DANGI DAYA HAUSA NOVEL

DANGI DAYA HAUSA NOVEL

“ina fatan haka Doc, domin duk abinda mata ta bataso nima banaso, banason bacin ranta ko yayake”

“masha Allah, kanason matar nan taka Fawaz, dukanku kunason junanku,amma bansan wacce irin soyaiya ceba wannan, duk yanda kake sonta bazata iyama abinda kakeso ba, domin ta cetoka daga halaka”

“mekake nufi Doc?”

“matarka takirani rannan da alamun ma Kamar tana kuka, tace bakada lafiya inzo, nafada mata cewa maganin ai yana wajan ta, tabaka haqqin ka kawai, kai tsaye tacemin bazata iyaba”

Murmushi Fawaz yayi “ai tanada kunya Doc nima nasan bazata iyaba, kuma ni hakan datayi ya birgeni, inason mace Mai kunya, nikuma gaskiya kunyar tunkaranta nake da wannan abun, bansan ta Inda zan fara ba, please ko zaka bani wasu magungunan Wanda Zan dinga sha duk lokacin dana jini cikin wannan yanayin “

Dariya likitan yayi” lalle, ina Ruwan laila majnun, Wato ahakan batayi laifi awajan ka ba, kuma kai bazaka iya kai kanka wajantaba, lalle Fawaz irinku kadanne Awannan zamanin, to maganar gaskiya bazan baka kowanne irin magani ba, inzaku nemi haqqin junanku ku nema, idan bazaku nemaba shikkenan, amma kanada aure kanada mata bazan baka wani magani ba, wannan ai sai yarinyar ta rainaka ma tace baka iya mata komai “

Murmushi Fawaz yayi ” tace komai ma Doc, amma ni bazan iyaba “

Likitan yayi shiru yana kallan Fawaz, ikon Allah kenan, Awannan zamanin? ????

❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️

Tun bayan dasukai magana da Doc. Ya tattara maganarsa ya watsar yaci gaba da sabgarsa, har Tsawon sati daya, zaman su da Dida kuwa komai lafiya, yau Tun safe yakejin cikin sa yana murdawa, haka yatashi yafita, Dida na daki sai dirin motarsa taji, wajan wani abokinsa yaje, abokin na ganin Fawaz cikin damuwa ya tambayeshi meyake damunsa, nan take yafadawa abokin nasa, murmushi abokin yayi yace “dadina da gobe saurin zuwa”

Yatashi yaje daki yadauko masa wata kwalbar wine yace “abokina baka taba shan wannan ba, kasha ta, zakaji dadi, damuwar ka zata kau nan take”

Fawaz ya karbi kwalbar giyar nan yariqe, idan ya tuna cewa Dida bataso sai yaji jikinsa yayi sanyi, uwa uba shi duk shaye shayensa baitaba shan giya ba, to amma kuma idan ya tuna cewa damuwar sa zata kau saiyaji gara hakan “

Memakon yasha anan sai yatafi da ita gida, yana zuwa falo kuwa Dida tafuto daga daki zataje kitchen, kallan farko tayi masa ta hango rashin gaskiya awajan sa, taga sai boye hannu yake, bata zurfafa bincike ba tayi masa sannu da zuwa tawuce kitchen, shima cikin sauri yashige dakinsa, yadauko cup ya tsiyaya giyar aciki, Yazauna zai fara sha kenan taturo kofar dakin tashigo, abinda tagani agabansa ne yasa gabanta yayi mugun faduwa, giya? Dasauri taje tadauke gaba daya, ita dama tunda taga shigowarsa tasan cewa akwai abinda yake boye mata, cikin bacin rai tace “ya Fawaz miye hakan? Menene wannan?” idanunta suka cika da qwallah

Shiru yayi yakasa bata amsa, ita kuwa ta tsareshi da ido tana jiran amsa
Kallanta yayi sannan Dasauri yayi kasa da idonsa, cikin rashin gaskiya yafara yimata magana ” Dida… kiyi hakuri, wallahi ba laifi na bane, wani abokina ne…”

Kafin ya qarasa ta tareshi tace “to laifin waye?ya Fawaz Dan Allah yaya kakeso nayi da raina ne eh? Kai yaro kullum zamu dinga magana akan abu daya shekara da shekaru?”

Hawaye yazubo mata, tasa hannu ta goge, sannan tadauke kwalbar giyar da wadda yazuba akofin, ta miqe zata futo daga dakin cikin fishi

Dasauri yatashi ya fusgota jikinsa, ya rungumeta tabaya, tsayawa tayi cak, hawaye yana zuba a’idonta, Tun tana na hawaye harta dawo yi abaiyane, shi kansa yasan cewa bai kyauta mataba, amma yaya zaiyi? Kansa yadora akan wuyanta yayi shiru kuma yariqe ta gam ajikinsa, Ruwan dataji yana Saukowa daga wuyanta yana shirin shiga cikin rigarta ne ya tabbatar mata da cewa kuka yake

Saikuma jikinta yayi sanyi, tadena nata kukan tanajan zuciya, cikin hawaye yace “kiyi hakuri, bazan qaraba, Allah abokinane yabani, bansan yaya zanyi ba Dida, ina cikin damuwa, cikina kullum ciwo yake min”

Nan take Dida tafara tunani, karfa garin kunya tasa mijinta ya koma ruwa, bayan tasamu daqyar yadena shan komai, yanzu inda yasha giyar nan tasan cewa alhaki yana kanta, kuma dalilin ta ne yasa mijinta bayan shan qwaya ya koma shan giya, dolen dole zatai kokarin raba ya Fawaz da wannan abokin nasa duk da batasan ko wayeba

Cikin kunnanta yake mata magana Kamar rad’a yace “kiyi hakuri kinji, Dan Allah Karki sake tafiya kibarni”

Ajiyar zuciya tayi tace “toka cikani natafi, abinci Zan dora mana”

Cikin shagwaba yace “um um kibarshi, nasan sake guduwa zakiyi kibarni”

Girgiza kanta tayi, taga alama Jan magana kawai yakeso, ita zataje tabarshi Awannan halin salon yasake fadawa cikin shaye shaye, kokarin janye jikinta tafara yi shikuma yariqe ta gam, hannunsa takama tadaga masa su sama zata fita daga dakin, shikuma yakai mata wani irin ruqo, sai jin hannunsa tayi akan kirjinta, zaro ido tayi tana ganin Inda hannunsa yake, shi kansa yayi mamaki, amma memakon ya janye hannun nasa saiyayi shiru, laushin dayaji ne yasa yakasa dauke hannunsa daga wajan, baisan lokacin daya fara shafawa ba, amma hannunsa gaba daya rawa yake ????

Wani irin yanayi ta tsinci kanta aciki Wanda bata taba tsintar kanta aciki ba, cikin sanyin murya tace “ya Fawaz kabari Dan Allah, ni wani iri nakeji”

Yace “um um, nima haka nakeji”

Jikinta tafara janyewa, cikin sauri yaqara riqota, yaci gaba da abinda yake, wannan karon kam shiru Dida tayi, harga Allah tanajin dadin abinda yake mata, Dan haka tayi shiru tabarshi, daqyar ya’iya dago kansa ya kalleta, abin mamaki sai yaga Dida ta lumshe idonta, murmushi yayi, gaskiya in hakane yadade yana cutarsu gaba dayansu, cikin rad’a yace “akwai dadi?”

Ahankali ta daga masa kanta

Yasake cewa “kinaso in cigaba?”

Nanma Dida batayi magana ba kawai de tasake daga masa kanta, yana ji ta amince kuwa ya dauke ta cak, ya juya kan gadon sa da ita, kayan jikinta yafara cire mata, ahankali tabude idonta, mamaki ya kamata, tayi tunanin akan zaici gaba da kayan ta a jikinta, amma sai tayi shiru

Tana ganinsa yana kokarin cire nasa kayan tayi sauri ta rufe idonta, batasan lokacin daya gamaba sai jinsa tayi a jikinta, yasaka hannu ya balle mata breziyar jikinta, saida yagama kallan qirjinta tsaf yana ganin ikon Allah, sannan yadora bakinsa akai yafara sha, salon yanda yake mata ne yasa tarasa nutsuwarta, batasan lokacin data kai hannunta kansa ba, ta riqoshi sosai

Saida Fawaz yayiwa Dida charge sosai yanda bazata taba iya masa musu ba sannan yafara neman hanya, daga haka na futo nabar musu dakin

❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️

“maryam ga wannan kyautar danaso nabaki Tun ranar nan dakike min kuka, kuma Wanda nace yasiyo min bai kawomin da wuri ba”

Kallan hannunsa Diyana tayi cikeda mamaki, wata yar qaramar akwati ce da awarwaro aciki manya guda uku na gold, cikin murna ta karba tace “ya Adam duk nawane wannan?”

“yes naki ne, kawo hannunki nasaka miki”

Babu musu tabashi hannun, yazura mata awarwaron, sunyi mata kyau sosai

Tace “ya Adam nagode, nagode sosai”

“nine yakamata nayi miki godia maryam, saboda kyautar dakikamin, maganar gaskiya banyi tunanin haka Zan sameki ba, amma ina Mai qara baki hakuri akan hakan, kiyafemin”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81Next page

Leave a Reply

Back to top button