DEEN MARSHALL COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

DEEN MARSHALL COMPLETE HAUSA NOVEL

MAMUH

ZAFAFA BIYAR 2022????

NANA HAFSAT(MISS XOXO)
SO DA ZUCIYA

SAFIYYA HUGUMA
DABI’AR ZUCIYA

MAMUH GEE
DEEN MARSHALL

HAFSAT RANO
HALIN GIRMA

BILLYN ABDULL
TAKUN SAKA

Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka????????
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

Zaku tura kudin a

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Sai shedar payment dinki a????????????

08184017082

Kokuma katin waya na MTN anan????????

09134848107

DM 31
Ahankali ta sake hannun Hanifar tana komawa ahankali ta kwanta sbd Jin hanifar tafara tunanin akwai dalilin dayasata batason ta zauna din tareda ita,
Har cikin zuciyarta tana Jin zafi da takaici tareda tsananin kunyar Hanifa ta Dan samu alama ta fahimta koma hasahsen wani Abu yafaru a dakin,bama dakin ba kawai a tsakaninta jalal din gabaki daya
Abune mafi kunya da tozarci gareta idan Hanifa tasan wani Abu gameda hakan,bazata taba Bari wani yasan wannan tsausayi da qaddarar data hau kantaba.

Ajiyar zuciya Hanifa ta sake cikin kulawa ta tako ta matso gaban gadon ahankali ta gyara Mata rufarta tana cewa”

Shikenan kiyi baccin zanje Nima na kwanta Dana tashi zandawo na dubaki.

Gyada Kai tayi ahankali tana rufe idanuwanta tareda gyara kwanciyar kanta a pillow.
Sai dataga fitar Hanifan ta saki Dan qaramin numfashi tana sake komawa baccinta dayake idanuwanta har lokacin.

Bacci tayi Sosai Bata fitoba Wanda yasa hajjo nacewa zancen tabbas Naj ba lafiya take ba Dan Haka Babu sanin Naj din tasa Hanifa takira Dr sa’id Wanda baizo gidan ba sai yamma bayan yataso daga asibiti.

Dagashi sai ita ya Mata Yan tambayoyi tabasa amsa a Dan gaggajarce sbd son qin bada hanyar dazata saka koshi ya Dan gane wani abun
Shima Bai wani zurfafaba sbd gane zazzabin tun ranarda Marshal yakirasa acan gidansane Bai Gama sakinta musamman idan sake kusantarta akai Wanda hakan ke nuni da Bata taba saduwa da kowane namijiba hakama Bata budeba ta hanyar tsallake tsallake da yawace yawace Wanda yake ragewa budurcin mace qarfi shiyasa take wannan wahalar Dan Haka Bai zurfafa tambayaba ya Bata maganin dazasu taimaka Mata nasu zazzabi da pain relief ya miqe Yana Dan kallonta yace”

Inshallah zaki warware zuwa gobe ko jibi idanma dai kinji bakyajin daidai har lokacin Zaki iya kirana kokuma ki sameni asibiti saimuyi waeu dube duben mugani Amma dai Inshallah ma Zaki warware din zuwa gobe.

Hajjo takira Masa ta fito tana kallonsa tana qarasowa tana cewa”

Dr sa’id zaka tafi?
Kagama dubatan?
Bansan menene wannan zazzabin sanyin dayaqi sakinta ba tun dawowarta na fahimci batada lafiya Amma tace sanyi ne,
Kuma anyi maganin sanyin kwana biyu yau Kuma abin yadawo.

Dan murmushi yayi Yana cewa”

Nabata magana Inshallah zata warware zuwa gobe
Ba wani ciwon daga hankali bane zazzabine kawai sai gabobi da zasuyi ciwo dama, ALLAH ya Bata lafiya Zan tafi hajjo idan kwana biyu zazzabin Bai tafiba nace ta sameni asibiti.

Ok Inshallah Dr sa’id,
Agaida gidan dasu hajiya.

Zasu shi Inshallah.

Ficewa yayi daidai fitowar Hanifa data fito daga kicin tagama ciyo wainar fulawar dataji kwai wadda umma ta Aiko Mata,ta qaraso palon ta zauna gefen Hanifa tana kwadawa ruqayyat Kiran takawowa Naj Naman Hantar datasa ta dafa Mata dazu tareda ruwa Tash magani.

A gabanta ta ajiye Mata Kan table Takoma takawo Mata ruwa marasa sanyi sosai Dan kaidar Naj dinne Bata Shan ruwan sanyi sosai.

Ahankali takeci sbd ya ‘dan yimata Dadi dan yajin da ya ‘danyi sbd bakinta da baida apatite na zazzabin,
Taci sosai Saida cikinta yacika Tasha maganin da Dr sa’id yabata tasake dorawa da Ginger tea me zafi
Ahankali taji jikinta ya Dan Yi Mata Dadi tasamu kuzari dakuma zazzabin daya sauka.

Ahankali ta kalli ruqayyat dake dauke kayan data Gama cin abincin tace”

Ruqayyat idan kinkai kije dakina ki dauke zanin gadon Dana cire Yana Nan Kan kujera kikai laundry.

Yes Ma.” Ruqayyat din ta furta tana Kai kayan kicin tadawo ta nufa dakin Naj din ta kwaso zanin gadon ta fito.

Miqewa hajjo tayi ta nufa hanyar dakinta sbd kiran sallar magriba da aka fara daidai ruqayyat na kawowa da kayan zata wuce Hanifa tadawo daga dakinta dataje dauko Abu ruqayyat na giftawa gabanta ta kalleta cikin mamaki tace”

Ruqayyat wannan beddings din Marshal ne?me sukeyi a hannunki?
Ta Yaya sukazo hannunki?” Taqarasa fada tana sake shaqar qamshin Dake tashi ajikinsu kamar yanzu ya kwanta akai.

Hajjo ma dakatawa tayi tana kallon ruqayyat Jin abinda Hanifa ta fada Dan dai tasan Babu me shiga sashen nasa a taqaicema namijine me aikinsa dayake Masa gyaran sashensa da wankin kayan zanin gadonsa da komaiba.

Da sauri cikin tsananin tsoro da girmamawa ruqayyat ta kalli Hanifa tace”

Anty wannan da dakin Ma’am ne tace akai laundry ba na Sir Marshal bane.

Rintse ido Naj tayi zuciyarta na Shiga takaici wannan al’amari gashi ba damar tasa Baki tabada kanta dan Haka Tai shiru tana fatan ruqayyat din ta wuce ga hajjo ma datake saurarensu sbd Jin sunan Marshal Dan gskia ba’a Wasa da harkan Marshal ko bayanan ba’a yin abinda akasan bayaso.

Qamshin turensa ne yake tashi a kayan Nan sosai kin tabbata Wanda Naj tace ki dauko ne a dakinta,
Bafa sashensa tace kijeba a dakinta take nufi……..

Da sauri ruqayyat tana sauke Kai tace”

A dakinta na dauko wlh
Acan ya kwana shine zanin yake qamshin,
Wlh banje sashensaba a dakin Ma’am na dauko.

Wata irin wuta Naj ta dauke zaune agurin wani zafi na huro Mata tako Ina ta dago ahankali zuciyarta na gaurayuwa da daci ta kalli inda hajjo take taga Bata gurin Dan tunda taji Ana neman tada sallah ta shigewarta Bata tsaya Jin zancenba tunda ga Hanifa.

Rufe ido tayi wani Dan sauki saukinda baida wani amfani na shigarta ganin hajjo bataji me ruqayyat din tafadaba
Taqi waiwayowa ta kalli Hanifa datai Kamar bataji me ruqayyat din taceba duk da ta girgiza matuqa dajin zancen ruqayyat din ta fuske tana cewa”

Wuce kije aikin gabanki kardai ki kuskura Koda aike kije sashensaba batareda iziniba.

Ruqayyat na barin garin hanifar Bata waiwayoba tayi dakinta tana cewa”

Naj Bari nayi sallah kafin na zauna.

Rufe ido Naj tayi tana dafe Kai cikin tsananin hali,gabaki daya zuciyarta ta cike da damuwa da bacin Rai tana zamanta cikin kwanciyar hankali da rufin asiri kame kame da boye boyen bacin Rai yaganta,wane tashin hankali da damuwa ne wannan¿Bazata iya cigaba a hakaba kunya da baqin ciki zasu iya illatata kawai zata daukarwa abin mataki wlh kanta bazai iya daukan wannan ba.

Miqewa tayi ta nufa daki a sanyaye itama tayi alwala tayi sallah tana idarwa ta miqe ta nufi gaban madubi sbd abinda ta hango.
Sai alokacin idanuwanta suka gane Mata katin bankin Dake daukeda sunansa JALALUDDEEN ALFA da wayarta a gefe aje.
Wani sabon mamakinsane ya kamata ta kalli takardar dake daukeda pin na katin ta yamutsa fuska tana rintse ido tareda dafe goshinta sbd kanta dake sake daukan ciwon haukatata da komai nasa ke Naman yi,
Me hakan ke nufi daya bar Mata katinsa?
Ya dauki nauyintane da dawainiyarta sbd ya karbi auren kokuma zai karba kuwa matsayinsa Miji yake son nunawa?to ita Bata karba ba Kuma batajin zata iya Dan Haka ta hada katin da paper din ta nufi wardrobe ta bude safebox dinta ta bude ta jefa ciki ta rufe tareda rufe wardrobe din gaba daya tadawo ta zauna da wayarta a hannu tana kunnawa saiga massages suna shigowa kusan duk na Sarah ne saina Abbas Wanda ko budesu bataiba ta gogesu tana Danna Kiran Sarah.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button