DEEN MARSHALL COMPLETE HAUSA NOVEL

Zaku tura kudin a
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank
Sai shedar payment dinki a????????????
08184017082
Kokuma katin waya na MTN anan????????
09134848107
[1/16, 2:58 PM] +234 808 457 6211: DM 16
Hannah ce tayi Dan knocking dakin so biyu kafin ya tura kofar suka shigo tana Dan nuna kulawa ta qarasa gurin hanifan tana ajiye bowl din hannunta kan table tana cewa”
Ohh sister in-law sannu da jiki tun dazu naso shigowa kaina Yana Dan ciwone shiyasa ban shigoba ya jikin?
Gyada Kai Hanifa tayi tana cewa”
Alhmdlh naji sauki thank you.
Dagowa tayi ta kalla Marshal din Yana tsaye da hannu cikin aljihu ganin hanifance kawai a dakin yasashi zaunawa ahankali kan sofa Yana kallonta da fararen idanuwansa ya bude Baki cikin kulawa yace”
Yaya jikin?
Ina tare da dad yau duka sai yamma nasamu kaina,
Dr sa’id yamun bayanin komai Yace hadda sanyi yana Miki yawa meyasa bazaki daina kwana da AC ba?
Murmushi ta ‘dan saki tana kallonsa yanda koyaushe yake tamkar shine yayan sbd irin tasa kulawar.
Gyara zama tayi tana kallonsa da sauran rashin kuzari a muryarta tace”
Ina kiyayewa Marshal.
Jeho kanta Hannah tayi cikin zancen da cewa”
Sister in-law Allah yabaki lafiya duk mundamu dake bamason ganinki cikin irin yanayina ciwo musamman Marshal he cares for you so…….katsewa zancenta yayi yawu na neman zubo Mata daga Baki tayi saurin hadiyewa sbd idanuwanta dasuka sauka Kan kofar toilet da aka bude Naj ta fito daureda towel sky blue me haske cinyoyinta dasukafi komai tada hankalin Hannan sai daukan ido sukeyi tayi sama da idanuwanta kan qirjinta dasuka fito Dan fito ta saman koina jikinta daukan ido yakeyi gashinta daure a tsakiyar kanta ta dauresa da Banda gabaki daya Bata lura dasuba Dan batasanda suna dakinba Dan hakan taqarasa fitowa Kai tsaye ta rufo toilet ta nufi closet tana cewa”
Hanifa ruqayyat takawo wankin kayan da aka dauka jiya??
Tsit dakin yayi musamman Hannah data waiwayo da sauri ta kalli marshal din taga idanuwansa basa kan Naj suna kan wayarsane ta kalla Hanifa da ita Kuma Jalal din take kallo Dan kuwa akan idonsa sak Naj ta fito Kuma ta tabbatarda ya qarewa Naj din kallo sak kafin ya basar ya dauke Kai.
Da sauri Hannah ta miqe tana cewa”
Umm Naj Ashe kina ciki bamu saniba sorry Bari mukoma Palo zamu jira ki Gama shiryawa tukuna.
Wuta Naj ta dauke tareda waiwayowa cikin tsananin mamaki da takaici ga sabon baqin cikinta ba Hannah ce kawaiba akansa idonta ya sauka daidai ya dago zai miqe ya fice idanuwansu suka shiga cikin na juna ta dauke idonta suna sauyawa kin wani irin baqin ciki da kunya da takaici lokaci daya suna taso mata ta juya Kai tsaye Takoma toilet din daukeda kayan barcin data fitar zata saka a hannu.
Kodata Gama shiryawa ta fito basa dakin sun tafi har Hanifa Bata dakin tana dakin hajjo taredashi da hajjon suna magana sbd gobe zai koma duk yanda taso kasa Masa maganar Naj din kasawa tayi ta kalli fuskarsa dake fresh Kamar wani Dan baby hankalinsa nakan hajjo Yana sauraron bayanin datake Masa akan dawowarsa yanzu akan lokaci sbd akwai nauyin iyali akansa.
Marshal bazakai magana da itaba kafin ka wuce?
Kaji koda akwai wani abun datake buqata?
Shiru sukai suna jiran Jin amsarsa saisukaga ya miqe Yana kallon agogon hannunsa yace”
Zanje na kwanta gobe zantashi da wuri.
Kofa ya nufa hajjo tace”
Goben ka tabbatarda kayi mgn da ita kafin ka wuce.
Da umarni tayi maganar ba wani Wasa acikinta shiyasashi Dan dakatawa batareda ya juyoba kafin ya taka yafice Hanifa na bayansa tana sake Dan saka Baki a maganar.
Sam ba irin wannan auren yasoba Wanda kowa zai ringa shiga tsakanin mu’amalarsa da matarsa sbd yanason yayi nutsatsiyar rayuwar aure Mara hayaniya da soyayyarda baya buqatan shigan wani zancen,
Ya lura zata ringa hada Masa tarin mutane acikin rayuwar auren Wanda baya buqatan hakan Amma zaiga tsarin dazai dauka.
Koda ya Isa sashensa Saida yakuma wanka da ruwan dumi kafin yayi Shirin bacci ya kwanta.
Bacci me qarfi da dadi itama yau tayi shiyasama tayi lattin tashi sallar asuba Dan sai guraren qarfe bakwai ta bude idanuwanta dake tareda sauran bacci ahankali tana Dan motsawa ta lumshe ido sbd Jin sabon qamshin daya Shiga hancinta ta tashi zaune tana ‘yar miqa botiran gaban rigarta uku na sama suna budewa sbd miqar datai ta zuro qafafunta qasa tareda miqewa tsaye idanuwanta suka sauka Kan mutum a tsaye cikin dakin Yana kallonta jikinsa sanye da Prada-gabardine straight leg trouser brown sai White spread collar long sleeves gabaki daya dakin ya gauraya da qamshinsa fararen idanuwansa ya zuba Mata akaro suna yawa ajikinta sbd tunda aka daura Masa aure da ita ake maimaita kalmar girmansa datai Wanda haryau yakasa ganin wani Abu dayake tunanin ya girme Masa
A taqaicema kallon dayake Mata yasa yake qara ganin zamtowarta qasanshi.
Kallon dayake Mata yasata dakatawa daga wucewar datasoyi ta shige toilet saita nufi kofar ficewa daga dakin zata fice bacin ran dake ranta Yana bayyanuwa kan fuskarta akaro na farko da mace ta wucesa tabarshi tsaye
Kai tsaye ya damqi hannunta tareda dawowa da ita baya ya tsayar da ita gabansa fuskarsa a hade tsaf ya kalli hannunta datake kokarin fuzgewa a fusace batareda tace komaiba Dan bazata iya bude Baki Tai Masa mgna ba Sam,
Ba wani riqo yayi Mata ba Amma gabaki daya takasa qwacewa ta dago a fusace ta kalli fuskarsa idonsa cikin nata ta janye idonta Kai tsaye tace”
Meye hakan?
Kabar hannuna.
Wannan auren ba wani aureneba kamar kowanne dazai baka Daman tabani so can u get your hands off me.
Sabon kallo yayi Mata Jin abindata fada daya basa mamaki Dan baiyi tunanin zata iya magana Haka ba.
Fizgota yayi ta Fado jikinsa ya dago shanyayun idanuwansa ya zuba Mata Yana kafin ya kalla kirjinsu daya manne Dana juna tana ganin hakan ta qwace da qarfi cikin tsananin bacin rai tareda turesa da iya qarfinta yayi baya ya zube kan gadon dakin kafin ta juya ya janyota tafado jikinsa daidai turo kofar Hanifa data shigo dakin Hannah na bayanta Jin shiru sbd dama itace ta fito din tace yashiga Naj din na ciki Dan wucewa zaiyi.
Da sauri a firgice Naj ta waiwayo kofar tana kokarin tashi daga jikinsa idanuwanta na cikowa da hawayen baqin ciki da bacin Rai
Hanifa kuwa juyawa tayi da sauri tana cewa”
Sorry sorry.
Hannah kuwa da sauri ta qaraso gurin tana Kama Naj dakeson tashi tana cewa”
Bari na taimaka Miki.
Sakinta yayi yana tashi daga kan gadon Kai tsaye ya fice daga dakin Yana duba agogon hannunsa sbd lokaci dayaso shige Masa Bai luraba.
Hajjo Kamar koyaushe idan zai tafi har mota take rakasa itada Hanifan Haka suka fito Hannah na gefensa tana fada Masa irin yanda zatai missing dinsa a can harabar gidan ya tararda Dad Alfa dazasu fita tare tareda mum Malika daketa zuba nata iyayin na zatai kewarsa matsayinta na uwa.
Gidansu Naj yashiga tareda Hanifa yaje yayiwa umma bankwana tareda bar Mata abindaya Saba Bata duk yazo idan zai koma hakama Dadah wannan karon kyautar dataso firgitata yayi Mata kafin yafito tareda Dattijo suna maganar Yana sanar dashi abar Naj din taci gaba da aikinta idan tanada ra’ayin.
Motarsa data sojojinsa lokaci daya suka tashi sukabar kofar gidan wasu na ‘yar murnar zasu samu ‘yancin unguwa zakai iskancinsa cikin anguwa yanda kaga dama ka tada hayaniya da rigima son ranka tunda sojojin Marshal sun tafi sojojin dake tsoron gidan basuda muguwar fitina da ikon wahala Kamar na Marshal din matuqar Yana gari ko Rigima da fada andaina a layin Dana bayansa sai Kuma suntafi Dan Haka yau kowa yayi yanda yaga dama.