DANGI DAYA HAUSA NOVEL

DANGI DAYA HAUSA NOVEL

Ahankali tace” kayi hakuri Abba, kadinga maimaita kalmar Innalillahi wa inna ilaihir raju’un, insha Allah zakaji sanyi aranka “

Beyi musu ba haka yafara fada cikin ransa, Momy tana shafa kansa, tunani fal ranta, ahaka sukai bacci, Momy de baccinta ragagge ne, amma shi ya danyi kadan

Kiran sallar farko ne yatashe su, taji jikinsa da zafi, tabashi magani yasha sannan yatafi masallacin gidan, ita kuma ta nufi dakin Daddy

Bayan an idar da sallar asuba Momy bata koma bacci ba, addu’ah taci gaba dayi har gari yawaye tashiga kitchen da kanta tafara hada musu break fast

Karfe tara da minti uku tagama komai, takai musu kan dining, har lokacin Nihla bata futoba da alama bata tashi ba, Abba ma haka

Hanyar dakinta tanufa zataje ta watsa ruwa wayarta tayi qara, duba me kiran tayi mamaki ya kamata, afili tace “Mai hakuri!”

Sannan tadaga wayar, bayan sun gama gaisawa baba yace “hajiya dama maganar yar taki ne”

Tace “to Allah yasa de bamuyi laifi ba,”

“A a bakuyi laifin komai ba, jiya de munzauna da mahaifin Yusif dakuma yan’uwana dasuke yalleman, anyanke ranar bikin yartaki nanda wata biyu masu zuwa insha Allah, saiki fada mata, sannan kuma idan ansamu lokaci Zan turo muku da naku goron saka ranar saiki rabawa mutanan gidan “

Jikin Momy yayi sanyi sosai, cikin sanyin jiki tace” to shikkenan Ibrahim, mungode sosai, Allah yasa ayi damu, insha Allah zan sanar mata itama idan tatashi, yanzu tana bacci “

Yace” to shikkenan hajiya, ki gaida mutanan gidan “

Daga nan sukai sallama, Momy ta zubawa wayar ido tana kallo, wannan al’amari yafara bata tsoro fa, qamshin turaren daya saka ne yasa tadago kanta da sauri ta kalleshi, sanye yake cikin qananun kaya dasuka karbi jikinsa, ta kalli fuskarsa tayi fayau, kana ganinsa zaka hango tsananin damuwa a tattare dashi, tace “Abba na katashi?”

“yes natashi Momy, good morning”

Bata kula da gaisuwar dayake mata ba tajashi har dining tace “zoka zauna nabaka abinci, duk idonka yafada, kacire damuwa aranka fa”

“A a, Momy, bazan iyacin komai ba, kibarshi kawai, inaso zanje saudia, may be nadawo after 3 day’s, Momy nasan Daddy yana fishi dani, Kibashi hakuri, kifada masa naje saudia”

Tausayinsa ya kamata, duba yanda yashiga damuwa ahaka ma baida labarin saka mata rana, ahankali tace “saika dawo, zan sanar dashi, amma kayimin alqawarin zaka kula da kanka”

Badan yaso ba ya qaqaro Murmushi yace “insha Allah Momy”

Ahankali yatashi yafita daga falon Momy tabishi da kallo jiki a sanyaye

Sharhi please ????

Amnah El Yaqoub ✍️
[7/11, 11:52 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI ‘DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook ????
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493

49&50

Tasan cewa ba komai ne zai kaishi saudia ba saidon saboda damuwar dayake ciki
Kuma hakan ma tunani ne Mai kyau, domin kuwa addu’ah ita kadai ce mafita Awannan halin da yake ciki, ta Inda yake birgeta kenan, kokadan baya Manta Allah acikin dukkanin al’amuransa

Dakin Daddy tawuce domin sanar dashi yanda sukai damai hakuri

Tana shiga taganshi yafuto daga wanka yana shirya wa

Waje tasamu tazauna agefen gadon tace “Alhaji barka da tashi”

“yawwa Rahma”

Tasake dubansa tace “Alhaji kana nunawa al’amarin yaron nan Kamar bai dameka ba, kuma yana cikin matsala sosai fa, jiya kasa bacci yayi, ita Nihla taqi amince wa dashi, kai yazo da maganar ka koreshi, yanzu haka jikinsa Babu dadi yatafi saudia nasan kuma saboda hakan yatafi, dazu Mai hakuri yakirani yace ansawa Nihla rana nanda wata biyu bikin “

” daidai kenan “

Cikin sauri ta kalleshi tace” Alhaji,yakamata aduba wannan al’amarin, bazai iyu nasamu yarinyar nan da batun taso danaba, Kamar na tursasata ne, tunda batayi niyya ba”

“kinsan da hakan kikazo kikemin magana, ni mezan iyayi akai?”

“Alhaji kaine kuwa zaka iyayin komai, tunda idan kafada tazauna”

“ba kuma zan fada dinba bare tazauna, angama break fast ne?”

Momy ta kalleshi cikin mamaki, Annabi yayi gaskiya dayace abu uwa har sau uku, sannan yace uba ????

Tace “angama”

Sannan tashige toilet domin yin wanka

Zaune suke a dining Sunayin break su uku, Momy ta kalli Nihla cikeda kulawa tace “Dazu munyi waya da Mai hakuri yace zai aiko mana namu goron”

Dago kanta tayi “Momy goron me?”

Cikin farin-ciki Momy tace “nasaka ranar yata nanda wata biyu”

Cikin kunya tasa hannu ta rufe idonta

Daddy yayi Murmushi ya kalleta yace “saiki Rubutamin list din abinda kike buqata kije daki ki dauki atm dina kuje keda yayanki kusiyo, abinda Babu kuma saiki shirya kuje Dubai keda momynki kusiyo Acan”

Kanta aqasa cikeda kunya tace “nagode Daddy”

Momy ma tayi Murmushi cikin ranta tana Jinjina irin yanda Allah yasaka musu qaunar yarinyar aransu baki daya

❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️

Tunda yaje saudia baije ko’inaba, yana zaune cikin harami yana addu’ah, ya kashe wayoyin hannunsa, bai nemi kowaba, kuma bayason a nemeshi adede wannan ranakun
Addu’ah yake Allah yakawo masa mafita akan wannan al’amari, idan har Nihla matarsace to Allah yahuci zuciyarta ta soshi, idan kuma ba matar sa bace Allah yabashi hakuri da juriya akan rashin ta, Allah kuma yasa hakane yafi alkhaairi a gareshi

Sosai yaduqufa wajan neman zabin Allah, yana kaiwa Allah kukansa saboda shine Mai kowa Mai komai,kowa ya juya masa baya, banda ‘yan’uwansa da Aslam Babu Wanda yake sonsa da Nihla, sai kuma Momy datake tausaya masa, abinci ma ba sosai yake cinsa ba, gaba daya ya rame cikin kwana kin, ya lalace, ga qirjinsa dayake masa zafi sosai idan yatuno da cewa Nihla tayiwa baban ta maganar Yusif, jiyake Kamar ana zuba masa barkono acikin qirjinsa

Allah shine gatansa a yanzu, bashida wani gata daya wuce yakai kukansa wajan mahaliccinmu

Daren juma’ah kuwa yayi addu’ah sosai, yayi kuka yayi kuka harya gaji, sannan cikin dare yabiyo jirgi yadawo gida, su kansu su Momy basusan yadawo ba, saboda Saukar cikin dare yayi

❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️

Zaune yake afalon shi kadai, yana sanye da three quater, da wata riga marar hannu, computer ce agabansa yana ta typing cikin sauri, gaba daya hankalinsa ya tattara shi akan abinda yakeyi

Momy ce tafuto falon sai ganinsa tayi, ta tsaya tayi turus, tace “Abba na yaushe kadawo Babu sanarwa?”

Dagowa yayi daga typing din dayake yadubeta “Momy cikin dare nasauka, bansan na tasheku ne shiyasa banje dakin ki ba”

“to sannu da zuwa, duk wayoyinka akashe, ina kabarsu ne?”

“Momy kashe su nayi wallahi, ina Daddy?”

Zama tayi a gefensa tace “yana dakinsa, yanzu zai futo shima”

Yace “Ok” sannan yaci gaba da abinda yake

Futowa tayi daga dakinta tayi kyau sosai cikin wani Material,qamshin ta dayaji ne yasa Ahankali yadago kansa ya kalleta, karaf idonsu yahadu, itace tafara janye nata idon, shikuwa Kallanta yayi yana mamakin canjawar datayi cikin kwanaki hudu, jikinta yayi lumai, sai wani qara cika takeyi, hankalin ta kwance
, sauke kansa yayi yaci gaba da abinda yake

Momy ta kalleta tace “wannan gyaran jikin nasu gaskiya sun iya sosai, idan aka miki na 3week ma ya’isa, saiki zauna agida kidena fita ko’ina, saiki sanar awajan service din naku ma”

Tace “to Momy”

Ta kalli Abba dake zaune yana typing amma tunani ne da tambaya fal ransa, gyaran jikin me ake mata? Ko bikin qawarta za’ayi? ????

Bai samu amsar Tambayar tasaba yaji tace “Ya Abba ina kwana”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81Next page

Leave a Reply

Back to top button