BABU SO HAUSA NOVEL

BARIKI NA FITO 1 & 2

Bariki tace hjyta adai yi hakuri

Hjy babba yace ya wuce yana tabe baki

Bariki tace godiya nake tare dayin gaba ta nufi d’akinta…..

Tana cikin had’a kaya haulat tazo, ganin bariki nata aikin had’a kaya yasa haulat tace badai bikin yazo ba??

Bariki tace eh Wlh, Kinga wata biyu aka sa, gwara in fara had’a kaya, in kyautar dana kyautar wa inbar na Bari

Haulat tace hakane, ni har yanzu ba’a fad’amin dan wani gari bane ko sunanshi

Bariki tace saurin Mai kike ki jira koma Waye zaki gansa in lokaci yayi

Haulat tace Allah ya kaimu, nan ta Fara taya bariki had’a kaya, haulat ta d’auko wata Leda nan kayan suka zube dan ledan ya fashe, Aiko ayabar roba suka fito…… Haulat d’auka ta farayi taga har guda biyar tace bariki dama kina dasu?? Ah ba banza ba kika daina harka da maza ba, ashe kina da abunda yake d’ibe miki sha’awa

Bariki kai ta girgiza tare da cema haulat ki d’auka duka na baki, ni ban taba amfani dashi ba, yanda aka bansu haka na ajiyesu dan banda abunda za suyi min

Haulat ta dinga godiya tare da fad’in amma wanda ya baki yasan kina son babban ayaba tunda harya baki….

Bariki tace Alh madu Yaban dan iskan tsoho, ci gaba da had’a kayanta tayi harta gama taba haulat kyautan kayanta da yawa.

Haulat tana ta mata godiya duk yanda haulat taso bariki ta fad’a mata wa zata aura amma bariki ta’ki Tadai fad’a mata dan gidan sarauta ne, abunda kawai bariki ta fad’a mata kenan……….

A kwana a tashi babu wuya wajan uban giji, bariki ta gama istabra’i, sannan iyayenta sunyi aure, mai martaba ya siya musu Gida Mai kyau 4bedroom a u/kanawa inda anan iyayen nata na Bariki suka tare, sannan bariki tace ta bar musu gidan halak malak, domin suna Mata aiki yanda ya dace, bariki ta K’ara kyau da haske domin ana mata gyaran jiki Sosai…..

Yau bikin bariki da Yarima baifi kwana Goma ba, Yarima yanzu ba kullum yake zuwa wajanta ba, domin aiki sunyi mishi yawa, ga hidiman biki, gana asibiti ga fitinar zinatu, abubuwa sunyi mishi yawa Sosai….. Yana office ya Gama duba patient yaji yana bukatar ganin Zainab dinshi dan haka ya tashi ya nufi gidansu, wanda yanzu in yazo ciki yake shiga dan akwai falon ba’ki a gidan, kiran Zainab din yayi yace ta sameshi a waje basai y’a shigo ba.

Fita tayi inda ta sameshi a mota ta bud’e ta shiga tare da gaidashi

Mai makon ya amsa sai yace Kai my princess Kinga yanda kike K’ara kyau kuwa?? Gskya ana gyaramin ke dakyau,

Murmushi tayi cikin jin kunya sannan tace Kai Yarima wani kyau nake karawa?? Tayi maganan a shagwabance

Yace Zona nuna miki tare da janyota jikinshi, wani irin kamshi ne ya daki hancinshi Wanda tunda ta shigo yake ji, amma daya janyota jikinshi sai yaji kamshin ya fito Sosai, gaba d’aya yaji jikinshi ya fara weak domin kamshin turaren yasa jikinshi ya fara yin sanyi….. Itama ta gefenta wani iri take ji domin maganin da ake bata ya tsumata Tana matukar bukatar namiji amma babu yanda ta iya dole sai mijinta Bayan tayi aure, gashi yanzu Yarima yana son tada mata bala’i…. Yarima Aliyu hura mata iska yayi a fuska da sauri ta d’ago suka had’a ido peck yakai mata a goshi tare da furta I love you my princess

Da sauri ta lumshe ido

Ganin haka yasa Yarima ya kura mata ido yana kallonta tare dajin wani irin mugun sonta na K’ara shiganshi…. Jin shuru yasa ta bud’e ido a hankali idonta ya sauka cikin kwayar idonshi da yake kallon nata idon….. Dukansu wani irin yanayi mai wuyan misaltuwa suka shiga……. Karan wayar Yarima yasa ya saketa ta tashi da sauri daka jikin nashi ta koma ta zauna dakyau….. Daukan wayan yayi ya duba, ganin mai kiran yasa bai d’auka ba, zinatu ce……

Bariki kam gaba d’aya ta birkice, dan dan tabata dinnan da Yarima yayi har tana jin zuban ruwa a cikin pant dinta, lallai ya kamata Yarima ya rage zuwa, ko kuma ya daina tabata…. Domin Indai hakan zaici gaba da faruwa zata sha wuya, ido ta lumshe tasan ba komai yake sata yawan sha’awa ba sai maganin da take sha, wacce y’ar Sokoto take bata…..

Yarima ne ya Katse Mata tunani da fad’in, my princess zan gudu, bata sim yayi guda d’aya tare da cewa ta cire nata, baya son ta kara amfani dashi…..

Amsa tayi, tace toh dama tun tuni take da burin canza layi, amma tana tsoran Kar Yarima yace Mai yasa, yanzu tunda ya kawo mata, hankali kwance, sannan ya bata check na 3mil yace a K’ara gyaran jiki domin naga suna gyaramin ke dakyau……

Tace Yarima kafa ban kud’i cikin kwanakin nan, kaban a kalla wajan 7mil kace in siya kayan akwati, kuma gashi kace May be gidanku su Kawo nasu gobe ko jibi, kai kamin gashi gidanku zasu kawo, ga kud’i kuma kana karamin, gskya abun yayi yawa, ka barshi…..

Bata fuska yayi tare da fad’in in kin ciro kud’in ki zubar a bola tare da ajiye mata check din a jiki…..

Ganin yanda ya bata fuska, yasa tace Yarima kayi hakuri, wlh ba haka bane, naga hidimar tayi yawa ne Sosai, Kaga y……

Yace enough, komai na miki, kin can Canta inyi miki shi, and karki manta am your husband to be, waya kamata inyi ma Abu Inba keba?? In my life ban taba kyauta ko wani abuba a nuna ba’a soba sai ke..

Da sauri tace kayi hakuri plz na tuba, ngd Allah ya saka da alkhairi….

Jin ta fad’i haka yasa yaji dad’i….. Ba komai yasa Yarima ya bata wannan kud’in ba, sai sanin da yayi ba masu hali bane su, and y’an uwanshi zasu Kawo akwati, ance ana bada kud’i, sai yasa ya bata wannan kud’in dan iyayenta su bada tukwici… Ajiyan zuciya yayi tare da fad’in zan tafi sai munyi waya,

Tace OK

Yace kin dai ki zuwa kiga gidanki koh?

Tace Yarima saurin Mai kakeyi?? Ka Bari har a kaini mana

Murmushi yayi domin kin amincewanta yasa ya kara yarda damai tarbiya da kuma kamun kai zai aura, sabanin matan yanzu da suka lalace suke ganin haka shine wayewa, tab kunji Yarima shi’a dole zai aura ustaziya????

Sallama ya Mata sannan ya wuce……

Bariki gida ta shiga jiki a sanyaye lallai Yarima yana matukar sonta da yawa, hawaye ne ya gangaro daka idonta, tare da tausayin kanta yanda zai dauketa in yasan ko ita wacece……

Anata shirin biki musamman ta gefen ango, domin dai ita amarya rufa rufa take ma auran ba kowa bane ya sani, sai dai zargi da wasu sukeyi……

Ranan da za’a kawo akwati saida bariki da habib sukai hayan mata guda biyar, An kawo akwati guda ishirin da hud’u, dozen biyu kenan, kaya ne makil na Kece raini masu tsadan gaske….. Ganin yawan kayan yasa umman bariki taga 1mil yayi kad’an dan haka ta sami bariki dake boye cikin wani d’aki, tace ya kamata a K’ara kud’in nan Kinga uban kayan kuwa? Bariki kara 1mil tayi ya zama 2mil, nan aka basu kud’in tukwici, tare da abun ciye ciye da aka tanadar musu, bayan sun fito sis din Yarima Fatima tace Kai ance yarinyar talakawa ne amma har da bata 2mil, Aini ban d’auka zasu bada koda dubu d’ari ba, dariya sukayi sannan aka canza firan,

Bayan sun tafi bariki ta fito tana kallon kayan, itama Abun ya bata mamaki ganin kaya masu uban yawa da tsadan gaske, yanzu ga akwati ishirin da hudu, gashi kudin da Yarima ya bata itama ta siya guda sha biyu, duka talatin da shida…..

Ummanta ta bariki tace Kai gskya ki gode Allah y’ar nan, Yaron nan yana sonki Sosai, ji uban kaya sannan kayan d’aki yace baya bukatar komai, kai Kinji dad’i wlh

Bariki murmushi kawai tayi jiki a sanyaye, domin sai yanzu ta Fara jin tsoran abunda take kullawa na auren bariki, da tana ganin abun kaman wasa, amma tunda har taga akwati yau an kawo ta tabbatar Abun dagaske ne, d’aki tayi ta Fara rusgan kuka tare da fargaban abunda zai biyo baya….. Hmmm Allah ya kyauta dai zan iya cewa

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button