SIRRIN ƁOYE COMPLETE

Assalamu alaikum jama’a na tallatamuku hajar mu ta online/offline business dina wanda zanrin ga sayar muku da data ta mtn a sassaukan farashi Kamar haka
I selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
10GB@===2,600
15GB@===3850
20GB@===5000
40GB@===9900
Dial 460260# to check Data balance.
Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
Whatsapp OR Call 08066268951
Comment&Share.
SIRRIN ƁOYE
By Oum Ramadhan✍????
Shafin Sadaukarwa Ne Ga Duk Makarancin Wannan Littafi, Alkhairin Allah Ya Isa Gareku A Duk Inda Kuke.
30)
naji zuciyata ta motsa, ba kalmar auren da Baba ya ambata bace ta razana ni, illa sunan mutumin da yake ikirarin zan aura shi ya firgitani, mijina dai! hakan yasa na ɗago na dube shi a kiɗime jikina har na shaking, mamakin Baba yay tsalle daga zuciyata ya fito ya dira a saman fuskata ƙarara.
tunani nake anya kuwa wannan Babana ne ba wani Baban aka sauya min ba?, zuciyata ta hau tantama akan anya ƙwaƙwalwar Baba bata samu motsuwa ba kuwa?, anya Baba bai sha abinda ya gusar da hankalinsa da tunaninsa ba?, sai dai duka amsar tambayar saɓanin tunanina suke, domin kuwa naga hakan a saman fuskar Baba, Babana ne! kuma ragagas yake, babu alamar ciwo ko gushewar hankali tare da shi.
to amma ayau me yasa yake magana irin ta marasa lissafi?, naiwa kaina tambayar da bani da amsarta, zuciyata tayi wani ƙundun bala ta cure wuri guda, kafin sunan daya ambata ya haska acikin idona da kyau, ya kuma zana min hoton mutumin da kyau, yana tsaye a gabana, Emanuel! Emanuel dai!, kafirin nan da baya sallah, zindiƙin arnan da babu hasken musulunci a tare da shi, mutumin da yay sanadin halin dana shiga, mutumin da harda silarsa a mutuwar Gwaggona, mutumin da akaf duniya babu wanda naƙi jini sama da shi, Allah ya sani ko kaɗan zuciyata bata yinsa, mutumin da zuciyata ta ƙudurta duk ranar da tayi ido huɗu da shi saina ɗauki fansar mutuwar Gwaggona akansa.
ai sai bayan mutuwar Gwaggona na yarda da maganarta na cewar Arna mugwaye ne macuta maso son kansu, ashe tafi Baba hange shi da yake cewa ai kamar yanda Ubangiji ke fitar da rayayye a cikin matacce, kuma ya fitar da mutanen kirki da a azzalumai acikin musulmai, to hakama kafiran, suma ana samun na ƙwarai acikinsu, amma ita tata zuciyar taƙi amsar gaskiyar hakan.
lallai banga laifinta ba akan ƙinsu da ta ke, ashe gudun da ta ke kenan karsu dulmiyar da Ya Amadu cikin ƙazamin addininsu, da rabon ba zata shaƙi takaicin da bata taɓa kawo lissafinsa akanta ba ne, lallai mutuwa ma Rahma ce, da Allah kaɗai yasan halin da Gwaggona zata shiga idan taji cewar na rayu cikin kafirai kuma na ginu akan addininsu.
na dubi inda Inna Amarya ke zaune inda ganinta ya ma ye min gurbinta da Gwaggona, ƙwalla ta taru a idona, Allah ya jiƙanki Mahaifiyata, da ace kina raye tabbas wannan zaman ba za’ayi shi ba, na rufe idanuna dake min zafi, bayan dukkanin tarin ƙiyayyar da Baba yasan Gwaggona nayiwa su Obi, da wadda ni kaina nake musu a ynzu amma a hakan yake ambatar zai aura min shi, wai zai zama mijina, ta ya ya hakan zata kasance kenan bayan akwai haramcin aure ma a tsakaninmu?, amma tun a sanda na kalli ƙwayar idon Baba na gano abinda ya faɗa har cikin zuciyarsa yake, kuma auren da nake tunanin ba zaiyi yiwu ba ƙwayar idonsa na shaida min zai tabbata.
ci gaban maganarsa ta katse dukkan tunanin daya kutsa ta cikin kaina, na tattare komai na ture gefe, naci gaba da sauraron maganar da yake yi.
“acikin hankalina nake Mairo, kuma ki ture zargin da zuciyarki ta kawo miki akan ko kwaɗayin abin duniya ne yasa zan aurar dake ga kafirin mutumin da addininmu bai halatta aurenku ba, da ilimina, nasan abinda nake…amma ina ƙara faɗa miki Emanuel shi na zaɓa miki a matsayin mijin da zaki aura idan har na isa dake, kuma nan kusa bada jimawa ba, sai dai ko kaɗan karki zargi cewar na nemi alfarmar aurenki a wajensa ne, ko ɗaya ba haka bane, shi da kansa yazo ya sameni da maganar aurenki, kuma hatta mahaifinsa ma yazo ya sameni. su ɗin mutanen kirki ne, masu ilimi kuma manya wanda ƙasa ke ji dasu.
tun ranar da Gwaggonki ta mutu yaron nan ke sintirin zuwa gidan nan yana mana ta’aziyya, ko kin san da Amadu ya sanar masa da mutuwar a daren ranar ya sauka a garin nan, kuma da Amadu ya shaida masa yanda muke gudanar da zaman makoki, haka ya kama hotel ya zauna acan shima yace har sai an gama zama sannan zai koma gida. a washe garin zaman ɗaya yaron nan daya tashi zuwa sai ganinsa mukai da lodin kayan abinci, shinkafa babu ƴar hausa buhu goma haka ya ajiye ƴar gwamnati, banda galolin mai da duk sauran kayan abinci dai da kika san anaci, ruwan jarka na faro kuwa da kika ga kowa nasha mota guda haka yasa aka ajiye a ƙofar gidan nan, ya ɗauki maƙudan kuɗi naira dubu ɗari da hamsin ya bawa Amadu yace a dinga cefane dasu, na karɓa nace masa a’a ba zamu karɓa ba, ko waɗancan ma dan ya riga ya kawo ne ba tare da yayi shawara damu ba, kuma ba’a maida hannun kyauta baya, amma da duka za’a haɗa a bashi, dan haka ya riƙe kuɗinsa an gode.
duk yanda nayi da shi ya karɓa yaƙi yace shi bai bayar dan wai muyi bikin mutuwa irin nasu ba, ya tambaya ne idan musulmi ya mutu kyautar me ake musu akace ba’a kyauta sai dai a bada sadaƙa, dan haka shi duk abunda ya bayar ya bayar da shi sadaƙa ne, kuma wannan kuɗin idanma ba zamu riƙe ba ayiwa Gwaggo sadaƙa dasu.
ko da yaushe yaron nan yana tare damu a wurin zaman makoki tun daga safe har dare sannan yake mana sallama, tashi sallah ne kawai yake rabamu da shi, kuma haka yayta wannan zaman har akai sadaƙar bakwai, kuma a kullum tambayata yake wace iriyar adu’a muke yiwa mamacinmu, na faɗa masa, kuma tun daga wannan rana kullum sai yayi kyawawan adu’oi masu tarin yawa wa Gwaggonki, ranar sadaƙar bakwai har kuka saida ya sakani, yace yana tausaya miki ne kina ƴar ƙarama dake kin rasa mahaifiyarki, kuma an faɗa masa dalilin ciwonta harda silar rashinki a kusa da ita, kuma ba kowa yay sanadin tsayin ciwon nata ba illa shi, shima yana da babban kamaso a rasa mahaifiyarki da kika yi, dan Allah na roƙeki ki yafe masa, duk abinda yay bai aikata miki da son zuciya ba, saima dan gudun kada ki tagayyara idan yasa cigiyarki, kidnapers zasu iya yin ƙarya su ƙarɓeki.
amma ki yafe masa, yana kwatantawa ne akansa ranar da akace shima babu tasa uwar ko uban ya zaiyi. ya daɗe a ranar da zai tafi yana cewa dan Allah nace kiyi haƙuri, har Amadu yace ya tsaya a kiraki yace a’a ace yana miki ta’aziyya kawai, ba zai iya haɗa ido dake ba dan aduniyarki babu wanda kika tsana sama da shi yanzu, kuma zaki iya kashe shi dan kin faɗa masa hakan.
bayan wannan a washe gari sai gashi ya turo min mahaifinsa da maganar wai yana so ya aureki, mahaifinsa ya rantse min yay alƙawarin ba zasu cutar dake ba, kuma ba zasu rabaki da addininki ba, banbancin addini ba zaisa su ƙyamaceki ba, na faɗa masa cewar addininmu ya haramta auren musulma mace da kuma namiji kafiri, dan haka ba zan iya bawa ɗansa auren ƴata ba.
ya tafi cikin rashin jin daɗi, amma a washe gari sai gashi Emanuel ɗin da kansa yazo, a jiya kenan, har hawaye sai dai yay min akan magiyar aurenki, ban yarda da irin tsananin son da yake ikirarin yana miki har cikin zuciyarsa ba sai dana kalli ƙwayar idonsa, kuma ya faɗa min soyayyar ba wai ta yanzu bace, tun ta sanda ya haɗu dake ne, kuma inda yayi niyyar cutar dake da tuntuni ya cutar dake, dan zuciyarsa ta daɗe tana ingizashi akan ya aikata wasu abubuwa marasa kyau agareki amma ya dinƙa kwaɓar zuciyarsa saboda son da yake miki na gaskiya ne.
sai dai duk ta yanda naso na fahimtar da shi rashin yiwuwar abin ya gaza fahimtata, yace shi kawai bana so na baki shine, kuma har wata ƴar’uwarsa ya kira min a waya dan naji wace ita, arniya ce ita amma mijinta musulmi ne, saboda haka idan har auren waɗan can zai kasance kuma naku zai kasance.
da ƙyar da ƙyar yaron nan ya fahimceni daga ƙarshe, sanda ya miƙe ya tafi bakiji yanda zuciyata ta tsinke ba, da ace addininmu bai haramta auren Kafiri da Musulma ba da babu abinda zai hanani aura masa ke, ba don komai ba sai dan karamcinsa a garemu, mutumin daya zauna tsawon sati guda acikinmu ba ƙyamatarmu talakawa ne ballantana addininmu, abinda muka ci shi yake ci, kuma kullum adu’a yake ga mamacinmu, taya zaka ƙi karɓar buƙatarsa ta alkhairi agareka?.
ba wannan ba Mairo, wallahi ban rufa daga tunanin dana faɗa ba sai ga yaron nan ya dawo yana shaida min idan har zan aura masa ke to tabbas zai musulunta, nace masa a’a ni ban yarda ba, sai dai ya musulunta saboda Allah ba dan ke ba, yay min rantsuwa iya rantsuwa da gaske yake yi zai shiga addininmu idan har zai sameki, saboda ba zai iya rayuwa ba idan har babu ke a tare da shi, nace ni ba zan mallaka masa ƴata ba saboda zai musulunta dan ita ba, nafi so ya musulunta saboda Allah, ni kuma idan har ya musulunta dan Allah nayi masa alƙawarin zan aura masa ke a washe garin ranar, ta yanda zuciyarsa ba zata sauya shawara ba anan gaba bayan ya aure kin.
kuma bai ƙara cewa dani komai ba yay shiru, anan bakin masallaci muka barshi muka shiga sallar magriba, kuma har muka fito yana nan a zaune, ya kira Amadu yace yazo ya kai shi wajen limamin masallaci, Amadu shi yay masa jagoranci zuwa gaban Malam Liman, Liman da kansa yace in harda gaske wurinsa yazo to a shigo da shi cikin masallacin, ya zube gwiwonsa a gaban Liman ɗin, ya duƙar da kansa ƙasa, ya shaida masa cewa yana so ya shiga cikin addinin musulunci, ba wai dan saboda wani ya tursasa shi ba, ko kuma don bin umarnin wani, sai dan saboda ra’ayin kansa, ra’ayin zuciyarsa, saboda kwaɗayin wannan ni’imar da hasken da Amadu ya jima yana masa nasiha akansu. saboda haka a faɗa masa adadin kuɗin da zai biya ko da ya kai nawa ne, idan ma da abinda akeso bayan kuɗi a faɗa masa duka zai bayar, shima yana so ayau ya shiga cikin wannan addinin da tun wayonsa yaji ana faɗin shine addinin gaskiya.
Mairo bayan ubangiji, sannan kuma da Liman da babu shi anan, daga Innarki har Amadu shaida ne a yanzu Emanuel ba arne bane musulmi ne, ya zama cikakken musulmi tun a daren jiya kafin sallar isha’i, ya amsa kalmar la’ila ha’illahu har ƙarshenta, kuma ya amsa sunansa na Al-Mustapha.
haƙiƙa ubangiji me ikone abisa dukkan komai, Emanuel ya ƙara amsa cewar zai shiga musulunci ne tun a sanda imani ya ratsa zuciyarsa ata dalilin kalamai na wa’azi da Liman yay masa masu ratsa zuciya da ɓargon jiki.
Liman ya faɗa masa musuluncin ba kasuwanci bane, kuma ba’a biyan ko sisi idan za’a shiga addinin musulunci, saboda Allah maɗaukakin sarki ya halicci dukkan halittu ne domin su bauta masa, kuma ya sawwaƙe musu abinda zai taimaka musu na arziƙinsa. kuma Ubangiji da kansa ya faɗa a littafinsa me tsarki, surah ta (51) aya ta (56-58) yake cewa ,”(56) Kuma ban halitta aljanu da mutane ba sai domin su bauta mani. (57) Bana nufin wani arziƙi daga gare su, kuma bana nufin su yi min hidimar ciyar da ni. (58) Lallai Allah shi ne kaɗai mai azurtawa, me ikon yi, me gafara”.
saboda haka babu abinda ubangiji ke buƙata daga gareka Emanuel fa ce ka amsa kalmar Shahada, ka kuma yi mubaya’a akan ƙa’idar,”annama ilahukum wahid”. domin akan wannan ƙa’idar aka gina addinin musulunci. ka shaida babu wani Abin Bautawa Da Gaskiya Sai Allah, Kuma Annabi Muhammadu Manzonsa ne, Waɗannan kalmomin sune ƙofar shiga musulunci, kuma rukuni mafi girma, kuma ba a yin hukunci da musuluncin mutum sai yay furuci da su, da kuma yin aiki da abinda suka ƙunsa, daga sannane ka tashi daga kafiri ka koma musulmi Emanuel. Liman ya ɗau alƙur’ani yay masa nuni da shi yace Emanuel wannan shine zancen Allah, littafin da aka aiko Manzonmu Annabi Muhammadu (S.A.W) da shi. ka samu damar yin riƙo dashi domin ka tsira daga wannan narkon azabar da zaka riska a ranar alƙiyama in har ka mutu kana kafiri. acikinsa zancen Allah yake gaba ɗaya, Emanuel ba don san kanmu ko kuma mu yaudari zuciyarka ba, amma babu wani addini na gaskiya sai addinin musulunci, kuma babu wata kyakykyawar hanya saita bin ubangiji, inhar kabi Allah, kayi koyi da koyarwar Manzon Allah, Ka yarda ba zaka ƙara yin shirka ga Allah ba, ka riƙe gaskiya da amana, ka yarda ba zaka aikata zina ba, kiyaye jinka da ganinka daga haramun, ka yarda da haramcin sata, ka tsare kanka daga saɓawa ubangiji, to haƙiƙa ka rabauta daga dukkan wani narko na azabar ubangiji.
domin haƙiƙa Ubangiji ya tanadi gidaje guda biyu wuta da Aljannah, ya kuma yi alƙawarin cikasu da mutane, za’a cika Aljannah da mutanen da suka riƙi gaskiya suka tashi a tafarkin Manzon Allah, ita kuma wuta za’a cikata ne da mutanen da suka ɓata, suka yi watsi da gaskiyar da ma’aikin Allah yazo mana da ita. Dan haka Emanuel idan ka shirya zaka karɓi kalmar La’ilaha’illah, Muhammadur-Rasulillah. ni kuma zan amsa mubaya’arka, zan roƙa maka gafarar ubangiji domin haƙiƙa Allah mai gafara ne kuma me jin ƙai.
a Wannan lokacin duk wanda ya kalli Emanuel sai ya hangi irin raunin da zuciyarsa tayi, jikinsa gaba ɗaya yay sanyi saboda tasirin waɗan nan kalamai, kuma ya shiga faɗar kalmar da Liman ya umarce shi ya maimaita bayan ya faɗa, Mairo sai da nayi hawaye, daren jiya tare mukayi sallar isha’i da Al-Mustapha a masallaci, kuma yau da asuba ma ni nasa Amadu ya tasheshi, kuma ya roƙi Amadu akan ya dawo da sauri domin ya fara masa bitar karatun alƙur’ani…Mairo ban amsawa Al-Mustapha zan aura masa ke ba sai bayan ya musulunta, kuma hakan ba yana nufin zan tursasa miki ba dan shima bai ƙara tunkarata da maganar ba, sai dai a yau da safe nasa Amadu ya kira min shi na shaida masa na basa ke, idan ya shirya ya fito zan ɗaura muku aure, amma duk da haka ki faɗa min ra’ayinki dan ba zan miki dole ba, ba zan tauye miki hakki ba, alƙawarin dana ɗauka kawai nake tsoron saɓawa, dan ban san wane irin hukunci ubangiji zai min ba”.
shirun dai nayi ba shiru ne na haka kawai ba, wani irin shiru ne da nake jin guguwa na kaɗawa acikinsa, shirun da acikinsa na kasa zuƙar numfashi me daɗi, tun a sanda Baba ya shiga kora min wannan jawabin nayi mutuwar zaune, gaba ɗaya abin jinsa nake tamkar almara, yanzu ba maganar auren ce abin mamakina ba, mamakin yana ga musuluntar da Emanuel yayi, kuma tsoro sai ya kamani, naji a zuciyata ban yarda da wannan tuban nasa ba, ban kuma yarda da karɓar musuluncinsa ba, nafi yarda da yay amfani da siyasa ne don kawai Baba ya bashi ni ɗin, domin ya rama abinda nayi masa a waccan ranar, ga Baban kuma ya amince masa.
hawaye suka cika min idanuna, kewar Gwaggona da mararin kasancewarta a wannan lokacin ya kamani, wata ƙila da ta na raye duk ba za azo kan wannan gaɓar ba, ba za aiwa ƴarta abunda taƙi jini ba wato auren wuri, ba za’a aurawa ƴarta wanda bata so ba, ba kuma za’a dakushewa ƴarta karatun bokon da ta cimma burinta akansa ba, dama na sa ni! na kuma ji ajikina tun a ranar da Gwaggona ta rasu wani shafi na ƙaddarar rayuwata ya buɗe.
na ɗago da idona a hankali na dubi Baba da idanuwansa ke akaina ƙyam, ko ban shiga zuciyarsa ba nasan babu komai acikinta fa ce tsoro da fargabar amsar da zan bashi, kuma ni kaina ɗin ina jin rashin kyautuwar abinda zanyi, to amma me?, alokaci guda sai naji duka ɓarika biyu na zuciyata sun sauya ra’ayi, sun sauya ƙin amincewar da nake shirin yi zuwa yarda, domin idan har naƙi amincewa Baba maganar auren nan tamkar nayi butulci ne a gare shi, sannan kuma shima kansa Emanuel ɗin naji ina jin tausayinsa, haƙiƙa ko bana sonsa zan iya amince masa saboda alkhairin da yay mana a sanda ake zaman makokin Gwaggo.
ba wannan ba ma tukunna, ni yanzu a duniyata ina jin zan iya mallaka komai nawa ga duk wanda yay adu’a ga Gwaggona, balle shi da Baba ya faɗa min ya ɗau tsawon sati guda yana ma ta adu’a, kuma har ya bada kuɗi akai sadaƙa ladan ya isa gareta, Gwaggona da bani da kamarta duk faɗin duniya.
bayan wannan ma! Allah ya sani tun ban mallaki hankalina ba nayi alƙawarin babu abinda Babana zai nema daga gareni na kasa yi masa, ko da kuwa rayuwata yace na sadaukar, Allah ya sani na jima ina jiran wannan rana da Baba zai umarceni da auren mijin daya zaɓa min na amince masa kai tsaye, dan ta hakanne kaɗai zan iya rama masa da irin sadaukarwar da yay a gareni.
zan iya yin komai dan ganin na wanzar masa da farinciki, Baban nan nawa da nake mutuwar so, Baban nan daya sha wahala akanmu a rayuwarsa, ba don komai, sai dan ganin rayuwarmu ta inganta, Babana dai! Mahaifina! Mahaifina daya sadaukar da ƙodarsa guda ɗaya aka saka min a sanda nake shekara goma, Babana daya ƙarar da komai nasa a sanda za’ai min aikin ƙoda, Baban daya sha wahalar jinya ta sanadin bada ƙodarsa da yay a gareni, wanda har saida muka fitar da rai da shi, to akan me yanzu zan butulce masa kan wannan ƴar ƙanƙanuwar buƙatar tasa?.
to ni kuwa ko da wane nufi ne ma Al’mustapha zai aureni ni kam na amince, ni ba butulu bace, dan haka ayau ko da raina ne Baba yace na bayar wallahi zan bayar in har zaiji daɗin hakan. Baba ya katse tunani a sanda maganar tasa ta shigo cikin kaina da wani irin dagargaza zuciya, nasa hannu na share hawayena, sannan na ɗago na dube shi da murmushi nace masa,”na amince Baba, na amince zan auri Al-Mustapha in har hakan shine muradinka, kuma hakan ba zaisa ka saɓa alƙawarin daka ɗauka ba, na amince zan zauna da shi a matsayin mijina bisa turbar daka ɗorani akai, Baba na maka alƙawarin zan koyawa zuciyata sonsa idan har hakan shine zai faranta maka, ko babu komai nasan ba zan taɓa ganin ba daidai ba idan har na bi umarninka”. nai shiru saboda kukan daya danne sauran maganata.
Baba yay murmushi sannan yace, “matso nan gabana Mairo”. na rarrafa na ƙarasa gabansa, ya kamo duka hannayena ya riƙe a nasa yace,”na gode Mairo, na gode Allah yayi miki albarka ya saka miki da alkhairi…kuma ina mai tabbatar miki ba zaki taɓa wulaƙanta a hannun wannan yaron ba, ni ba magini bane saboda haka ban duba filin wurin ba, amma ina da yaƙinin Al-Mustapha ba zai cutar dake ba. a gobe insha’Allahu zan ɗaura miki aure da Al-Mustapha, fatana ɗaya a gidan aurenki kici gaba da ginuwa akan wannan kyakykyawan halin dana sanki da shi, ki zama tamkar mahaifiyarki, mace me gaskiya da amana, Mace me haƙuri, juriya, kawaici da ƙyamar abin hannun wani…Allah yayi miki albarka ya kuma jiƙan mahaifiyarki”.
na amsa masa da, “amin Babana”. daga haka zaman namu ya watse, Baba yace ba zan tafi gidan Yagana ba anan zan kwana tunda dare yayi, ba haka naso ba, dan ko kaɗan yanzu bana son kwanan ɗakin Gwaggo babu ita. kuma sanda nake fitowa daga ɗakin Baba, sai naga Inna Zulai da Adawiyya sun bar wurin da sauri sunyi ɗaki, sunji komai, dan alama ta nuna ba tun yanzu suke laɓe a wurin ba, nai wani guntun murmushi kawai ina girgiza kaina.
kuma ko sanda na isa ɗaki na tarar har Kulu ta kwanta, na tura ƙofa na rufe sannan na wuce na hau kan gadon ƙarfen Gwaggona, na kwanta daga bayan Kulu, wacce idona ke haska min tamkar Gwaggona.
na cure a wuri guda, tunda na kwanta babu abinda nake banda hawaye, tun sautin kukan da nake bai fita har ya fara fitowa a hankali. maganar Kulu daga kaina naji ta ce,”kukan me kike?”. nai ma ta shiru har sanda ta ƙara yin magana. “tambayarki nake kukan me kike?”. sai kawai na tashi zaune na rungumeta ina ci gaba da shashsheƙar kuka, tasa hannayenta ta kewayeni tana faɗin,”kukanki yana ɗaga min hankali, yana sosa zuciyata, yana hanani natsuwa, idan ba so kike zuciyata ta buga ba to ki faɗa min me akai miki kike kuka?”. Muryata ta fito cikin sheƙar kuka ina fizgar numfashi nace,”aure Baba zai min”. Maganar tata ta doka tsalle a zuciyar Kulu, mamaki ya bayyana ƙarara a fuskarta, tsoro kuma da fargaba suka cika zuciyarta, wa Malam zai aurawa ƴarta ba ta sa ni ba, bai kuma sanar da ita ba?, ko dai ƙarya ta ke faɗa ma ta? ko kuma taji maganar tasa ba dai-dai ba?.
gudun karda Mairon ta gane halin da ta shige tai saurin ture komai daga ranta, ta lallasheta da bata haƙuri har ta samu zuciyarta ta sauko ta bar yin kukan. kuma daga hakan sai bacci ya ɗauketa saboda karatun qur’anin da Kulu ke karanto ma ta acikin kunne tamkar wata ƙaramar yarinya.
sai da ta tabbata baccin Mairon yayi nisa, sannan ta sauka daga gadon ta fita don zuwa ɗakin Malam, sai dai tana fitowar ne kuma tai kiciɓis da wucewar wannan mutumin dake lulluɓe jikinsa da daddare, wanda ko a daren jiya taga gimlawar inuwarsa ta ƙasan ƙofar ɗaki, da alama kuma ɗakin zai shigo sai bai sami damar hakan ba, saboda ƙofin da tayi na hana idonsa ganin komai.
ta sani shine silar ciwon ƙafar Gwaggo, dan rana ta ƙarshe daya shigo ɗakin ya fita da ta zo ta tarar da syringe a ƙasa wanda aka jefar saboda tsoron tahowar me shigowa ɗakin, ta ɗaga syringe ɗin ta duba na allurar botulinum toxin ne, gubar da zata iya kashe duk al’ummar ƙasar da akaiwa feshinta, kuma ko da ta saka ihu kowa ya fito a lokacin babu wanda aka gani.
daga baya zuciyarta ta saƙa ma ta koma wanene acikin gidan nan yake, wanda ya ƙware a ɓadda kama, ashe zuciyarta ba zargi ta ke ba, hakanne, don gashi kuwa yau idanunta sun gane ma ta ko wane, dan taga fuskar a sanda ta fito lokacin da ake ƙoƙarin lulluɓe kai.
zuciyarta ta tsorata da abinda zai iya faruwa, saboda haka ta haƙura da maganar da zata yi da Malam a daren yau, ta jira gobe idan Allah ya kaimu, tana gudun karta fita yazo ya cutar ma ta da ƴa, cutarwa da ba zata bari, dan ko ta Gwaggonma ba tayi shiru ta ƙyale bane, kwanaki goma ne kacal da rasuwar, tana jiran mutuwar ta sake barin jikin kowa kamin ta tona asirinsa, kuma lokacin da SIRRIN daya jima a ƁOYE zai fito fili.
dan haka sai ta mayar da ƙofar ta rufe ta dawo ciki, ta kwanta ta rungomo ƴarta jikinta tsam, amma duk da haka tsoro bai bar ranta ba. kuma acikin baccin nata ne taji wata magana da bata san amon sautin waye ba tana faɗin,”ni ban taɓa tsara abu ya tafi ba ayanda nake so ba, shirina na gaba akan Kabiru da ɗan’uwansa ne, ina so a gobe ku sace Kabiru, kuma ku buƙaci adadin kuɗaɗen da zan lissafa muku, sannan kubi bayan ɗan’uwansa ku haddasa hatsarin da kowa ma zai rasa ransa, babu ruwana da sauran rayukan in har shi ɗin ya mutu…bana aikin asiri, da ƙwaƙwalwata nake amfani, a tafin hannuna nake zana duk wata manufa tawa, na kuma juya yanda nake son duk wani tsarina ya kasance, saboda haka a gobe wannan aikin ya gudana”.
a firgice Kulu ta farka, kuma dai-dai lokacin da itama Mairo ta farka a firgicen, dukansu salati suke tashin hankali bayyane a fuskokinsu. sai da Kulu ta sauke wata doguwar ajiyar zuciya sannan hankalinta ya sauka akan Mairo, wacce ta takure, jikinta sai rawa yake, ga wata uwar zufa da ta haɗa.
“menene Mairo?”. ta tambayeta tana me yi ma ta rumfa, kuma bata fasa bin kowacce kusurwa ta ɗakin da kallo ba tana biyo adu’oi a bakinta.
“mafarki nayi”. “mafarki kuma? me kika gani acikin mafarki?”. na ɗago na dubi Kulun a tsorace sannan nace,”wai acikin wani jeji me duhu an ɗauremu ni da Basma, ga kuma wata ƙatuwar rijiya me zurfin gaske a kusa damu, wata Mata da ban san kowace ba tazo tana jawomu zata jefamu ciki sai ƙyalƙyala dariya ta ke, tana faɗin wai a tsarin rayuwarta bata lissafa da wani abu da zai shige ma ta gaba ba, kuma tana dab da hankaɗamu cikin rijiyar sai kawai Gwaggona ta bayyana acikin wani irin haske me kyau, tana kuka tana roƙonta akan karta aikata mana hakan ta duba maraicinmu, Gwaggona na cewa kada na bari ta jefamu na sami ƙarfin da zan ƙwaci kanmu, kuma nai gaggawar zuwa na ƙwaci Ya Kabiru daga mummuna hatsarin dake tunkararsu kuma duk ata sanadin wannan matar, karna bari, karna bari komai ya samemu. daga faɗin haka kuma sai Gwaggon ta ɓace, muka nemeta muka rasa, shine Basma ta gartsawa Matar cizo a hannu ba shiri ta sakemu, maimakon mu faɗa rijiyar sai ita ta faɗa ciki…kuma kema sai gaki kinzo mana kina murmushi da dukkan nuna wata ƙauna ta uwa a garemu, sai dai kina kama hannuna ina fizgewa ina tureki akan sai kin barni kin bar rayuwata, shine sai wani farin mutum ma yazo, rabin jikinsa haske rabinsa duhu, yana cewa na taho gare shi, amma sai kika ce min a’a karda naje, shi ɗin ba abin so bane, shi ɗin mutum ne me hatsari, shi kuma wani saurayi dake zaune kan wata kujera ya harɗe ƙafafunsa yana kallonmu da wani murmushi me cike da tarin ma’anoni da yawa, yana ta wani abu kamar basarake, bini bini sai yaja shati da yatsu biyu a goshinsa, yana murza karan hancinsa kamar me shirin ɗaukar wata fansa, kuma suna kama da ɗaya mutumin da kika ce karna je gunsa, duka saina ji kun bani tsoro, hatta dake ɗin da kika buɗen hannaye na isa zuwa gareki, amma alokacin zuciyata wani zafi ta ke ji akanki…dan haka saina kama hannun Basma muka shiga dajin da gudu don kuɓuta daga cikinsa, dan ganinku nake kamar zaku cutar dani ne koma kun cutar dani ɗin…sai dai ashe ba hanyar ɓullewa muke ɗauka ba cikinsa muka ƙara shigewa, kuma daga bakin wata ƙatuwar bishiya sai naga Ya Kabiru a hannun wasu tsamurarrun mutane kayan jikinsu duka baƙaƙe, sunyi masa jinajina yana miƙo min hannu akan nazo, wai naje na gare shi ba dan na cece shi ba sai dan ya mutu a ƙirjin matarsa, shine kawai na tafi da gudu kamin na ƙarasa suka fille masa kai”. na ƙarasa maganar cikin matsanancin kuka, jikina banda kyarma babu abinda yake, sai kalmar na shiga uku da nake ambata.
na sake ƙanƙame hannun Kulu tare da zare jikina daga nata, na ɗago kai na zubawa fuskarta kallo, idan ba wai kallon rashin fahimta nake ma ta ba, fuskarta na nuna firgici sosai, firgicin da ta ke son ɓoyewa, kuma ta yanda wani abu ya wuce ta maƙogoronta na tabbatar da itama ta shiga ruɗanin dana shiga, fararan idanuwan nan nata sun ƙara yin haske kamar fitila, yanayin yanda ta ke kallona na yin nuni da irin tasirin nazarinta akaina ko kuma labarin mafarkin dana bata.
sai ta kwanto da kaina saman ƙirjinta, ta ƙarasa zame ɗan kwalin kaina, ta ɗora hannunta saman gashina tana shafawa, muryarta a hankali ta fara magana, cikin muryar nan tata da sau tari na kanji ina samun wata iriyar nutsuwa da jinta.
“dukkan wani mafarki ba gaskiya bane sharrin shaiɗan ne, dan haka ki kwantar da hankalinki babu abinda zai faru acikinsa sai alkhairi insha’Allahu”. “amma fa Kulu harda Gwaggona na gani aciki, sannan kuma ki ce min wannan mafarkin ba zai zama gaskiya ba, ki tashi dan Allah muje mu sami Baba a ɗaki, wata ƙila shi ya iya gane me hakan ke nufi”. ina jin sanda ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya da hucin zafin numfashinta ya sauka ajikina.
tabbas mafarki ƙarya ne, to amma ta yarda da maganar Bella da ta taɓa ce musu, “duk da mafarki ba gaskiya bane, amma wani lokacin yana juyewa tamkar madubi ya iya nuna abinda zai kasance a zahirin”. tabbas kuma ta shaida hakan, domin ta gani akan mafarkinsu daya zama iri guda da Aaliya, kuma gashi ayauma mafarkin Mairon na nema ya haska ma ta madubin zahirinta.
“ki bini a karatun da zanyi”. abunda ta faɗa kenan, sai kuma bakinta ya kama da ayatul kuriyyu, na shiga bin karatun bakina na rawa kalmomin na harɗe min, dan har yanzu tsoro bai bar jikina ba. kuma sanda muka kai ƙarshen suratul falaƙ, sai naji tsoron ya bar jikina, nutsuwata ta fara dawowa, firgicin da nake ciki yabi ta iska, na sauke ajiyar zuciya, sannan Kulu ta umarceni dana sauko muje muyi alwala muyi sallah, insha’Allahu koma wane irin sharri ne ubangiji ya juya shi ya zama alkhairi, bamu miƙe akan sallayarmu ba har saida muka idar da sallar asuba, sai dai har alokacin mafarkin bai bar dawo min ba, kuma cike nake da son sanin ma’anar dake cikinsa, dan haka kawai ba zanyi wannan mummunan mafarkin ba, dole akwai wata ayar acikinsa da ta ke zuwa gareni.
Kulu kuwa safiyar sai ta sakance ma ta mara daɗi, domin tun a mafarkin Mairo na jiya zuciyarta ta shiga cikin taraddadi, tabbas a yanzu, kuma a yau tasan anzo kan gaɓar, ayau ba sai gobe ba Gaskiyar da suke ta binnewa a matsayin sirri zata bayyana, a yau ba sai gobe ba Mairo zata san gaskiyar komai, domin shi lokaci baya wasa da kansa, yana bada mitsitsiyar dama ne ga me shirin yin wani tsarin aikinsa acikinsa.
bayyanar gaskiyar ba itace tashin hankalinta ba, Aaliyah!Aaliyah!!! itace zata zame ma ta matsala, itace zata zame ma ta tsaiko, itace zata wargatsa ma ta duk shirin da ta tsara. ta sani! ta san wace Aaliyah! tasan daga lokacin da suka haɗu zata saka ƙafa tayi fatali da wannan rufaffiyar kwalabar da suka rufe a tsakaninsu, idan ma har fashewar da kwalabar tayi baiyi ma ta zata iya sa ƙafa ta ƙarasa mitstsiketa ta yanda wannan alƙawarin nasu zai karye a lokacin, alƙawarin nan da suka ɗaukarwa juna kamin rabewarsu.