BABU SO HAUSA NOVEL

BARIKI NA FITO 1 & 2

Haulat ganin hjy habiba nata surfa bala’i yasa ta tashi ta nufeta tare da saka bakinta cikin na hjy habiba ta Fara tsotsa sunyi wajan minti biyar sannan haulat ta cire bakinta cikin na hjy habiba tace mumy wannan fad’an fah haka?

Hjy habiba data fara tsumuwa tace Wlh baby raina ne ya baci ta cika kwashe kwashe, tace muje d’aki daughter sha’awar ki nake Sosai haulat tace muje mum tun daka nan suka fara she’ke ayarsu.


Habib ne bakin titi daka gani yana jiran wasu ne, sai faman tabe fuska yake da baki a dan dole shiga mace, yana nan tsaye yaga jerin motoci har biyar kobai tambaya ba yasan Yarima Aliyu ne, gyara tsayuwa yayi da kyau yana d’an murmushi, dai dai inda habib din yake motar da Yarima Aliyu ke ciki ta tsaya, glass din motar aka bud’e driver din Yarima ya gani d’aure fuska habib yayi tare da fad’in mai ba’kin hali.

driver din murmushi kawai yayi tare da fad’in kaje motar gaba danka nuna mana gidan.

Habib bai kuma cewa komai ba yayi gaba aka bud’e Mai motar ya shiga, dai dai kofar wani Gida suka karasa gidan ginin kasa kana ganin gidan kasan basu da karfi.

Idon Yarima ya sauka a kofar gidan, gaba d’aya yaji jikinshi yayi sanyi da ganin gidan, tare da fad’in my princess bata dace da zama a nan ba, Sosai yaji tausayinta tare da kara Sonta.

Bayan sun tsaya habib ya fita ya nufi motar Yarima inda driver din Yarima ya fito ya bud’e Mai, habib shiga cikin motar yayi a gaba ya zauna dan Yarima yana baya, kallon Yarima yayi yana wani murmushi tare da fad’in Barka da zuwa Bari inje in kirata.

Yarima amsawa yayi da yauwa, da fatan kana lafiya?

Habib har wani fari yake da ido yace eh ranka ya dad’e, tare da bud’e motar ya fita, kallon driver din Yarima dake tsaye yayi ya banka mai harara tare da fad’in munafuki.

Yarima Aliyu yana mota yana kallonsu ya rasa mai yasa baya son habib, kodan yana hulda da wacce yake so ne oho, kuma ya tabbata badan uwanta bane….

Yana cikin wannan tunanin ya hangota ta fito ita da habib cikin hijab, idon Yarima na kanta yana kallon kyakyawan fuskanta duk da batai makeup ba dan dama ita ba ma’abociyar yin kwalliya bace, Yarima Aliyu kallonta yake har suka karaso inda yake

habib ya bud’e mata motar alaman ta shiga.

dan cijewa tayi alaman bazata iya shiga ciki ba.

Habib yace Zainab kiyi hakuri ki shiga yanzu kawu zai dawo, kuma Kinga ba mutunci bane ku tsaya a waje koh?

Shiga tayi ta zauna gabanta taji ya fad’i da taga Yarima, wani irin mugun kwarjini taga yayi mata, zuciyarta ta Fara buga mata da karfi, duk kallonshi da takeyi ta gefen ido takeyi…..

Yarima Aliyu yace tsarki ya tabbata ga Allah da yayi wannan halittar.

Kanta tayi kasa dashi tana wasa da y’an yatsun hannunta alaman kunya, tace Barka da zuwa, ina wuni.

Yarima idonshi na kanta yana kallon bakinta yanda take magana cikin nutsuwa yace lafiya kalau my princess, d’an shuru yayi yana kallonta wani irin sonta yaji yana fusganshi… A hankali ya kira sunanta da zainab

D’ago dakai tayi suka had’a ido da sauri tayi kasa da kanta.

Murmushi yayi tare da fad’i cikin ranshi tana da kunya Sosai, yace Zainab da farko dai sunana Aliyu mu biyar ne wajan dad dina nine namiji guda d’aya da iyayena keda shi, zainab na dad’e Ina sonki tun ina secondary school….

Da sauri ta d’ago ta kalleshi domin abunda yace ya bata mamaki Sosai, Anya Yarima bai sanni ba kuwa?….

Katse mata tunani yayi da fadin tun ina skul nake ganinki cikin mafarkina tun ban d’aukan abun da muhimmanci harna Fara d’auka har takai ta kawo na Fara zana hotan jikin ki, dan ban taba ganin Fuskanki ba, domin kina zuwa min cikin duhu ko kuma kizo min sanye da nikabi, danna wayanshi yayi yace kalla ki gani…..

D’ago dakai tayi tare da kallon wayan gabanta taji ya fad’i nuna mata hotan yake amma duk babu fuskanta akai sannan duk colour din hijab din duk tana dasu, harda wani farin hijab Wanda take dashi Mai leshi a wajan kan, tana kallo tana mamaki ya fara nuna mata Wanda akwai fuskanta akai, da sauri ta kalleshi ganin idonshi na kanta yasa tayi kasa dakai sannan tace duka duk Kalan hijjabai nane, abun yaban mamaki.

Yarima yace Zainab Nayi imani had’uwa na dake had’in Allah ne, tun sanda nake mafarkin ki nake ta fama da sonki tare da burin ganinki, sau d’aya na ganki a bakin hanya na tabbata Kece domin da jikin ki na ganeki.

Bariki tace hakane Abun yaban mamaki

Yarima Aliyu yace ba’a mamaki da ikon Allah Zainab, ina son in San koke wacece.

Bariki shuru tayi ga gabanta dake ta faman fad’i…… Muje zuwa muji bariki gaskiya zata fad’ama Yarima Aliyu ko akasin haka……

~MARYAM OBAM~

BARIKI NA FITO

            *BY*

MARYAM ALHASSAN DAN’IYA
(Maryam Obam)

https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/

WWW.Maryamobamnovels.com

Wattpad @maryam-obam

Instagram@maryam_obam

MARUBUCIYAR
1)FATIMA ZARAH
2)DUKIYAR MARAYA
3)BA’KIN ALJANI
4)BANDA ZABI
5)AMINIYA TACE
6)KISSA KO MAKIRCI
7)SAINA AURESHI
8)SUHAILAT
9)TAMBARIN TALAKA
10)JAWAHEER
11)MIYE ILLAR Y’AY’A MATA
AND NOW…. BARIKI NA FITO

DEDICATED THIS PAGE TO….
HAJIYA NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO

                 *PAGE 15*

Jin tayi shuru yasa Yarima Aliyu fad’in, lafiya kuwa?

‘kago murmushi tayi tare da fad’in sunana Zainab musa haifaffiyar garin kaduna, gidan mu yana u/kanawa mahaifina yana sana’ar rini, duk da bashi da karfi ya bamu tarbiya dai dai gwargwado sannan har yau yana kokari wajan bamu tarbiya, mahaifina Talaka ne amma yana da Kawa zuci, zaiyi abunda wani mai kud’in ma bazai iyayi ba, mu biyu iyayena suka mallaka sai yasa duk wani burinsu da kudirunsu yake kammu nida dan uwana, wajan ganin mun sami rayuwa mai in ganci kuma Alhmdlh tunda yau saukan mu ranan sati mai zuwa insha Allah zan haddace al’qur’ani Mai girma, shi yayana mai suna Saddiq ya dad’e da sauke al’qur’ani, sannan fannin boko inada matakin secondary domin mahaifina bazai Bari Inci gaba da karatu a gidansa ba sai gidan mijina, wannan dai shine labari na.

Yarima murmushi yayi sannan yace y’an Zaria ne kenan ku?

Gabanta taji ya fad’i dan in tace su y’an Zaria ne toh a wace anguwan? Kai a’a da sauri tace a’a mahaifina dan Kano ne domin a can aka haifeshi, tun yana dan shekara Goma sha biyu ya dawo kaduna shida iyayensa har Allah ya musu rasuwa inda mahaifina ya fara buga buga har yakai da yayi aure aka haifemu a garin kaduna, toh Kaga inda aka haifa mutum toh nan ne garinsa.

Murmushi Yarima Aliyu yayi tare da fad’in hakane,. Yace Zainab naji dad’i Sosai da naji tariyin ki, babban abunda ya kara burgeni daya kasance princess dita maddaciyan al’qur’ani ce, Allah yasa ya amfana al’umma

Tace Allahumma Ameen Yarima na….. Shuru tayi domin jin Kalman daya fito daka bakinta….

Yarima da sauri ya kalleta domin irin Sunan take kiranshi cikin mafarkin shi, yace Zainab plz say it again

Jin tayi shuru kanta na kasa yasa ya kamo hannunta da take wasa dashi ya ri’ke hannun duka biyu tare da fad’in plz say it again plz.

Ri’ke mata hannu da yayi yasa komai dake jikinta ya tsaya wannan ne karo na farko da namiji ya taba, taba mata jiki taji wani abu, danko mazan da take iskanci dasu bawai tana jin wani abu bane kawai tana dai yine, amma shi Yarima hannunta ya ri’ke yasa tana jin wani abu tun daka tsakiyar kanta Kar kasan kafanta, kokarin Fara Jan hannunta tayi daka nashi, amma ta kasa.

Murmushi yayi tare da fad’in sai kin fad’a min abunda nace zan sake ki, a hankali tace Yarima na, ido ya lumshe cikin jin dad’i tare da wani kara jin Sonta har cikin ranshi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button