam ɗin da abubuwa masu yawa da bata gama sani ba a irin rayuwar Nigeria.
“Haka ake tarbar miji dama?”.
“Kai yaya alwalafa nayi”. Ta faɗa murya a karye. Murmushi ya saki yana matsota. Ta matsa da sauri zata koma toilet. “Nidai ALLAH karka karya mun alwala”. Dariya yayi da yin ƴar ƙwafa ya juya ya fita. Itama saita sauke ajiyar zuciya dan ta san kaɗan daga aikinsa yace zai shanye jambakin dake a lips ɗinta.
Bai dawo gidan ba sai bayan sallar isha'i. Kai tsaye kuma sashinsa ya nufa, inda ya iske har an shirya abinci a dining. A falon ya zauna yana sauke numfashi da ƙoƙarin kunna television, so yake ya kauda duk wani damuwarsa domin more wannan daren. Kusan mintuna sha biyar da zamansa babu Anaam babu labarinta. Dan haka ya dauka waya yay kiranta. “An barni ni kaɗai kamar maraya”.
Murmushi tayi da har yaji sautinsa a kunensa. “Immhum ni ai bansan ka dawo bane ba fa”.
“Okay, ai yanzu kin sani”.
Min tuna kusan bawai tsakani sai gata ta shigo, tun kan ta iso ƙamshinta ya karaso. ya rasa a matan nasa wacce tafi wata iya gayune. Duk randa sukejin abin arziƙi susutashi sukeyi gaba ɗaya. Ta bayan kujerar ta tsaya, tare da ranƙwafowa kansa ta manna masa kiss a wuyansa. Numfashi yaja mai yalwa tare da fesarwa. Ya kamo hanunta ya zagayo da ita ya zaunar a cinyarsa. “Irin wannan wanka ai sai ki sakani manta kaina autar mata”.
Murmushi tai da ɗan tabe baki, “Ban san daɗin baki ni dai Yaya”.
“Kinfi ƙarfin daɗin baki ai a wajena. Duk abinda bakina ya furta a kanki shine ai nahin gaskiyar zuciyata”.
Sosai taji daɗi har cikin ranta. Amma dai batace komai ba sai murmushi kawai da taɗanyi. “Yau dai lipstick ɗin nan nawane ko?”.
“A’a”.
“Ashe zan miki kuka”.
Dariya ta sanya tana mai lafewa a jikinsa. “Oh oh ya kaga Yaya ana kuka”.
Murmushi yayi mai faɗi da lakace hancinta. “Wato harma hasasowa kikeyi ko”.
“Sosai ma”.
“Uhhyum mugunta.com”. Yay maganar da kaima lips nata kiss. Bai bari ta shaƙi numfashi ba ya maida lips ɗin nasa kan nata again. Sai dai a yanzu salon dabanne dana farko, dan sai da ya shanye lipstick ɗin tas hankalinsa ya ƙwanta. Lamo tai a jikinsa tana sauke ajiyar zuciya a hankali. “Tsadar tsada ke ta musamman ce”.
Muryarta a dashe tace, “Ai kaima ɗin na musamman ne”.
Ido yake son su haɗa amma taƙi yarda. “Please ki kalla cikin idona ki faɗa Noorie”.
Murmushi tai da juyowa kamar zata kallesan, sai ta mike zumbur daga jikinsa. Kamota yay yunƙurin yi ta zille tana dariya. “Biyu kenan fa, idan kika bari na kamaki zakiji jiki”. Gwalo ta masa da nufar dining. Ya murmusa cikin jinjina kai.
Waya ya ɗauka yay kiran Fadwa. Cikin murya ƙasa-kasa yace, “Babie kizo muyi dinner”.
“Uhm-uhm”. Ta faɗa a shagwaɓe.
Ɗan kallon Anaam yay, ganin hankalinta ba kansa yake ba ya sake ƴin ƙasa da muryar cikin lallashi. “Why”.
“Nifa bana jin cin komai”.
“Idan kika bari nazo da kaina akwai hukunci kenan”.
Dariya tayi da ga can. “Naji zanzo”. Shima sai yay murmushi da faɗin “Matsoraciya”.
Juyowar Anaam dai-dai yana ajiye wayar. batare data fahimci mi yayi ba ta ɗaga masa yatsu biyu. “Hy Yaya abinci na jiranka”.
Fuskarsa ya dan marairaice. “Kin yarda zaki bani da kanki?”.
Ɗan jimm tai na tunani, sai kuma ta kaɗa kanta alamar eh.
“This is for you my Noorie”.
Ya faɗa yana mai kissing hanunsa ya hura mata.
Dariyar da tafi kama data mugunta ta sakar masa. Ta tare kiss ɗin tana mai lumshe idanu da mannawa saitin zuciyrta. Rungumeta yay sannan ya kai zaune a kujer data ja masa baya. Dai-dai nan Fadwa ta shigo. Koda suka kalla juna ita da Anaam sai kowa ya watsar da ɗan uwansa. Sai da ta karaso ta zaunane Anaam ɗin tace, “Barka da yamma”. A takaice itama Fadwa ta amsa da “Barka”. Sai kuma ta ɗan saci kallon Shareff ta sakar masa murmushi. Murtani ya mayar mata ya ɗauke kansa.
Anaam daba lura tai da su ba tana ta ƙoƙarin zubama kanta abinci, koda ta ɗago sai suka haɗa ido itama da shi. Murmushi suka sakarma juna. Nanma ya kauda kansa batare da Fadwa ta gani ba dan itama ta maida hankalinta ga zuba nata abincinne. Yau ne kuma karon farko da Anaam ta fara girki a gidan, duk da dai tayisane da taimakon Aysha dan bata iya girke-girken Nigeria ba sai ƙalilan a ciki. Saukinma zuwa yanzu ta iya cin abubuwa da yawa ba kamar farkon zuwanta ba.
Gaba ɗayansu cin abincin suke cike da nishaɗi, dan kowacce ta samu irin farin cikin da take buƙata daga mijinta. Wanda a nata wautan gani take itace ɗaya ƙwalli ƙwal a zuciyarsa. Shiko cin abincin yake wani yanki na hankalinsa naga umarnin su Mommy, sai dai wani yanki najin matuƙar farin cikin ganin farin cikin matan nasa da har kowacce ta kasa ɓoyewa. Koda suka kammala Fadwa bata wani jimaba tare da su tai musu sai da safe ta wuce zuciyarta cike da kishin mijinta. Anaam kuwa ta shiga tattare kayan waje guda. Falo suka koma ita dashi, ya zauna a 3sitter tare da jawota jikinsa....
Sai da ta bari sun shagala da kallo yana mai cakuɗata a yanda yaso sannan taja numfashi. “Yaya gobe zan koma gun aiki ko?”.
Tamkar saukar aradu yaji maganar amma sai ya danne. Yay shiru kamar bai jita ba sai da ta ƙara maimaita masa tana ɗagowa ta kallesa. Shanyayyun idanunsa ya zuba mata na wasu sakanni. sai kuma ya dan lumashe da kaɗa mata kai kawai. Ta sauke ajiyar zuciya tana mai hamdala ga UBANGIJI. “Nagode Yaya wlhy na zata zakace a'a”.
“Humm”.
Kawai yace mata.
Tasan ya shaƙa dan haka tai shiru, ita dai tunda ya yarda zata koma ai Alhamdulillahi koma mi zaiyi mai sauƙine kuma. Saida ya kammala kallon labarai sannan suka mike. Ta fita domin zuwa tai shirin barci shi kuma ya nufi bedroom ɗinsa bayan ya bata umarnin idan zata dawo tazo masa lipton. Ya mata hakane dan kartai tunanin ƙin dawowar. Kamarko ya sani batai niyyar dawowa ba. Amma babu yanda ta iya kodan son komawarta aiki salin alin tabi umarnin nasa.
Sai da ta shafe kusan mintuna talatin sannan ta dawo cikin zumbulelen hijjab har kasa da cup na lipton. Rashin ganinsa a falo ya sata nufar bedroom ɗinsa kai tsaye. A bakin gado ta samesa yana haɗa wasu takardu da laptap ɗinsa alamar kayan zuwa office yake tattarawa. Ta ajiye cup din a bedside drawer dake gefensa.
“Jazakallahu khairan”.
Cikin jin daɗi ta amsa da “Amin ngd”.
“Kin rufe falon ko?”.
Hakan ya bata tabbacin nan ɗin zata kwana dai, dan haka ta girgiza masa kanta.
“Okay ki rufe kawai”.
Nan din ma kanta kawai ta jinjina cike da tsoro. Sai dai babu yanda zatai dole taje ta rufe ɗin ta dawo. Ta samesa ya fara shan shayinsa. Ya nuna mata gadon da fadin, “Bisamillah ki kwanta gobe akwai fitar safe. In kuma kikace zaki mun irin lattin da kike mun a gida zan tafi na barki ne”.
Baki ta ɗan tura masa batare da tace komai ba. Hijjab ɗinta ta cire ta hau gadon ta kwanta tana mai addu’ar ALLAH yasa kar yace yana bukatar komai. Dan duk da zaren ɗinkin da kansa ya fita saboda yawan shiga ruwan zafi da takeyi ba ƙaramin tsoro da fargaba take shigaba a duk lokacin data tuna za’a iya sake ratsa wajen again. Sauri-sauri tai addu’a ta gyara kwanciya da rokon ALLAH zuwan barci kafin ya kammala shan shayin nasa………..✍
????Abun dariya abun tausai????
ZAFAFA BIYAR
INAYAH
MamuhGee
GURBIN IDO
Safiya Huguma
SANADIN LABARINA
Hafsat Rano
FARHATAL QALB
(Miss Xoxo)
BABU SO
Billyn Abdul
Littafi daya 300
Littafi biyu 400
Littafi uku 500
Littafi hudu 700
Littafi biyar 1k
YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS????????????????????????
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902
IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA????
09134848107
ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????
[11/25, 10:30 AM] Hajiya Qarama: BABU SO
Chapter: 76
……….Sun iso gidan biki inda yake tanƙam da jama’a. Dan maza nata shirin wucewa massallaci saboda an haɗe ɗaurin auren waje guda har na Khaleel domin sauƙaƙawa mutane. Cikin takama da isa Gwaggo Halima da Fadwa suka shigo cikin gidan, anan fa kallo ya koma sama dan ko makaho ya shafa yasan naira ta zauna. Kai tsaye sashen Mom suka nufa dan ko kallon sashen Mommy a yanzu Gwaggo Halima batayi a gidan balle Gwaggo. Mom da babu ruwanta dama tai musu tarba ta mutuntawa duk da kuwa tunda aka tsira bikin sai yau kowa yaga idon Gwaggo Halima a gidan. Tadai aikoma Abba da Daddy Da mom gudun mawa. Shi kansa Khaleel mota ta danƙara masa duk dan cusama Mommy haushi. Tuni ƴar rahoton Gwaggo taje ta sanar mata isowar su Fadwan. Tai murmushi mai alamomi da yawa tana mai miƙewa, cikin toilet ɗinta ta shiga, duk da kuwa ta hana kowa shiga mata bedroom dama. Amma duk da haka bata yarda ta tsaya iya bedroom tai wayarba. Daga can aka ɗaga, fuskarta ƙawace da murmushi cikin bada umarni kuma tace, “Ki tabbatar da an ɗaura aure ki tura masa, dan ina son maimakon su iso gida da labarin farin cikin an gama ɗaurin aure lafiya, labarin ya canja”. Batako jira amsa ba ta kashe wayar gaba ɗaya.