JUHUD COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

JUHUD COMPLETE HAUSA NOVEL

JUHUD COMPLETE HAUSA NOVEL BY OUM HAIRAN

Batasan gari ya waye ba saida taji ana buga qofar a hankali yanayin sanyin bugun yasata miqewa ta dauki towel ta daura ta bude qofar Yana ganinta ya bude mata hannu ta fada qirjinsa kamar yanda ya sabar mata ya shafa kanta tare da tura hancinsa cikin sumarta ya shaqi qamshin turaren gashin da ta fesa yaja ajiyar zuciya ya dagata cak ya dorata a katifar ya juya ya bude wardrobe din nata ya dauko mata wasu riga da wando masu masifar kyau ya sake dauko mata pant da bra ya dawo ya zauna kusa da ita yasa hannu yana qoqarin janye mata towel din ta qanqame qirjinta tasa kuka yayi saurin sakin towel din tare da janyota jikinsa ya rungume sosai cikin rawar murya yace.
“Bantaba tunanin Christy zataci amanata ba shiyasa nabarta dake a gdannan wlh a mafarki aka nunamin abinda ya faru a qa’ida sai nayi sati zan dawo zuciyata bazata nutsu ba shiyasa na sato hanya na taho Ina zuwa ta fadamin wai kinqi yarda ta nuna miki yanda zakisa bra din tunda ta fadimin haka naji ban amince ba na matsa mata lamba daqyar ta fadamin gsky kiyi hqr don Allah Raina bai taba kawomin hakan ba”

Ajiyar zuciya ta rinqa saukewa ta dago ta kalleshi shima ita yake kallo ta lumshe idonta tasa hannu ta shafa gemunsa tace “ni….nidai bazan qara zama da itaba yar iskace harfa hannu tasamin a wando na…..” “What!?” Ya fada da qaraji nandanan fuskarsa ta qara canza yanayi ya miqa mata pant dinta jikinsa na rawa yace “maza kisa mu tafi bazan barki barreck dinnan ba gara itama mace ne komai zai iya faruwa cikin sati gudannan da zanyi bananan” karba tayi tasa ya janye towel din tayi qasa da sauri ya dakanta tsawar ds rabon da yayi mata irinta tun tana asibiti yace “ki tashi na shiryaki mu tafi tunda ke sakarci ya hanaki sanin yanda zaki shirya kanki” bai jira miqewarta ya miqar da ita da qarfi ya juyar da ita ya dauka bra din yasa mata yanajinta tana kukanta bai kulata ba Saida ya gama Sanya mata ya tureta yaja tsaki yace “sakarya kawai kintaba ganin Uba yaji wani abu game da yarsa ne maza ungo wando din sa”
Karba tayi tasa hankalinsa Yana kan wayarsa da taketa ring ya miqanta rigar tasa ya juyo ya zubanta ido yaja ajiyar numfashi ya murmusa ya yafitota ta noqe tana turo baki yayi murmushi me sauti ya sunkuya ya kama kunnensa yace “sorry my special daughter Baffa’am yayi laifi yaga nonon yarsa tanajin haushinsa….”

Hannu tasa ta rufe idonta tana yar qaramar dariya shima dariyar yayi ya dagata cak suka fito falon ya dauko abincin daya siyo mata ya baje mata da kansa ya rinqa bata tanaci idan taso tsokanarsa ta cije masa hannu hannu yakai yaja hancinta tayi dariya shima yayi murmushi suka tashi ya rufe gidan ya bude mata mota ta shiga yaja suka fice daga barrack din ya dauki hanyar Maiduguri suna tafe tanata zubansa surutunta na shirme komi ta gani sai tayi masa tambaya wata ya bata Amsa wata Kuma yace “Oh God Meenah kin fiye tambaya Allah zan dinke bakinki fah” daya fadi haka sai ta kama shure² a qarshe hqr yake bata.
A Damaturu suka tsaya ya nema mata abinda zataci sukayi sallah sannan suka sake daukar hanya tafiyar taqi qarewa tin tana surutunta da waqoqinta har bacci ya dauketa ya samu guri yayi parking ya gyaranta kwanciya a jikinsa yaci gaba da tuqinsa sai bayan suka isa cikin Maiduguri inda shi daya ne dare bazai hanashi qarasawa camp dinsu ba Amma saboda ita dole ya nemi hotel ya kama ya dauketa cak ya nufi dakin da ita ya dorata a gado yaja mata bargo ya sake fita yayi sallah ya nufi restaurant din cikin hotel din ya siyo musu abinci ya dawo, tunda suka iso ta farka tanajin sanda ya dagata ya shigar da ita dakin ya kwantarta bayan fitarsa ta tashi ta shiga bayin tayi wanka tayi alwala tazo tayi sallah tana idarwa Yana shigowa ya zube a gadon Yana mayar da numfashi ta miqe ta isa gabanshi ta tsugunna tace “Baffa’am barka da gajiya” miqa yayi yace “na gaji sosai daughter kici abinci kiyimin tausa” daukar abincin tayi sakwara ce da miyar agusi ta kalleshi tace “ni banason bata hannu na”
Dafe kansa yayi hutu kawai yake buqata yace “don Allah kici da kanki” ture abincin tayi ta fara shure² tana tabe baki zatayi kuka bashida yanda ya iya dole ya diro a gadon yaje ya dagota ya zaunar da ita a cinyarsa ya dungure mata kai yace “kina wahalar da Baffa’am am dinki bazaki qararmin da ruwan kai ba yarinya miji zan nema miki nayi miki aure kuje ku qarata” dariya abin ya bata tace “tabdi Ni banaso kaine kace aure damuwa ce inajinka kana fadawa Aunty Christy ranannan Kuma naji kana waya kana cewa Mai martaba bazakayi aure ba a qyaleka bakason duk wani abu dazai taba farin cikin ka”

Hadiye wani abu yayi me zafi dole ya saita bakinsa ashe yarinyar tana gane kalamansa, kafin ya gama nutsuwa yaji tace “ayyah Baffa’am Kuma naga kanada aure Aunty Christy ai matarka ce ko?….” Furzar da abincin bakinsa yayi saboda tashin zuciyar da yaji ya taso masa yace “kayyy ke nifa kin dameni Kuma idan zanyi auren don asara na rasa wa zan aura sai Cristian” miqewa yayi zai fita tace “to Kuma naga daki daya kuke kwana Kuma naga tanayi Mana girki…..” Shut-up Meenah…..” Abinda ya fada kenan ya juya ya fice ta tsaya sororo duk sai taji bataji dadi ba ta bata ran Baffa’am dinta komawa tayi ta zauna tayi tagumi kawai sai ta kama tsiyayar da hawaye, shiru² tana duba agogo har 12:30am bai shigo ba jikinta ya qara sanyi ta miqe tasa hijjab dinta ta bude dakin ta fito ta tsaya a corridor din tana kallon masu wuccewa ta qasa tana hango gifcin mutane jefi² tana share hawayenta tafi 30 minutes a gurin can ta hangoshi shida wata mace a tsaye suna tattaunawa ta zubansa ido ganin Yana murmushi ya karkace yasa hannu a aljihu ya zaro kudi yabawa matar daidai lkcn taji an taba kafadarta ta baya.

Juyowa tayi da sauri taja da baya ganin wani saurayi ne kyakkyawa dashi murmushi yayi cikin fara’a yace “tun dazun na hangoki a tsaye anan beautiful girl wa kike jira ne…..? Bai rufe bakinsa ba yaji saukar mari a kuncinsa bashi da aka mara ba ita kanta Saida ta dafe nata kuncin ya nunashi da yatsa yace “get out for my area….” Cije lebe yayi ya nunashi da yatsa zaiyi mgn kafin yace komai Rasheed ya figi hannun Juhud ya cillata daki a mugum fusace ya sake fita ya zare bindiga a qugunsa ya saita wannan saurayin da sauri yayi qasa cikin tashin hankali yace “wlh ba wani abu zan nema a gurinta ba ganinta nayi cikin damuwa tanata kuka shine nazo ko tana buqatar taimako…..” Sauke Gum din yayi ya furzar da iska me zafi ya dagoshi yace “sorry” daga haka ya shige dakin ya danno qofar da qarfi tana tsugunne inda ya watsar da ita ya fara yage kayansa Saida ya rage dagashi sai boxes ya juya zai shige bathroom da sauri ta miqe ta dago zatayi mgn ganinsa a tuben yasata ja da baya da sauri tana kallonsa bakinta Yana rawa, tunda take a rayuwarta bata taba ganin namiji a wannan yanayin ba, qwafa yayi ya fada bathroom din ya tsarkake jikinsa ya fito daure da towel a qugunsa Yana goge jikinsa da wani gashin jikinsa yaji ruwa ya kwanta luf kamar an shafansa mai.
Ji tayi ya dago kanta yayi jifa da towel din hannunsa yace “gidan ubanwa kika fita zakije a wannan tsohon daren?” Babu yanayin wasa a tare dashi hakan yasa ta shiga taitayinta tuni hawaye ya qara kwace mata ta rintse idanunta batason ganinsa a haka gabanta faduwa yakeyi bataji ba batayi aune ba taji ya cafki hannunta ya matse da qarfe ta sake rushewa da kuka yace “open ur eyes” da qaraji ya fada ta bude da sauri duk wata gaba ta jikinta rawa takeyi bata taba shiga tsoro da dimuwa irin na yau ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button