DEEN MARSHALL COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

DEEN MARSHALL COMPLETE HAUSA NOVEL

To ki amince da Abbas kawai ayi auren Nan idan ba hakan bane Najma sbd idan dukiya da rayuwa ne Abbas din yanadasu Kuma Yana tsananin sonki idan harkin daukeni mahaifiyarki…..

“Umma kadaki Bari fushi yasa ki lalata rayuwar Naj mana.” Anty Amina ce ta fada hakan tana isowa gaban umman Wanda idanuwanta suka rufe gabaki daya.

Naj kasa cewa komai tayi sai idanuwanta dake kan umman sunyi jajir ahankali ta dauke idonta ta bude Baki tace”

Zan aura Abbas idan har hakan Kika zabarmun.
Juyawa tayi ta fice daga dakin gabaki daya tana shiga dakinta wayarta kawai ta dauka ta fito ta fice.

Dadah dake zaune tsakar gidan tana Jin duk hayaniyar tasu farin ciki yacika ranta tunda tasan yanzu Kam Naj din bazata bada matsalaba tunda Zuciyarta ta karye da abinda umman tayi Dan Haka ta tashi Takoma dakinta a Daren zata fadawa Dattijo ya sanarda Abbas ya sanarwa iyayensa za’a matso da bikin Nanda sati uku ko biyu ayi ayi kowa ya huta Dan kaf zuriar gidan Naj din ce kawai ta riqe a gabansu batai aureba da wuri.

MAMUH

ZAFAFA BIYAR 2022????

Ina masoyan Kuma mabiya littaffan zafafa biyar wainda sukai fice gurin kawo muku littafansu masu tsafta da ilimantarwa tareda nishadantarwa,
Wannan shekarar sun dawo muku da wani sabon salon Kamar kowane zuwan inda suka kawo muku dada’dan labaransu da bazaku taba Dana sanin biya ba,

NANA HAFSAT(MISS XOXO)
SO DA ZUCIYA

SAFIYYA HUGUMA
DABI’AR ZUCIYA

MAMUH GEE
DEEN MARSHALL

HAFSAT RANO
HALIN GIRMA

BILLYN ABDULL
TAKUN SAKA

Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka????????
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k

Zaku tura kudin a

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Sai shedar payment dinki a????????????

08184017082

Kokuma katin waya na MTN anan????????

09134848107
[1/14, 3:33 PM] +234 901 771 2720: DM 7

GA CHANNEL DIN DAKE YOUTUBE NAN????????

https://youtube.com/c/sudaiskura

Sudais is a young boy who has passion in recitation of the Holy Qur’an at a very young age.

Please help him grow his YouTube channel by subscribing and liking his videos to encourage the little boy.

PLEASE SUBSCRIBE


Kodata dawo Hanifa tasamu komawa bacci Dan Haka Kai tsaye toilet ta Shiga tayo alwala tafito ta tayarda sallah.
Tana idarwa Shirin kwanciya tayi Dan batajin tanajin yunwa har zata kwanta ta fito ta nufi dakin hajjo
Tana Shiga kallo daya hajjon tayi Mata ta karanto yanayinta cikin kulawa dakuma tsananin qaunar data kewa Naj din tayi Mata hannu datazo ta kwanta kan cinyarta
Naj din ta qarasa ta kwanta qasa tareda Dora kanta kan qafafun hajjon ta rufe ido ahankali tanajin zuciyarta na samun nutsuwar data kasa samu daga gurin iyayenta.

Saidata fara bacci ahaka kafin hajjon takira sunanta ahankali tace taje ta kwanta a godonta
Ta bude idanuwanta tareda tashi zaune ahankali ta miqe tana cewa”

No hajjo zanje na kwanta da Hanifa sbd jikinta.

Shikenan kije Saida safe kiyi bacci karki saka damuwan komai aranki Allah ya tashemu lfy.

Amin”tace tana ficewa dakin.

Washe alhmdlh daga ita har Hanifa lafiya kalau suka tashi Hanifa wuyanta ya sake Takoma garau dinta dama Haka take yanzu lafiya yanzu ciwo,kokuma yanzu ciwo yanzu lafiya.
Itama sakayau ta tashi ba wani yanayi na damuwa kokuma dake nuna tana cikin wani hali sbd ta riga ta yarda ta yanke shawaran auran Abbas Dan Haka ta kauda bayyana damuwa a fuska da yanayinta sbd hajjo da Hanifa dasuka samu saqon an saka ranar auren an maida sati uku masu zuwa Wanda dad din Hanifan ne yakira hajjon ya sanar Mata sbd Dattijo ya kirasa ya sanar dashi Dan komai na harkan auren Naj da dad din akeyi sbd suna basa girmansa da matsayi na uba agareta sbd baitaba banbantataba da yarsa Hanifan tun daga karatun primary kuwa har zuwa yanzun.

Ranar bataje aiki bama Koda hajjo ta zaunar da ita akan maganar auren ta tambayeta akan tafada Mata gaskia idan batada ra’ayin auren Abbas din tasa dad yayi mgn dasu Dattijo a fasa
Tacewa hajjon ta amince da auren Abbas da raayinta ba Dole su dattijon sukai Mata ba.
Hanifa ma tayi tayi akan suyi maganar Amma tace Mata subar maganar ayi auren ahuta.
Dole suka haqura sunaji suna gani aka hau fara shirye shiryen auren gadan gadan.

Tunda aka fara wannan maganar Bataga ko shigowar saqon Abaas dinba a wayarta bare kiransa Wanda Bai wani dameta ba sbd tasan dama za’ai hakan Dan Haka ta tattara dukkanin alamarinsa ta cire akai ko a office Basu hadu ba sbd dama gabaki daya Bata zuwa office dinsa shine me zuwa nata to tunda yaga tagama shigowa hannunsa tunda zata zama matarsa saiyayi watsi da ita shima saima wani basarwa yakeyi a yanda Sarah take fada Mata yasa dokar shigar maza office dinta matuqar ba’a zo anfara tambayarsaba Koda kuwa aikine.
Hakan ya Bata mamaki sbd kaman rashin tunani yashigo al’amarin nashi Dan hakama Ana saura sati biyu bikin tafara hutun bikin auren dazatayi ta daina zuwa office.

Gidansu kuwa sosai da sosai aka hau shirin wani irin gagarumin hidima sbd bikinta kowa yasaka Masa burin holewa tunda sunsan za’a kashe dukiya sbd alaqarta da gidan tsohon marshal Alfa shiyasa suka hau shiri da anko anko na biki kala kala Wanda ita amaryar ma gabaki daya komai baya gabanta mamakinta daya har lokacin Abaas Bai taba kirantaba.

Dadah kuwa farin cikinta da murnarta a bayyane suke ba wani shamaki sai ji takeyi da Naj din tana lallabata hakama Dattijo manyan kudi tako Ina sai shigosa sukeyi sbd Alfa ya sakar Masa kudin hidamar auren fiyeda tsammani ga hajjo ma data tanadarwa Naj dukiyar aure ta musamman shiyasa kowa sai qara rikicewa yakeyi da harkan bikin.

Ummarta tuni tahau aikin gyaran ‘yarta sbd dama gyaran amare aikintane Dan Haka yanzu da Abu yake nasu ba kissa ko kadan gyaran Naj din takeyi ta ciki ta waje abinka da kyakkyawar farar mace tuni tafara sauyawa sosai Dan kuwa har wani daukan ido takeyi.

A duniya qawayenta biyu ne daga hanifanta sai Sarah Dan Haka kullum Sarah na gidan sunata shirye shirye Wanda Hanifan ce ke komai itadai nata ido da Kuma Dan murmushin yaqe Wanda babushi ko kadan cikin zuciyarta.

Saida akai saka lallenta kafin aka kawo kayan lefe mota biyu Wanda yasa gidansu yasake daukan bidiri suna sake yadda da Naj dama me kudin ta tsaya jira duk da hakan dai sudai sunyi murna musamman ummanta data ringa sadaka tana ciyar da mabarata sbd Allah yasa wannan karon ‘yarta tayi aure.

Ba gidansu Naj din kawaiba ya cika da baqin nesa Dana kusa ba hatta gidan Alfa yasamu saukar isowar Dad Alfa din tareda matarsa da sabbin masu aikinta datazo dasu har guda biyu sai babba ‘yar yayarta datake riqo tun tuni wato HANNA Wanda take wata irin wayayyiya datake ji da kanta da Kuma kyau da Allah yayi Mata itama wadda asalin irin son datakewa  Marshal Deen ne yasa tadawo hannun mum Malika saidai hakan be wani taimaka ba sbd takanyi shekara Bata ganshi ba duk da kuwa iyayen nasu sunsan da maganar so a tsakaninta da marshal din Dan Yana kulata ba laifi shiyasa akeda maganar da yiyuwar aurensu gashi Kuma yanzu sun dawo gida gabaki daya da zama tasan yana zuwa Nan akai akai fiyeda can gurinsu sbd Hanifa da hajjo Dan Haka Suma gidan yanzu zai rayu tunda su dad din sun dawo.

Sai yamma sosai Naj tasamu damar fitowa gidansu ta tafi yiwa dad Alfa sannu da zuwa kodata fita mutanen dake waje sai binta da kallo sukeyi sbd yanda tasake wani irin washewa
Tsakani da Allah dai kowa ya kalleta saiyace Abbas yayi dace da kyakkyawar sa’a.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button