DEEN MARSHALL COMPLETE HAUSA NOVEL

Team glow✅
Masu buqatan makeup ma duk mgs skincare suna kulawa da wannan ko a makeup studio dinsu kokuma a gidanka.
08062991549
Sarah binta tayi da ido tana sake qure kallonta akanta Dan kuwa duk da ita ba likita bace Amma ta taba aure harma da bari na ciki harso biyu kafin suka rabu da mijin Dan Haka tana iya ganewa ko hasashen ciki ajikin mace Amma Kuma Kamar yanda Naj din tafara batada Wanda zai Mata ciki bayan mijinta Dan kuwa tare sukai karatu da Naj qawartace ita din cikakkiyar sheda daga Nan har koina zata iya bayarwa akan nutsuwa da kamun Kai irin na Naj din to Kuma Marshal Wanda yake matsayin mijinta kowa ya iya yanda ya tabbata Babu ko gaisuwa a tsakaninsu bare su Aminta da zamansu ma’aurata a taqaice dai Babu ma wani maganar ciki da zai yiyu ajikin Naj din itama din tayi banzan tunani data Yi tunanin hakan harta fada din.
Kallon Naj din tasake Yi cikin kokarin kawar da dukkanin alamun da idanuwanta da zuciyarta ke nuna Mata a natse cikin kulawa tace”
Sorry Naj,Nima bansan tunanin daya shigeniba nace hakan kawai dai ganin yanda kike yawan Amai a kwanakin Nan ne dakuma wannan jirin dashima yake yawan kamaki,duk da hakan please Naj ki daure kiga Dr sa’id sbd Kar wani ciwon ne yake damunki yazo yayi qarfi.
Ahankali ta girgizawa Sarah din Kai suna fitowa daga office din tace”
I will be fine Inshallah,nafi tunanin ko stress ne yamun yawa so daga yau zanshiga hutu na huta sosai idan Naga Bai daina bane Inshallah Zan sanarwa Dr sa’id kokuma zanje asibitin sbd karna kirasa yazo su hajjo hankalinta ya tashi ta dauka wani babban ciwon ne.
Mota suka Isa ahankali ta bude gaba ta zauna ita Kuma Sarah ta shiga gurin driver ta zauna tareda Dan sake kallon Naj din data jinginar da Kai a rufe idanuwanta sbd baccin datakeji Yana cika idanuwanta ta sauke numfashi tana sake Kore tunanin tsananin hasken da fatar Naj din taqara zuwa kirjinta da Kamar sun Dan qara cikowa,tayi saurin girgiza Kai tana Kore tunanin abinda itama tasan bazai yiyunba wato ciki ajikin Naj bayan kowa yasan ko Gama daidaituwa auren baiyiba bare har asamu kebewa babba irin wannan dazatasa ciki a yanda Naj Babu ko alamar auren acikin kanta Dan Haka gskia ba ciki bane kawai sauyin yanayi ne.Tayarda motar tayi ahankali ta ja suka bar ALFAs.
Suna cikin tafiyar ta bude idonuwanta dake cikeda bacci ta kalli Sarah din tace”
Mu biya Bakery zansiya daughnuts idan na Isa gida Zansha da tea cake Yana dannemun zuciya idan naci yanzu kamar kwanan Nan ruqayyat idan zasuyi cake din suna cika butter ne ko kwai¿Nadai gaji dashi Zan gwada Sha da daughn din.
Ok,kokuma kisa suyi Miki ko Anty Amina tai Miki sponge cake shi bazai Miki nauyiba.
No daughnuts din nakeso dai yanzu.
Biyawa sukai wani babban bakery Basu shigaba suka nada ordarsu daga cikin Motar aka kawo musu doughnuts din cikin qaramin farin kwali me dauke da sunan gurin suka wuce.
Suna Isa gida Sarah daga harabar gidan ta juya Ta fito ta hau taxi Takoma office Naj dince kawai tashigo cikin sa’a kuwa tana shiga Dad Alfa na fitowa daga sashen hajjon ta qaraso gabansa ta gaishesa cikin girmamawa yana amsawa tareda tambayarta wasu ayyukan yace idan tasamu lokaci zasuyi mgn akan Marshal daya tsaya akan zai Saida shares dinsa a companyn matuqar Abaas yadawo.
Tana sane da wannan rigimar Dake kwance a ALFAs Dan kuwa Marshal din na janyewa Babu wani sauran nauyi sosai a ALFAs din Dan kuwa kusan Rabin uwar dukiyar tasace aciki saita mahaifiyarsu wadda kasonsane shida Hanifa sai sauran ta Dad Alfa da wasu abokanan kasuwancinsa su uku.
Ok tom Inshallah” kawai tacewa Dad din,Yana wucewa itama qarasa ciki.
A palon ta tadda Hanifa harma da hajjo data kalleta ganin lokacinda ta dawo cikin kulawa ta dago daga karatun datake a wani littafi The sacred path to islam cikin kulawa tace”
Harkin dawo ne?
Lafiyanki dai ko?
Naga idanuwanki Kamar bakyajin Dadi,qaraso zoki zauna Nan.
Kusa da ita ta nuna mata tana kallon yanayinta da duk ita ya sauya Mata a ido Nan tasake tabbatarda ba lallai lafiyar Naj din kalau ba.
Kallon Hanifa hajjo tayi tace”
Kira mun Dr sa’id.
Zama Naj tayi tana hanawa da cewan”
Hajjo lafiyata kalau wlh kawai dai rashin hutune yake damuna na wahalar aiki Amma Inshallah Zan huta kwana biyu saina ji duk wata gajiya ta sakeni Dan Haka ba buqatan Kiran Dr sa’id.
Aje qaramin kwalin hannunta tayi tana budewa tareda kallon Hanifa tana cewa”
Maman baby ga doughnut me chocolate nasan baby nason ci.
Kallon daughnuts din Hanifa tayi tana murmushi tace”
Baby batacin me chocolate saidai next time kila yanzu nagama cin fatan wake da doya da Umma ta aikomun.
Kallonta Naj tayi tana miqewa taje kicin tafara wanke hannuwanta da kyau tadawo ta zauna tana faracin daughnuts din dasukai Mata Dadi sosai.
Guda biyar ta cinye tabar biyar dan guda goma be Tasha orange juice da ruqayyat takawo Mata me sanyi har hajjo na maganar yaushe tafara shan sanyi Haka tace”
Zan daina hajjo Nima bason sanyin nakeba Sarah ce tafara koyan Sha sanyin Nan inaga a office.
Miqewa tayi ta nufi daki tana cewa”
Bari naje nayi sallar azahar nayi bacci ko kaina zai sake.
Tana Shiga daki handbag dinta tafara ajewa kafin ta nufa toilet Kai tsaye tashige tayi alwala da komaima ta fito ta dauki hijab ta saka ta tayarda sallah.
Tana idarwa hijab din kawai ta zare ta Haye gado wani irin bacci me Dadi ya dauketa take.
Bacci Sosai tayi sai yamma ta farka bayan zirga zirgar da hanifa tayita yi a dakin na zuwa dubata ganin baccin yaqi qarewa Dole ta tadata lokacin har qarfe biyar ta Dan gota cikin mamaki Hanifa tace”
Naj da gskiar hajjo fa Anya lafiyarki kalau kuwa?
Wannan baccin me lafiya bazaiyisa ba saidai me ciwo gskia.
Saukowa gado tayi ta nufa toilet bayan ta duba agogo ta shige tana Dan dafe kanta dake sarawar baccin Bai Gama isartaba.
Alwala tayo tafito har lokacin Hanifa na dakin tana zaune kan sofa tana waya mijinta.
Qarasowa tayi ta dauko hijab ta inda zata tayarda sallar ta tayar har lokacin Hanifa na waya.
Ko data idar kicin tafara zuwa ta debo abinci a plate tareda ruwan sanyi na roba a hannunta tadawo dakin ta zauna lokacin Hanifa ta Gama wayar tafaracin abincin ahankali tana cewa”
Yau bakije gyaran bane gurin umma?
Naje dazu kina bacci Amma zankoma yanzuma da yamman Nan gamaci muje Dan Nima Ina buqatan kiyi gyaran Nan tunda kema Amarya ce duk da haryanxu dai Baki zama cikakkiya macen aure ba.” Taqarasa maganar tana Yar dariya.
Qin kallonta Naj din tayi taci gaba da cin abincinta Dan sanin neman maganarta kawai Hanifan keyi Wanda ko tankawama bazataiba Dan ba zancen tankawar bane.
Tana gamawa wanka tayi ta Sanya jallabiya kawai suka nufi gidansu bayan sun sanarwa da hajjo dake dayar palon da baqi datai.
Tunda suka shigo gidan Dadah dake zaune tsakar gida ta zubawa Naj din ido tana cewa”
Masha Allah,
Wannan Ya Allah yaqara tsare Mana ita daga Baki da ido Tubarkalla Masha Allah,
Gatanan sai qara santalewa takeyi Kamar abiya kudi a taba wannan aure da ace lafiya lafiya ake da ita akan auren Kuma da ace ta tare agurin mijin ne da Babu abinda zai Hana tace cikine a jikinta Amma Ina wannan magana datake Kamar babban sa6o me zunubi agurin Najma zata fadu ko kwatantuwa Dan Haka sbd ma karsu Bata da maraicen ta tsuke bakinta ko fatarta Bata fitarba a fili ta hadiye abarta ta kallesu tana amsa gaisuwar Hanifa data wuce gaba zuwa gurin uwarta Naj kuwa gefen Dadahn ta zauna Tama cewa”