WATA ALKARYAR COMPLETE HAUSA NOVEL

WATA ALKARYAR COMPLETE HAUSA NOVEL

  *
Las Vegas.

Mika mata wasu files aka yi ta zuba mishi ido, kafin ta ce.
“Tana raye kenan? Dole mu cigaba da samun wasu bayanai masu matukar muhimmanci akan ta.”
“Mss Kelly Clarkson an dai tabbatar tana raye ne ta hanyar zanen dan ysatsarta bamu da tabbacin tana nan din. Kuma kusan shekaru ashirin da biyar kenan da mutuwar ta” inji Mr Andrew Cuomo. Murmushi tayi tare da mikewa tare da nufar water dispenser ta dibi ruwa a cikin shi yana k kallon Mr Andrew Cuomo.

  “Ka tab’a ganin fatalwa a cikin rukunin mu?” Girgiza mata kai yayi, sannan tace.
“Ita din Fatalwa ce, duk ALKARYAR da ta zauna ta kuma basu horo akan mutuwa toh tabbas zakwakuran dalibai ne masu matukar hatsari. Dan haka ka duba yanayin idan ka samu ta horar da daliban da suka mutu tabbas ita ce”
“Mss Kelly Clarkson Babu wani labarin ta horar da wasu dalibai, tana zaune a garin Tivilo na Æ™asar.”

   “Keep it secret zan wai-waiyi batun” ta fada tare da ajiye kofin ta taka har gaban glass din, da yake jikin building din, wanda yake kamar da shi aka gini baki daya, kallon yadda ake zarga zarga ake, jikin ta yayi mugun sanyi. Idanun ta ya cika da kwalla, domin ta san laifin ta ne da ta bar kome ya faru a wannan ranar, da bata yi magana ba da babu abinda zai faru ta kuma san halin ta, bata yafiya bata manta ranar daukar fansa, idan har tana raye tana kan shirya yadda zata dauki fansa kuma zata rama bata tab’a aiki ta fadi ba.

    Zata nime ta koda kuwa zata rasa rayuwarta zata bata goyan bayan daukar fansata.
*
Lagos.

Irfan Kabir Wazir.

Yana dakin daukar karfen shi, ta shigo a hankali tana kallon shi. Ganin bai d’ago kai ya kalle ta ba, jikinta ya kuma sanyi.

“Irfan!” Banza yayi mata bai d’ago kai ta kalle ta ba,.ajiye cup din tea din tayi sannan ta rike karfen da zai d’aga.
“Please ka saurare ni mana”

“Ki tafi bana son magana” ya fada mata a dake, kallon shi tayi tare da cewa.
“Kayi hakuri ba laifina bane nima babu yadda na iya ne, amma kayi hakuri gani nan gare ka”

   Murmushi yai tare da sauke karfen da yake hannun shi, ya mike.
“Kika ce nayi hakuri?” Gabanta ne ta fadi, kafin ya mike a hankali ya d’ago a hankali tare da janyo hannun ta suka fita daga cikin falon ya nufi waje.

“Don Allah ka saurare ni, don Allah kar ka kore ni, na hada ka da Allah kasan waye aka bani a matsayin mijin da zan aura? Bilal Ahmad Jikamshi…” Wani irin shake ta yayi sai da Idanunta suka firfito waje.

“Yar iska bayan kin gama sake min jikinki na ji dadin cin ki ba dare ba rana ki ce min wancan kazan turawan zaki aura? Meye zai Miki? Look tunda kika shiga ya mike ya tsaya sabida ya ga abincin ruhin shi. Wallahi kika sake aka makala miki shi sai na kashe ki da hannuna bayan nayi f**ck É—inki crazy out” ya cillata kofar gidan shi.

Wani irin kuka ne ya zo mata, kallon shi tayi yana tafiya cikin nutsuwa, kamar ba ita ya wulakanta ba, dan haka cikin fushi. Tashi tayi tare da nufar waje, shiga motar ta tayi tana kuka.
*
Tashi tayi tana had’a kayanta, musamman materials din ta, ta zuba a cikin jakarta, dake yau sun shiga lab ne practical. Tana gamawa ta fito a hankali tana juyar da wuyarta, tare da mika.

   Tana fitowa wurin da aka daukar su, ta hango shi tsaye. Jikin motar shi, dauke kai tayi tare da shiga motar makarantar, kulle motar shi yayi tare da nufar school bus din. Yana shiga akayi ya matsa mishi, tsayawa yayi akanta,
“Sir ka zauna mana” murmushi yayi tare da kallon Yarinyar ya ce mata.
“Nan ma ya isa!”
Dauke kai Rahmah tayi tare da jin kwalla na zuba mata, sabida baki daya ya hanata sakat, kuma ya hana kowa yayi musamman mazan ajin su. Har kofar gidan su aka kawo ta, da zata sauka ne ya dauki wani abu ya saka a cikin jakarta. Sannan ta ce mata.
“Saura kwanaki Æ™alilan ku fara exam ki nutsu ki yi karatu”  a hankali ta bar bus din, tana share kwalla da yake zuba mata, har ta shiga cikin gidan sannan suka wuce kai sauran Yaran.

A falo ta sami Ammyn da Alhaji Muhammad Lawal Dambatta, da Mammyn sai Hajiya Atikah da take gefen su.
“Assalamu alaikum! Sannun ku da gida” ta fada,
“Rahmah” Hajiya Atikah ta kira sunan ta, dake bata san ta ba, sai dai yanayin ta da ya mata kama da na Faisal, ta koma a hankali ta durkusa cikin matsanancin kunya ta ce mata.
“Sannun Ma”
“Ajin ki nawa?”
“Ss2”
“Ok daga wannan zaku gama kenan? Me zaki karanta?” Sunkuyar da kai tayi tana kallon kasa, kafin ta ce mata.
“Medicine.”
“Aure fa” da sauri ta d’ago kai tana kallon ta kafin ta mai da kanta gefe bayan ta kalli Ammyn, Idanunta na zubda kwalla.
“Kina son shi ne?” Ta kuma tambayar ta, juyar da kanta tayi tana kallon Ammynta, bata san me zata ce ba. Itama ganin yadda Ammyn taki kallonta yasa ta ce mata.
“A’a!”
“Toh me yasa kira kuka?” Goge kwallar tayi tana cewa.
“Ba kuka nake ba”
“Jeki”
Da sauri ta mike tare da É—aukar jakar, tana shiga dakin su, Jamilah ta rungume ta.
“Sun zo niman auren ki ne?” Girgiza kai tayi tana kuka.
“Bana son shi fa”
” Shi yasa kike kuka! Kina son shi Dan gashi kina kuka, kuma tun ranar da Ammyn ta miki magana kika koma haka Love!.”

Share ta tayi tare da nufar ban daki.

Murmushi Hajiya Atikah tayi sannan ta ce musu.
“Ba zan tirsassa ki akan Yar ki ba, sai dai zan ba shi hakuri ya nime wata, duk lokacin da kika ga ya da ce yazo niman aurenta shi kenan…
300â‚?… Insha Allah’
+2347035133148 a tuntube Zahrah Addah Ramlat, Yan Niger su tuntubi Nana A’ichah
+22784506476
0472282105 Ramlat abdulrahman manga GT bank

Mai_Dambu

3/1/22, 18:57 – Nuriyyat: 41
“Sam babu laifi a duk hukuncin da zaki dauka duk daya ne.” Girgiza kai Ammyn tayi sannan ta ce mata.
“Ba naÆ™i bane, ina son duk inda zasu shiga kar a wulakanta min su ne, bana son su yi rayuwar kuncin da muka yi ya cigaba da tab’a rayuwar su ba zan yafewa kaina ba, yayi hakuri idan matar shi ce sai mu ga babu bata lokaci an yi amma yanzun yanzun idan ta had’a gudu da sosa duwawu zai mata yawwa karatu karatu aure aure, amma idan har ta bukaci auren ba damuwa sai a mata tunda tana bukatar haka”

        Shiru falon ya dauka, sai dai kuma babu yadda zasu mata dole, domin maganar gaskiya sun fahimci bata son ayi auren, amma kuma yadda suka fahimci Rahmah na kuka sai suke ganin kamar tana son Faisal din ne.
“Toh Ammyn su, duk yadda aka yi daya ne, ina jiran abinda kuka yanke, Allah ya gani ba suruka Nazo nima ba a cikin gidan ba, Y’a nazo a bani sannan bana jin daga ni har shi Faisal din zamu hanata karatu ba, sai dai idan itace bata bukata, idan dan karatun likitanci ne, ni da kaina zan kaita inda zata yi karatu da sakamakon ta me kyau, kamar yadda nake da Layinah da Lubna bana jin zan cutar da wata Yar nima ina son idan aka dauke Layinah, bani da kowa sai Rahmah amma sai Ammyn Rahmah ta amince. Toh ni zan tafi” ta faÉ—a, mikewa suka yi tare da rakata waje, sannan suka dawo Alhaji Muhammad Lawal Dambatta ya cewa Ammyn.
“Idan dai na wani abu bane a ranki, ki basu auren ta mana,  kuma Hajiya Atikah Abbas Jikamshi ba karamar mace ba ce, domin tana cikin manyan mata masu daraja a cikin garin lagos da katsina..sannan idan kika duba Yaron yana da nagarta, da kanta tazo niman auren danta, don Allah ki amince ayi auren”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137Next page

Leave a Reply

Back to top button