DEEN MARSHALL COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

DEEN MARSHALL COMPLETE HAUSA NOVEL

Harta kammala sallar azahar data la’asar da aka gama idarwa lokacin Basu Gama wayarba wadda fiyeda Rabin harshen zancen turanci ne Hanifan keyi Dan Kamar yafi Kama bakinsa yanzu fiyeda hausarsa bugu da qari ma duk rayuwarsa yanzu idan Basu yakira bama baida Wanda zai Kira suyi yaren hausan sbd dad dinsu dai Yafi zama yanzu a Angola sbd tun wasu shekarun aiki da yayi acan bayan rasuwar mahaifiyarsu ya auri wata Yar can wadda gabaki dayama Bata wani Jin hausa Saida tahadu dashi ne ma tafara koya harta iya bayan auren danshi yasa ko dad din yakira sbd duk sun sama zama da yare yanzu Basu wani cika Yin hausar ba sai dai idan sun Kira su Hanifan da hajjon.

Kwashe dadduman tayi ta nade tareda zare milk hijab din datai sallan ta ajesu cikin wardrobe ta juya ta nufa water dispenser dake dakin nata Dan Shan ruwan dumi kawai ta matso ruwan dumi cikin cup tadawo ta zauna kan kujera tareda bude laptop dinta tana Sha tana duba saqon datace Sarah taturo Mata ta email.

Tana cikin aikin wayarta takawo haske tana vibrating ta dan kalla wayar ahankali da idanuwanta dake bayyanarda Bata buqatan Kiran kowa a lokacin taga sunan Dr sa’id ajikin wayar take ta saki ajiyar zuciya siririya sbd bazata iya sharesa ba kokuma nuna qosawarta dashi din sbd tsananin mutuncinsa datake gani dakuma yanda shima yake matuqar mutunta dakuma kulawa da ita.
Kallon Hanifa dake waya har lokacin tayi kafin ta dauki wayar tana amsa Kiran cikin taushin muryarta me zallar daukan hankalinsu sbd nutsuwa wadda sukafi daukanta da Jan aji tace”

Barka Dr sa’id.

Murmushi yasaki me Dan qaramin sauti daga nasa bangaren sbd yasan iya gaisuwarta kenan akoda yaushen
Ita bame hayaniyar surutu bace Dan Haka cikin taushin murya shima yace”

Kinbar office kokuwa na biyo na kaiki gida?

Ajiye cup din hannunta tayi bayan ta qarasa shanye ruwan tana kallon screen din laptop din gabanta tace”

Nadawo tun kafin time din tashina yayi sbd Ina fama da Dan ciwon Kai
Thank you.

Ajiyar zuciya ya sauke boyayya kafin yace”

Sorry,
Ki huta to idan natashi Zan biyo na dubaki…..

Cikin nutsuwa ta katsesa da cewa”

No kadaka wahalan da kanka gurin zuwa ba stress ne kawai na Dan meeting din danayi Amma yanzu yariga ya wuce.

Ko Naj Bata fadaba yasan damuwan fitanar Abaas ce bataso Dan ya tabbatarda fitarsu jiyan saita kusa zautarda Abaas din Wanda shi tuni ma yake Masa kallon Mara lafiyar qwaqwalwa Dan wasu abubuwan dayakeyi sunfita daga dabiun lafiyayyun mutane,
Kishinsa na hauka ne bana mutanen dasukasan kansu bane,
Fitinarsa ta marasa ilimi da wayewa ne kamar wanda baida ilimin da wayewar,
Shi gabaki dayama ya rasa ta Yaya Macen datake da tsananin aji da sanin darajar Kai tareda wayewa irin Naj ta yadda da auren namiji kaman Abaas lamido,
Ta Yaya Allah yabashi irin wannan sa’ar me girma ta samun Naj amatsayin Mata.,
Shi Yana tsananin son Naj tareda sanin qimarta Dan Haka bazai taba cire Rai ga samunta ba matuqar ba aurenta aka daura din ba da Abaas shiyasa ma duk haukan Abaas din Bata damunsa Dan bayama gabansa shi Naj din ce kawai a gabansa Dan kuwa irin son dayake Mata idan ya aureta zai maidata sarauniyar rayuwarsa Dan kuwa zai tattaleta tamkar ita kadai yakeda ita a duniya.

Kashe wayar tayi tana ajewa daidai itama Hanifa na aje tata wayar ta dawo gurin Naj din ta zauna tana janye laptop din gefe tareda rufewa tana cewa”

Naj zamuyi mgana akan Abaas.

Fararen idanuwanta ta zubawa Hanifan tana cewa”

Wai Ni rayuwata shikenan kullum akan maganar rashin aure yake?

Ahankali Hanifa ta girgiza Mata Kai tana riqo hannayenta duka biyu cikin kulawa da tsananin qaunarta tace”

My beautiful Naj tasan cewa bantaba damuwa da rashin aurenta ba sbd nasan aure lokacine dashi Kamar mutuwa ta yanda idan lokaci yayi Babu mai hanawa ko tarewa,
A zuciyata dakuma adduata kullum shine Allah yasa wannan jingikirin yazamo babban alkhairi agareki,
Wlh banajin dadin yanda su dattijo da su Dadah suka sakomin ke gaba akan rashin auren Nan gashinan umma itama tabisu tana tsangwamanki da rashin aure.

Sai alokacin tasaki wani kyakkyawan murmushi tana kallon kyakkyawar fuskar Hanifan tace”

Bana damuwa da dukkanin zancensu na rashin auren
Koba komai Baga Abaas Nan ba tunda sun saka auren 4month masu zuwa ai zancen ya mutu yanxu Ina Dan samun sauqinsu.

Bata fuska Hanifa tayi tana cewa”

Abaas lamido bazai taba auren Naj Dina ba matuqar bazai sauya hali ba.

Murmushi me sauti Naj din tayi tana riqota da murmushi akan fuskarta tace”

Kuma Kinga as long as Hanifan Naj bata Aminta dashiba Naj bazata taba aurensa ba.

Dariya suka saki lokaci daya sbd yanda haryanxu suke irin wannan wasar wa junansu
Hanifa tace”

Alqawarine ai kidainma Wasa da zancen,
Inshallah nice Zan tayaki zaban mijin danasan zai darajanta min ke tunda idonsu umma ya rufe Akan kowa Kika samu ki aura nikuma bazan yadda ba taqarasa tana ‘yar dariya,
Kinga dama shima Marshal nafada Masa Ni Zan tayasa tantance Matar dazai aura sbd shima shine ya tsaya akan nayi aure da wuri sbd yanayin qarancin lafiyana kema kece Kika tsayawa Isma’eel sbd lokacin amininsa arfat yakawo kudin aurenki Kika ci amanata Kika bi bayansu Saida ya aureni da yanzu lukuman ne mijina ko?
Dariya suka kwashe da ita su biyun suna tunano lokacin musamman yanda Hanifan Bata wani so auren Isma’eel din ba Amma da hajjo da Naj din suka hade Mata Kai gurin Dad dinsu akai auren sbd dama ya dade Yana Sonta tun suna secondary school sbd ‘dan yayar dad din nasu ne
Shima Marshal Isma’eel din yafi kwanta Masa sbd yasanshi sosai Yasan halayensa ba laifi Kuma shi Dama Wanda zai iya kulada Hanifan da lalurarta yake muradin ta aura din shiyasa.

Dan qaramin mayafi Naj din ta Dora akanta suka fito daga dakin har lokacin Fuskokinsu dauke suke da yanayi na dariyar tuna baya dasuka samu kansu
Anty Amina ta kallesu tana cewa”

Hanifa ki fadawa hajjo yau ba hirar dare saidai gobe kayan umma dazata aika sako abekuta zamu hada.

Anty Amina wannan fira taku keda hajjo ai yau kuwa zatayita mitan rashin firar Daren nan dakuke.

Fita sukai umma dai da guntuwar harara tabisu da ita Dan sun kasa gane abinda yake cin ranta,
Tsakani da Allah ‘yarta Kamar Naj wadda kaf gidan tafisu ilimin Boko da wayewa tareda abun duniyama ace anyi sadakarta ga duk me rabo idan Batai aureba wlh zata mugun cutatuwa Dan kuwa ciwon zuciyama kamata zaiyi Amma hanifar datakeson ta karkato Mata Naj din tamafi naj din kasa fahimtarta tana ganin Kamar sun takurawa Naj din.

Dakin Dadah suka nufa tun Basu qarasa ba ta tsuke fuska Dan tana zaune kofar dakin kan kujerar roba da qaton farin glass dinta.

Dariya Hanifa tasake tana qarasawa gabanta da cewa”

Dadah my love.

Uwar harara dadar ta sakar Mata tana hararar gefen Naj tace”

Yaudarata za’a kenan?

Da sabuwar dariya Hanifa tace”

Mezaisa na yaudari Dadah me ran qarfe¿
Kawai dai dama……

Cikin hanzari dakuma zallar Kokonto Dadah ta katse Hanifan da cewa”

Wlh idan har kikacemun matsala yarinyar Nan tasamu da Abbas to wlh yau daga ita har uwarta kwanan bacin Rai zasuyi mummuna kuwa
Kuma wlh gobe zuwa jibi suga ‘danyan hukuncin dazansa Dattijo ya yanke Inga qarshen Boko da wayewa…

Zubawa Dadah fararen idanuwanta Naj tayi tana sauraron kalaman bacin Rai na fada na fitowa daga bakin dadar take tahau fada me tsanani Wanda yasa umma yin tsit daga aikin datakeyi Dan tana jiyo fadan Wanda aketa zubawa har ita ba’a ragawa ba qarshe ma korarsu tayi daga gabanta tana tabbatar musu da cewan aure da Abaas anyi angama idan Kuma shiyace yafasa da kanshi wlh auren sadaka zasuyi Mata can ta qarata da kyawun idanma shine take korar maza akansa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button