BABU SO HAUSA NOVEL

BARIKI NA FITO 1 & 2

MASARAUTAR ZARIA

Kwance yake a makeken gadonshi Wanda kallo d’aya zaka ma gadon ka gane an kashe naira wajan had’ashi, an kashe millions of naira wajan kayan gyaran d’akin domin ya had’u sai juyi yake akan gadon daka gani mafarki yakeyi, tashi yayi a furgice duk yayi zufa duk da kuwa akwai AC a d’akin, ruwa ya d’auko yasha tare da ajiyan zuciya ya rasa mai yasa yake mafarkin yarinyar nan a kullum ya kwanta bacci Wanda mafarkin da yayi yau ya ganta tana fad’in yarima na Kai nake jira kullum dan Allah kazo ka fitar dani daka cikin wannan ‘kangin kokarin matsawa yayi kusa da ita dan yaga fuskanta amma Kafin yakai inda take ta ruga da gudu, ya fara binta kenan wata mota tazo da gudu saura kad’an ta bigeta shine ya farka, abunda yake bashi mamaki shine kullum yana mafarkin yarinyar amma bai taba ganin fuskanta ba, yana yawan ganin yarinyar cikin hijab da nikaf, wani zubin kuma cikin duhu, abun yana damunshi amma koma dai miye dole ya sami limam ya mishi bayani abunda yake faruwa…. Waye wannan guy din ku biyoni domin jin ko Waye

~MARYAM OBAM~
BARIKI NA FITO

            *BY*

MARYAM ALHASSAN DAN’IYA
(Maryam Obam)

https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/

WWW.Maryamobamnovels.com

Wattpad @maryam-obam

Instagram@maryam_obam

MARUBUCIYAR
1)FATIMA ZARAH
2)DUKIYAR MARAYA
3)BA’KIN ALJANI
4)BANDA ZABI
5)AMINIYA TACE
6)KISSA KO MAKIRCI
7)SAINA AURESHI
8)SUHAILAT
9)TAMBARIN TALAKA
10)JAWAHEER
11)MIYE ILLAR Y’AY’A MATA
AND NOW…. BARIKI NA FITO

DEDICATED THIS PAGE TO….
NAFISA MRS DAN MALIKIN KAWO

                 *PAGE 2*

Yarima Aliyu d’ane d’aya tilo wajan Mai martaba Alh Murtala, sai mahaifiyarshi Khadija, bawai Ina nufin shine kawai d’ansa ba a’a shine d’a namiji kwaya d’aya damai martaba yake dashi, yana da y’an uwa Mata su biyar, akwai rukayya tana aure a garin katsina, sai salamatu Tana aure a garin adamawa, sai Fatima wacce take aure a garin kaduna, sai Aliyu shine d’a na hudu wajan Mai martaba, sai aysha wacce take aure a garin abuja, sai Hafsat wacce ita bata da aure domin bata dad’e da zana waec ba, Aliyu dogo ne amma ba Sosai ba sannan kuma ba gajere ba, yana da tsawo dai dai misali, shiba fari ba kuma ba ba’ki ba, saboda hutu fatar jikinshi har walkiya takeyi tana wani shinning da she’ki, yana da faffadan kirji ga idonshi fari Sol kaman madara yana da kyau na kin karawa, Aliyu yayi bala’in had’uwa ya wuce tunanin duk mai karatu, mahaifinshi duk yafi sonshi cikin y’ay’ansa kodan shi d’aya ne d’a namiji oho, Aliyu bai cika son magana ba gaba d’aya rayuwanshi a kasar waje yayi, a nan yayi karatu tun daka primary har zuwa degree dinshi inda ya karanci doctor a fannin mata, sai yasa yake kallon ko wace mace a d’age dan yasan komai dake jikin mace sai yasa har yau baiyi aure ba duk da mahaifinshi Ya bashi kashedi na karshe akan yaje katsina yaga y’ar sarkin katsina su daidaita da y’ar sarkin katsina, domin wajan sau uku ana zaba mishi mata yace baya so, Aliyu yana da bala’in kishi Sosai tun yana karami koda kaya aka siya Mai yaga wani mai irinshi Toh har abada bai kara saka kayan, abun ya had’e Mai biyu ga kishi ga jinin sarauta Wanda yasa mutane suke ganin yana da wulakanci, sannan magana bai dameshi ba, in kuka ga yana magana harda dariya toh yana wajan mum dinshi ko Mai martaba ko y’an uwanshi, amma inka ganshi zaka d’auka baya dariya, Aliyu yana da kwarjini Sosai Mata da yawa suna burin samunshi a matsayin miji domin guy din ya had’u Sosai.

Aliyu tunani yaita yi akan wannan mafarkin da yakeyi, tun yana secondary school yake wannan mafarkin, tun yarinyar bata girma Sosai ba yake ganinta sai dai har yau bai taba ganin fuskanta ba, abun yana matukar damunshi, har Abun yakai ya kawo ya fara zana yarinyar jikinta da suranta Mai kyau da diban hankali sai dai fuskanta ne dabai gani ba, ido ya lumshe tare da tashi ya shiga toilet, shower ya saki akanshi ya dad’e ruwa na dukanshi Kafin yayi wanka ya fito, kimtsawa yayi cikin kaftan tare da malin malin yasa rawaninshi domin zashi wajan Mai martaba ne, yayi kyau Sosai ga kamshi na tashi na fitan hankali, fita yayi daka d’akin inda fadawa suka zube a kasa suna zuba mai gaisuwa baiko kallesu ba, suka tashi suna binshi tare dayi mishi kirari Allah ya taimaki Yarima d’an sarki jikan sarki kaima gobe sarki ne, an gaida Yarima Mai jiran gado, takawanka lafiya, Yarima, haka sukai tamai kirari har ya shiga cikin inda mahaifin nashi yake, koda ya shiga yaga abban nashi shida wazirinsa waziri ganin Yarima Aliyu ya shigo yasa ya tashi ya basu waje, Yarima Aliyu zama yayi inda ya fara mi’kawa mahaifin nashi gaisuwa cikin girmamawa, mai martaba amsawa yayi tare da fad’in ina fata kaji sa’kona wajan Waziri? Yace eh naji Abba, amma Abba dole goben zan tafi? Mai martaba yace eh domin haka muka tsara da sarkin katsina dan haka a goben zaka tafi, yace Toh Abba Allah ya kaimu lafiya, mahaifin nashi ya amsa da Ameen, tashi yayi tare da fad’in bari in shiga gefen mum, fita yayi direct har wajan mahaifiyarshi inda kuyangi keta mata hidima, ganin d’an nata yasa tace su fita su bata waje, fita sukayi su duka Aliyu zama kusa da ita yayi tare da d’aura kanshi akan kafad’an mum din, murmushi tayi tare da fad’in waya tabamin dan lelena? Yace mum Abba yace gobe zani katsina ganin y’ar sarkin katsina, mum ni Wlh bana son zuwa kwata kwata, ni nafi son inga wacce tamin in aura ban San auran hadin nan, mum tayi murmushi tare da shafa Mai fuska tace son kasan nan gidan sarauta ne dole auran hadi za’ayi maka sannan inaso ka sani Indai bason ganin fushin mahaifinka kake ba dole gobe ka tafi katsina, yace mum dan Allah kiyi min wani abu mana ni akwai wacce nake so, mum tace wacece a ina take y’ar wacece? Duk a tare da jefo Mai wannan tambayoyin, shuru yayi domin bai San sunanta ba Toh y’ar wa zaice ma mum tunda bai taba ganinta ba sai a mafarkin shi, shuru yayi tare da lumshe ido yana mai jin zafin abun, mum ce ta katse shi da fad’in ya naji kayi shuru? Bakinshi ya tsinta da fad’in mum yarinyar karama ce bata gama karatu ba saita gama za’a mta aure, mum shuru tayi can tace toh Kaga mahaifinka bazai Bari kace zaka jira wata ba, dole ka tafi kt gobe kuma Kaga yayi ma sarkin katsina magana, yace mum ya……. Dakatar dashi tayi tare da fad’in ban son rigima kawai kayi abunda mahaifinka yace ni nayi maka alkawari duk Sanda ka kawo wacce kake so din zan tsaya maka har sai ka aureta, rungume mum dinshi yayi cikin jin dad’i, Sun dad’e suna fira Kafin ya fita, d’akinshi ya koma inda ya d’auko zanan yarinyar da yake gani a mafarki Wanda yayi ya d’auko yana ta kallo, a cikin ranshi yake fad’in kina da kyan jiki Allah yasa haka Fuskanki yake da zuciyarki, murmushi yayi tare da ajiye zanan domin jin karan wayanshi.

Ganin haske ya bud’e yasa bariki ta tashi tare da kallon Hon salis Wanda yake bacci abunshi gashi ya wani manneta a jikinsa kaman ance Mai zata gudu, d’an kokarin Fara jan jikinta daka nashi tayi, a hankali ya furta haba ina zaki ina son wannan fatan naki Mai laushi, tace sakeni inje inyi wanka sallah zanyi gashi har rana ya fito Banyi sallah ba, zumbur ya tashi yana ‘Kare mata kallo yace kina nufin kina sallah? Wani irin kallo ta watsa Mai tare da fad’in maika daukeni? Tana maganan ne tana tafiya, toilet ta fad’a tayi wanka sannan ta fito tasa kayanta sannan ta bud’e jakarta ta d’auko hijab tasa, sallah tayi Bayan ta idar Hon salis yace amma bariki Zanzo insan koke wacece, tace ba abunda ya kawo ni ba kenan, na riga Na baka abunda kake so tun jiya duk ka tsotse min ruwan jiki, dariya yayi tare da fad’in ai ruwan jikin ki bazai taba karewa ba, domin fita yake kaman famfo, har wani kara yake Tsit Tsit dariya bariki ta saki tare da fad’in kaga lokacin tafiya na yayi zan wuce, yace haba ki zauna mana gobe zan bar garin saiki tafi gaba d’aya, tace inada uzuri amma inda hali zan iya dawowa, d’auko check yayi ya rubuta mata 500k mi’ka mata yayi tare da tashi ya matseta a jikinsa yace komai naki yayi Ina jiran dawowanki, ayabarsa ta kamo Wanda yaji wani zir har saida taji jijiyar ayabar na harbawa sannan ta saki ta fita, dariya yayi domin ya gane tsokanan shi tayi gashi ta tafi ta barshi da sha’awa. Koda ta fita bank taje aka bata kud’in sannan taje bakinta tasa kud’in a ciki, direct gida ta koma inda Tana sauka a mota taga driver din alh madu har zata wuce komai ta tuna kuma oho yasa ta nufi wajan driver din, tace Yadai? Yace oga yace inzo in d’auko ki yana son ganinki kaman Kar taje sai kuma ta zaga ta shiga tace muje inji lafiya yake turoka kullum naga dai jiki nawa ne Sai naso zan bada, shidai driver baice komai ba sai tuki da yakeyi dan zuwa guest house din mai gidan nashi…….

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button