BABU SO HAUSA NOVEL

DUBU JIKAR MAI CARBI HAUSA NOVEL

Tun a ranar su Baba Abubakar suka riƙa kiran mutane suna sanar da su janyo lokacin bikin, haka a cikin garin Ɗangwauro kafin wani lokaci tuni labarin ya karɗe ko’ina. Baƙin ciki a wurin Hajiya Nafisa har ya ƙi musaltuwa don ranar kwana suka yi suna yin babu daɗi ita da Maigidanta. Haka daga wurin Aseem ranar kusan kwana ya yi cikin takaici, amma Dubu ko a jikinta baccinta ta yi hankali kwance. Hafsa ma kusan kwana ta yi tana kuka don gani take lokaci ne ya yi da za ta rasa masoyinta ba tare da cikon muradinta ba.

Gari na wayewa Aseem ya fice daga gidan yana fita ya kira wayar Nasir ya sanar da shi, nan dai Nasir ya jajanta masa daga baya kuma ya tambaye shi ko akwai wani party da za su yi. Aseem na jin haka ya katse wayar, Nasir ya yi ta kiransa amma fir ya ƙi ɗauka.

Shirye-shirye gabaɗaya sun gama nisa a cikin gidan, daga ɓangaren Mazan har matan. Da yake duk lamarin na cikin gida ne rana ɗaya aka kai lefen su Dubu wanda a lokacin bikin saura kwana biyu. Inna Furai da Yaya babba bilhaƙƙi suka dage da gyaran amare su ne jiƙa wannan, dafa wannan duk a basu. Sai kuma gyaran jiki da Hadiza take zuwa tana yi musu, Dubu ta yi kyau sosai hasken fatarta ya sake fitowa. Sai dai gashi shi ne ya yi mata cikas. Donma tana da kufan gashi kan ya yi dubu sumar ta fara fitowa, sai dai daga baya idan ka hangota sai ka rantse da Allah namiji ne. Duk wani abin buƙata da mace take yi na Party da wasu harkokin Baba Abubakar ne ya bawa Dubu, wannan dalilin ne ya sa ko kaɗan Dubu bata wani damu da rashin ganin Aseem ba. Ita kuwa Yaya babba da yake mutane sun fara cika gidan sabga ta sha kanta ya sa bata bi ta kansu ba.

Mutane sai mamaki suke da akan auren Dubu kasancewar duk sai daga baya aka ji zancen haɗin nata auren da Aseem, nan dai aka ci gaba da shagali. Aseem kuwa daga Nasir babu wanda ya sanarwa a cikin abokansu, don gani yake ci baya ne ace an yi masa aure da yarinya kamar Dubu.

RANA BA TA ƘARYA…

Kimanin ƙarfe biyu na ranar Juma’a aka ɗaura auren jikokin marigayi Mai carbi, ciki kuwa har Dubu da Aseem a babban masallacin gidan Sarki da ke cikin garin jihar Kanon Dabo. Mutane masu tarin yarawa ne suka shaida wannan ɗaurin auren, fuskar su Salisu abin ba a magana saboda farinciki. Shi kuwa Aseem ban da cin ɗaci babu abin da yake yi, daga Nasir sai abokansu da basu kai goma ba. Suma duk Nasir ne ya sanar musu lokacin da Aseem ya ji labari kiran Nasir ya yi, yai masa fata-fata har sai da suka yi faɗa a wurin. Daga wurin ɗaurin aure suka ɗungumo zuwa gida.

Daga can gida mata ne suke ta shagali, an kira masu kiɗan ƙwarya sai cashewa ake. Idan ka ga yadda Dubu take cashewa sai ka ɗauka ita ma ƴar taron biki ce ba amarya ba, su Yaya babba da Inna Furai an sha atamfa mai kyau sun yi anko sai fama ake da jama’a. Bayan angwaye sun dawo gida nan fa aka shiga hotuna angwayen da iyayensu fuskarsu fal farinciki. Abin da ya hana Aseem tafiya sashensu don kar ya kunyata Mahaifinsa, saboda ya san matuƙar ba a gan shi ba an riƙa tambayarsa kenan, don haka ya daure aka yi ta ɗaukan hotuna sai daga baya ya zame jikinsa ya wuce can sashensa shi da su Nasir.

Da daddare.

 Gabaɗaya angwaye da amaren aka haɗa a babban falon Yaya Babba, haɗe da iyayensu maza da mata, Sai Yaya babba da Inna Furai. Tun da magriba da doso Yaya babba take sharar ƙwalla, lokacin da aka tattaru a ɗakin duka amaren kansu na cikin mayafi a lulluɓe da alama kuka suke wanda bai kai har zuci ba. Wasu daga cikinsu ma babu ko ɗugon hawaye, Angwayen kuwa sai sunne kai ƙasa suke yi saboda wani irin nauyin Iyayen nasu da suke ji. Dubu da ke cikin mayafi a lulluɓe ban da satar kallon mutanen ɗakin babbu abin take yi, da ta gaji da kallonsu ta cikin mayafi sai ta riƙa ɗaga mayafin tana fakar idonsu tana leƙe, da sun haɗa ido da ɗaya daga cikin kawunnan nata sai ta maza ta sauke mayafinta.

Baba Mumkaila ne ya yi gyara murya haɗe da addu’a sannan ya ɗora da nasiha, daga ƙarshe ya buƙaci su Yaya babba da su yi wa amare d angwaye nasihar zaman aure.

Yaya babba har lokacin ban da kuka babu abin da take yi, ganin haka ya sa Baba Abubakar ya ce Inna Furai ta wakilci Yaya babba. Inna Furai ta rangwaɗa kai gefe sannan ta ce, “Garba ban ƙi ta taka ba amma ka san dai bin na gaba bin Allah? Tun da kuka taso a cikin gidan nan kun taɓa ganin na shige gaba a abu ba tare da Yaya ta fara yi ba.” Yaya babba ta sharce hawaye ta ce, “Bar shi Furaira so yake ki kaucewa tarbiyyar Malam. To gaskiya ba haka mu ke ba, kar dai ka yi wani mugun halin a gaban yaran nan su ɗauka suma su idar a gidajen aurensu. Shi ya sa mu ke aikata alheri ni da ƴar uwata, don mu samu rabo da gidan Aljannah.” Yaya babba ta ƙarasa maganar tana kallon Inna Furai. Baba Sule ya gyaɗa kai sannan ya ce, “To Inno bismillah!” Yaya babba ta gyara zama tana cewa:

“Ku ba ni hankulanku wuri ɗaya domin zaman aure ba wasa ba, ku dubi iyayenku kamar yau aka kawo mana su ɗakin nan ga shi yau sun aurar da ku. Zan fara da ku matan alƙur’an ku ji tsoron Allah ku yi wa mazajenku biyayya, idan ba haka ba har abada babu ni babu ku. Ga Furaira ita ce sheda ko a lahira kar wanda ya nuna ya sanni, tun da duk wacce bata bi aure ba kwarankwatsa dubu makomarta wuta. A’a ku raba ni da zan cen jahannama a na zaune ƙalau, meye haɗina da ita bayan ina sahun masoya Annabi (S.A.W). Ku yi biyayyar aure ku samu Aljannah mu haɗu da ku a zangon barka-barka a cikin Aljannah. Idan na hango Zulfa na ɗaga mata hannu sai na hango Dubu musha alkausara, mu ci abin da muke so mu sha abin da muke so. Yoo zaman duniyar nawa yake a kan idonku dai Munkaila yake gadinmu ni da Furaira, don masifa naman ma suna hanamu ci ina dalili. A’a rabani da wannan mugun halin ku yi biyayyar aure mu ci nama mu ci ƴan shiloli tare ba wanda zai mana iyaka, idan kun ƙi kum a kaiku Jahannama a haɗa ku da Mala’iku su yi muku walmukalifatu.” Mutanan ɗakin ne suka sa dariya don yadda Yaya babba take haƙiƙancewa a zancen aljannah sai ka rantse da Allah tuni an yi mata bushara da tata aljannar tun a duniya. Ta juya wurin angwayen suma ta ƙare musu kallo ta saki murmushi tana faɗin:

“Allah mai iko ku dubi su Soja fuska sai walƙiya take, don Allah ban da aure wa zai yi maka haka? To ku saurareni da kyau don har ga Allah ba zan lamunci baku jikokina ku riƙa gasa musu aya a hannu ba, a’a raba ni da wannan falsafar. Yara dai amana muka basu ku kyautata musu da ma zaman aure sai haƙuri, iyayenku ma duk da haka suka kawo nan. Ga dai Ado nan ga sauran iyayenku tun da nake da su ban taɓa jin wata falsafar tashin hankalin ta ɓullo daga wurinsu da matansu ba. A cikinsu duk wacce ta ɓata muku rai ku zo ku same ni ku gaya min ranar mai cetonta a hannuna sai Allah, ku riƙa kula da su ɗan tsiren nan da ƴan kajin nan kun san suma suna ƙara danƙon ƙauna. Allah dai ya ƙara yalwata kaji a faɗin duniya ba don su ba da tuni ba a haife ka ba Salisu, ga Uwarka nan ba zan mata ƙarya ba, lokacin da aka aurota alƙur’an bata ƙaunar Ubanka. Amma da yake Ubanka ma’abocin siyan kaji ne sai wayar gari na yi na ga uwarka da ciki, don Allah ka gaya min idan kaji suka yi ƙaranci ya ya gidan aure zai yi.” Ɗakin dai kowa ya yi shiru ba su tanka ba. Yaya babba ta yi ƙasa da murya ta ci gaba da cewa:

“Kun san dai sha’anin tsoho sai haƙuri, ni dai tun da nake baku taɓa yi mini komai ba amma ni dai ku gafarce ni idan na ɓata muku rai, yanzu Furaira ta ci gaba da nasihar.”

Amsa mata suka yi sannan Inno ta ci gaba da jawabi. “Ni dai ƴar taƙaitacciyar nasiha gare ni. Gabaɗaya zan ce su ji tsoron Allah idan ba haka babu abin da zai hana mu zazzage musu albarka a tsakiyar ka. Ku matan yi na yi bari na bari sai kwalliya kissa da kisisina kamar yadda muka koya muku, Allah ya sani idan kuka saɓawa Allah babu sa hannunmu a ciki. Ku kuma mazan ku ne jagorori idan laifi suka yi banda duka ko zagi, don Allah ya sani ba za mu juri haka ba duk wanda ya taɓa mana jika alƙur’an mai hana mu maka shi wurin human rai (Human right) sai dai idan bama numfashi. Da haka nake yi musu fatan alheri.”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button