SIRRIN ƁOYE COMPLETE

Farashin MTN Data 5GB akan 400 masu tsarin Betatalk, ga masu buƙata sai ku tuntuɓi wannan lambar 09060523731.
Assalamu alaikum jama’a na tallatamuku hajar mu ta online/offline business dina wanda zanrin ga sayar muku da data ta mtn a sassaukan farashi Kamar haka
I selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
10GB@===2,600
15GB@===3850
20GB@===5000
40GB@===9900
Dial 460260# to check Data balance.
Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
Whatsapp OR Call 08066268951
Plss Comment&Share.
SIRRIN ƁOYE
By Oum Ramadhan✍????
Tabbas Abu-Ɗalib Mahaifin Annabi Yana Daga Cikin Mutanen da Suka yi Tasiri Wurin Yaɗuwar Addinin Musulunci Har Ya kai Zuwa Yanzu. Ya Zamo wa Manzon Allah Garkuwa ta Yanda Duk Dukan da Za’a Kawowa Annabi Shi Yake Kare Masa, Kasantuwar Yana Daga Cikin Dattawan ƙuraishawa Yasa Suke Shakkarsa Har Suke Ragawa Annabi.
Bayan Rasuwarsa Manzon Allah Ya tsinci Kansa Cikin tsananin Wahala Saboda Mai Bashi Kariya Daga Cutarwar ƙuraishawa Yau Ubangiji Ya Amshi Rayuwarsa, Da Cutarwar Tayi tsanani ga Sahabban Annabi Raunana, Sai Ya Umurce su da yin Hijira Zuwa Habasha Don Su Samu Sauƙin Wahalar da Suke Sha a Hannun ƙuraishawa. Wanda Daga ƙarshe Allah Ya Umurcesa da Yin Hijira Zuwa Madinah.
Sai dai Duk da Kariyar da Ya Bawa Annabi, Ubangiji Bai ƙaddara Masa Karɓar Addinin Musulunci ba. Wato a Kafirinsa Ya Rasu. Mutuwarsa A Matsayin Kafiri Yana Daga Cikin Abinda Ya Baƙantawa Annabi Rai, Ganin Yanda Ya Tallafawa Da’awarsa. Hakan Yasa Annabi Ya Ɗauki Alƙawarin Nema Masa Gafara, Har Sai da Ubangiji Ya Haramtawa Annabi Yi Masa Addu’a Kamar Yanda Wannan Ayar Ta Tabbatar:
(مَا كَانَ لِلنَّبِيِّ وَالَّذِينَ آمَنُوا أَنْ يَسْتَغْفِرُوا لِلْمُشْرِكِينَ وَلَوْ كَانُوا أُولِي قُرْبَى مِنْ بَعْدِ مَا تَبَيَّنَ لَهُمْ أَنَّهُمْ أَصْحَابُ الْجَحِيمِ)
Kuma Hadisi Ya Tabbata Cewa:
عَنْ سَعِيدُ بْنُ الْمُسَيَّبِ عَنْ أَبِيهِ، قَالَ: لَمَّا حَضَرَتْ أَبَا طَالِبٍ الوفاة جاءه رَسُولِ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ فَوَجَدَ عِنْدَهُ أَبَا جَهْلٍ وَعَبْدِ اللَّهِ بْنِ أَبِي أُمَيَّةَ بْنِ الْمُغِيرَةِ فَقَالَ: «أَيْ عَمِّ قُلْ لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ كَلِمَةً أُحَاجُّ لَكَ بِهَا عِنْدَ اللَّهِ»، فَقَالَ أَبُو جَهْلٍ وَعَبْدُ اللَّهِ بْنَ أَبِي أُمَيَّةَ بْنِ المغيرة: أَتَرْغَبُ عَنْ مِلَّةِ عَبْدِ الْمُطَّلِبِ، فَلَمْ يَزَلْ رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ يَعْرِضُهَا عَلَيْهِ ويعودان بِتِلْكَ الْمَقَالَةِ حَتَّى قَالَ أَبُو طَالِبٍ آخِرَ مَا كَلَّمَهُمْ: عَلَى مِلَّةِ عَبْدِ الْمُطَّلِبِ، وَأَبَى أَنْ يَقُولُ لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ، فَقَالَ رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ: «وَاللَّهِ لَأَسْتَغْفِرَنَّ لَكَ مَا لَمْ أُنْهَ عَنْكَ»، فَأَنْزَلَ اللَّهُ تَعَالَى: ﴿ مَا كانَ لِلنَّبِيِّ وَالَّذِينَ آمَنُوا أَنْ يَسْتَغْفِرُوا لِلْمُشْرِكِينَ وَلَوْ كانُوا أُولِي قُرْبى مِنْ بَعْدِ مَا تَبَيَّنَ لَهُمْ أَنَّهُمْ أَصْحابُ الْجَحِيمِ ﴾،
[القصص: ٥٦]
An Karɓo Daga Sa’eed bn Musayyib (ra) Daga Mahaifinsa Yace: Yayin da Ajali Yazowa Abu-Ɗalib, Sai Annabi (saw) Yazo Ya Samu Abu-Jahl da Abdullahi bn Umayyah bn Mughirah. Sai Manzon Allah (saw) Yace: “Ya kai Kawuna, Kace La’ilaha Illallahu, Kalmace da Zan Kafa Maka Hujja da Ita a Wurin Allah”. Sai Abu-Jahl da Abdullahi bn Abi-Umayya Suka ce: “shin Yanzu Zaka Ƙyamaci Addinin Abdul-Muɗallib? Manzon Allah (saw) Bai Gushe ba Yana Maimaita Masa Kalmar Shahada, Su Kuma Suna Ƙara Ce Masa: “Yanzu Zaka Bar Addinin Abdul-Muɗallib”. Har Sai da a Ƙarshe Abu-Ɗalib Yace Shi Yana nan Akan Addinin Babansa Abdul-Muɗallib Yaƙi Faɗin La’ilaha Illallahu. Sai Manzon Allah (saw) Yace: “Zan Dinga Nema Maka Gafara Matuƙar Ba’a Hanani ba”. Sai Allah Ya Saukar da:
(مَا كَانَ لِلنَّبِيِّ وَالَّذِينَ آمَنُوا أَنْ يَسْتَغْفِرُوا لِلْمُشْرِكِينَ وَلَوْ كَانُوا أُولِي قُرْبَى مِنْ بَعْدِ مَا تَبَيَّنَ لَهُمْ أَنَّهُمْ أَصْحَابُ الْجَحِيمِ)
“Bai Dace Ga Annabi da Waɗanda Suka yi Imani ba Su Dinga Nemawa Mushirikai Gafara Ko da Kuwa Sun Kasance Ma’abota Kusancinsu Ne Bayan Sun Bayyana A Garesu Cewa Su Ma’abota Wuta ne”.
(Qasas: 56)
*Sannan Damuwar da *Annabi (saw)* Ya Shiga Saboda Rashin Musuluntar Baffansa, Sai Ubangiji Ya Sake Jawo Hankalinsa da Cewa:*
﴿إِنَّكَ لَا تَهْدِي مَنْ أَحْبَبْتَ وَلكِنَّ اللَّهَ يَهْدِي مَنْ يَشاءُ﴾
“lallai Kai Baka Iya Shiryar da Wanda Kake so, Allah Ne Ke Iya Shiryar da Wanda Yaso”.
Har Wayau Hadisi Ya Tabbata Ga me da Kasantuwar Abi-Ɗalib Ɗan Wuta, Manzon Allah Yana Cewa:
عَنْ أَبِي سَعِيدٍ الْخُدْرِيِّ رضي الله عنه: أَنَّهُ سَمِعَ النَّبِيَّ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ وَذُكِرَ عِنْدَهُ عَمُّهُ أبو طالب، فَقَالَ: «لَعَلَّهُ تَنْفَعُهُ شَفَاعَتِي يَوْمَ الْقِيَامَةِ، فَيُجْعَلُ فِي ضَحْضَاحٍ مِنَ النَّارِ يَبْلُغُ كَعْبَيْهِ يَغْلِي مِنْهُ دِمَاغُهُ»
An Karɓo Daga Abi-Sa’eedil Khudry (ra), Lallai Yaji Manzon Allah (saw) Yana Ambaton Kawunsa Abi-Ɗalib Yana Cewa: “Wataƙila Cetona Ranar Ƙiyama Ya Amfane shi. Za’a Sanya Masa Takalmi Na Wuta Wanda Ƙwanyar Kansa Zata Dinga Tafarfasa”.
Waɗanda Suka Fara Kawo Maganar Wai Abu-Ɗalib Ya Musulunta Sune Ƴan Shi’a Kawai Don Su Kambama Sha’anin Aliyu bn Abi-Ɗalib (ra). Daga Baya Kuma Wasu Sufaye Suka Ara Suka Yafa.Wallahu A'alam.
36)
ganin yacca Yagana ta faɗo ɗakin, Malam dake zaune kan kujera ya miƙe da sauri yana tambayarta lafiya, kuma tambayarsa tai lokaci ɗaya da shigowar Amadu wanda ya karɓo magunguna a pharmacy.
shima ganin yanda Yagana duk ta ke a hargitsa ya jefa ma ta tasa tambayar. ta haɗiye wani yawu daya wuce da ƙyar tace,”ni Rakiya yau gane-gane na yaja min”. ta faɗa tana ɗan haki kamin ta nuna gadon da Akila ke kwance tace,”Yama sunan wannan balarabiyar?”. kan su bata amsa ta ɗora da,”kai ku barni da wannan sunan mai kwalmaɗa, mu tafi a Kulun dai…ku ashe duk zaman jinyar nan da muke da gawa muke tare bamu sa ni ba”. a tare duka suka waro ido waje suna tambayarta,”gawa kuma Yagana?”. ta gyaɗa kai,”ƙwarai kuwa gawa…yanzu ina alwala naga ruhinta na tunkaroni da wani irin haske, ba shiri nayo ciki da gudu, har fa da Mairo na gani itama hannunta kamar da makaman yaƙi, tahowa suke dadab fuskokinsu duka a fusace..ni Rakiya ko me mukai musu Allah masani”.
Amadu yay guntun tsoki da shi kaɗai yaji kayansa sannan ya wuceta zuwa ciki, tabi bayansa da ido tana faɗin,”au ina faɗa maka ruhinta yazo a fusace kana ƙara zuwa inda ta ke…kai wannan ɗa kai da Mairo ban san waya fi wani rashin jin maganar na gaba ba…Amadu gawa ce fa kake tsaye a gabanta, ni dai ina faɗa maka kazo ka karɓo mana takarda wucewa gida”. yay ma ta shiru yana buɗe ledar magungun nan ya fito da su. Malam yace da ita,”Yagana ƙila kin saka wani abu a ranki ne shi yasa, amma Akila da ranta dan yanzun nan fa bacci ya ɗauketa ko minti uku ba’ai ba…”. ta katse shi da faɗin,”Adamu kana ina?”. ta faɗa a sanda ta ke zura fuskar hijabinta. Malam yace,”gani Yagana”. “to ban hanya na wuce, dan ni kaɗai nasan abinda na gani”. kuma rufe bakinta kenan a sanda ta ke ƙarasowa bakin ƙofa saiga su Mairo sun ƙaraso wurin, kuma kan ƙiftawar ido Yagana ta ture Malam ta koma ciki tana shimfiɗa hailala tana neman mafaka. Ba Malam kaɗai ba, harta Amadu sai da allon ƙirjinsa ya girgiza da ganin Aaliya, abin mamaki da al’ajabin da zasu iya kira basu taɓa gani ba shine mutane masu kama da juna sak irin haka.
da ace Akila bata basu labarinta ba, da su kansu a yanzu da sukaga ƴar biyunta zasu iya tsorata su kirata da fatalwa. to amma sanin cewar sun san komai dan haka sai basu ji wani ɗar ba, kuma basu yi mamakin ganin nata ba kasancewarta tare da Mairo, dama tun a daren jiyan Adawiyya ta kira waya ta ke shaida musu wai Mairo tace ta shiga yawon duniya, Kabiru ya koma gidan ko Allah zaisa ya gamu da ita a hanya sai dai haka ya ƙaraci bincikensa har a tasha bai sameta ba, kuma da suka koma gida yaje gidan Yagana ɗauko wallet ɗinsa ya tarar babu ita kuma babu kayan Mairo ya tabbatar da cewar zaiyi wuya idan ba Qatar ta nufa ba, kuma a safiyar yau ɗin ya wuce airpot dan tabbatar da zuwan nata.
Malam ne ya amsa sallamar Aaliya tare da yi musu maraba da zuwa, sai dai sam ita ba fuskantar me yake cewa takeyi ba tun bayan sallamar daya amsa musu. kuma kanta kawai ta ɗaga musu kan ta sauke idanuwanta akan Akila dake kwance tana bacci, yayin da gefe guda na zuciyarta ke ma ta wani susa da ita ɗaya ta san irin abinda susar ke haifar ma ta.
“Mairo kin kyauta”. abinda Malam yace kenan da ni yana duban fuskata, saina ɗago da kaina daga barin kallon yatsun hannuna da nake na dube shi na sakan ɗaya sannan ta faɗa jikinsa. “dan Allah Baba kayi haƙuri ka yafe min, nayi kuskure kuma na tuba, ina neman afuwarku”. sai kawai ya ɗora hannunsa akaina ya shafa tare da faɗin,”babu komai Maryam, ƙuruciya ce taja kika aikata hakan, amma sai dai ina so na tunasar dake wani abu, ubanjiji baya ramuwar gayya kuma baya son masu yinta, dan haka ko dan gaba ki dinƙa tunawa da wannan…Allah ya sanyaya miki zuciyarki ya kuma baki haƙuri da juriya…kuma Allah yay miki albarka da ayanzu kika zama silar dawowar mahaifiyarki duniyarta ta asali”.
kuma maganar da Yagana keyi ta karkata hankalinsu gareta.
“yo aini gaba ɗaya na mance da wannan balarabiyar ta shaida mana ita biyu ce, kai jama’a Allah da iko yake, yo ku me iya ganinku ai sai me dakakkiyar zuciya…ka duba dan Allah wata sarauta ta ubangiji…Mairo to ita wannan ɗin aina kika tsintota?, kar dai kice min ɗaukar fansar ta ki ne ya kai ki can Ƙasarun”. “kai Yagana mene wani kuma ƙasaru, Qatar ake cewa”. Amadu ya faɗa a sanda yake miƙawa Alhassan kujerar zama.
a cikin larabci Baba da Amadu suka gaisa da Aaliya kasancewar suna jin kaɗan-kaɗan, Yagana ce dai ta ke ta zabga mita akan tana ta kula Aaliyan tayi mata banza tana yi mata kallon hadarin kaji daga ita har shi zololon ɗan nata.
sai da Mairo tace ma ta,”Yagana dukansu fa basa jin hausa, Larabci da turanci suke ji idan kuma kin iya to bismillah”. ta riƙe haɓa da faɗin,”ashe abin babba ni Rakiya ƴar gidan larabci da turamci, da dai alu ambaki ne saina biya…kuma kema tun farko ai sai ki min bayani ba sai ta kai ga na fara jin haushinsu ba, ko da yake kema Mairo yanzu ai kinfi ƙarfina ni Rakiya Mannir”. murmushi kawai nayi, na shiga yiwa Aaliya bayanin cewar Yagana na gaisheta, kai kawai ta ɗaga kuma kamin na ƙara cewa wani abu ta tari numfashina wajen faɗin,”ki tambayesu mene silar ciwon nata?”. maganar tata ta fito very cool, kuma har sannan idonta na kan fuskar Akila da tai looking very innocent, duk ta rame tayi duhu, idonta kuma bai bar saukar da ƙwallar tausayi ba a hankali.
“to mu dai tana cikin bamu labarin rayuwarta ne sai kuma ta shiga wannan halin”. Malam kewa Mairo bayanin, kuma itama saita juyar da shi ga Aaliyan.
“me tace musu a labarin nata?”. Mairo ta kuma faɗawa Malam ɗin, kuma kan yace wani abu Yagana tai caraf tace,”ke labarin wannan ja’irar uwar ta ki da kayan haushi yake, ki faɗa mata ta haƙura daji dan Allah tunda dai tasan komai, ni labarin ɓatan rai yake…ƴar ƙaniya kana kallonta fuska a bar tausayi ashe nan iya shege ne fal acikinta, banda ma dai yarinya da babu hankali da tausayi ina ke ina haifar ƴaƴa kice a watsar da su, kai kaji wani ɗibarwa kai zunubi…yo ba ma dole aman jini ya maƙure miki maƙogoro ba, ja’irar yarinya kawai me kafiyar jaraba. shegen taurin kanki ai duk shi yajawo miki halin da kike ciki, kuma gwanda da rayuwar ta garaki, kinga kya gane taurin kai abin cutarwa ne”.
tai shiru ta ɗago ta dubeni kan ta ɗora da cewa,”kema da kika biyo halinta idan kinga dama sai ki sauka tun wuri daga kai…dan ba komai yaja miki zuwa duniya a shegiya ba sai taurin kai…duk da naga jikinki yayi laushi kamar lawashi ban sa ni ba ko ita ƙanwar Uwar taki ta labarta miki komai shi yasa kika rissina…amma ni ai ce nake idan kin tashi dawowa da makamai za ki zo”.
maganar ta ke da Mairo, amma ita tuni ta bar ganin Yagana da abinda ta ke cewa, tun a sanda ta furta “ki haifi ƴaƴa kice a watsar”, ba ƙaramin harbawa zuciyarta tai ba, kuma maganar Alhassan ta dawo ma ta cikin kanta, kenan suma da tuni yanzu suna a matsayin marayu? idanma sun rayu kenan, tunda Jaririn da za’a yasar ai ba lallai ya rayu ba, ita kenan Ummi da bayan laifin zinarma da ta aikata da saita kuma azawa kanta wani laifin?, kamar ta faɗi wani abu sai kuma zuciyarta ta kwaɓeta dan abinda zata faɗa akan mahaifiyartata ba me kyau ba ne.
tasa hannu ta goge hawayen dake sauka acikin dasashshiyar muryarta tace,”wai lokacin da ta ke faɗa musu zata zubar damu a time ɗin da ta haifemu shine sai kawai ta fara aman jini”. “ba ita ta haifeku ba, ni na haifeku”. kuma kamin maganar ta kaɗa Mairo da Alhassan, ta girgiza Amadu dake tsaye gefe wanda yay saurin waro ido waje yana faɗin,”what?”.
“Mami kika ce mene?, ke fa kika haifemu? wannan wanne irin batu ne na ɗaure kanmu?”. ta kalli Alhassan ɗin, sannan ta kalli Mairo kana kuma ta kalli Amadu da har lokacin yake mata kallon rashin gasgata maganarta. sai tai murmushin daya tsaya iyakar leɓenta kamin tace,”Alhassan kamar yanda ka taso kaji kowa na kirana da Akila ciki kuwa harda iyayena, to bani bace asalin Akila ba, ni Aaliya nake ita kuma wannan ta kwance itace Akila, haka kuma ni na haifeku wanda bayan ita da Major da kuma ni ɗin dana haifa Allah kaɗai ne zai shaidi hakan domin shine shahidi.
lokacin dana haifeku da ace da wani makami a kusa da zan iya kasheku tabbas a wannan lokacin zanyi amfani da shi wajen ganin na aikata abinda zuciyata ke ingizani akai, na sha baƙar wuya sosai kafin zuwanku duniya, tun daga sanda na sami cikinku har zuwa sanda aka min aiki aka ciro minku, tun baku zo duniya ba nake ƙinku, zuwanku duniyar kuma yasa ƙiyayyar taku ta ninku a raina ba don komai sai dan saboda ban sameku ta hanyar da ta dace ba.
a wancan lokacin dana haifeku ni da mahaifinku duk bama ƙaunarku, ko da yake zan iya cewa gwara shi akaina, dan ni gaba ɗaya ne bana sonku, shi kuma saboda wani dalili nasa na zubewar mutuncinsa yasa yake jin ba zai iya karɓarku ba balle har ya rayu tare da ku. dalilin daya sa ya yanke shawarar cewar mu kaiku gidan Marayu idan yaso ko daga baya ne saimu ɗauko ku, ni kuma nace sam sai dai a zubaku a leda aje a ajiye wanda Allah ya tsaga da rabonsa ya ɗauka, ko kuma ayi floshing naku, muka ɗaukeku da yaƙinin zamu watsar daku a bola amma sam wannan baiwar Allahn ta hana, tace matsawar muka aikata hakan wallahi sai tayi shari’a damu, shekararmu goma sha biyar a duniya kuma tun muna yara bamu taɓa samun saɓani da ita ba sai a wannan ranar, wannan rana da kuka zo duniya, wannan rana da ake neman yanda za ai daku.
faɗa muke sosai da ita har Major ya kasa rabamu, nayi mamakin da duk haƙurin Akila sai dana tuƙeta a wannan ranar, dukanmu muna da baiwar ƙofi amma ita duk zaluncin da mutum zai mata bazata taɓa yi masa ba, amma a wannan ranar sai da ta min, sai dai sam ba zata iya cutar da ni ba hakan yasa ta maida abinta.
kuma na tsira daga baƙar kunamar da ta turo min ta harbeni sai nima na jefa mata nawa ƙofin macijin, macijin da zai iya illata kuzarinta dama lafiyarta, to amma kuma sai nai katari da abinda ya kaini ƙololuwar mamaki akan jaririyar dana haifa a wannan lokacin, abin da kuma har ya tsorata ni.
Allah me hikima, me ikon da babu irinsa, cikin ƙudurarsa Maryam ke kika ceci Akila daga wannan macijin dana san ko magani ba zaiyi aiki akansa ba, da idanuwanki a waje tarar kika kafe wannan maciji da ido da wani irin sauyin halitta ta ƙwayar idonki tayi har macijin ya kasa tunkararta balle harya cutar da ita, ƙarshema sai ni naji ajikina a sanda macijin ya ɓace.
babu irin roƙon da Akila bata min ba akan nai haƙuri mu tafi daku gida amma sam naƙi, nace ba zan taɓa bari ku lalata min duniyata ba, domin ina da tarin buruka a rayuwata a gaba, burukan da suke na siyasa da kuma riƙe manyan muƙaman dana nake fatan Allah ya ida min nufina akansu, kuma matsawar ina tare daku ƙasarmu ta shaida ta yacca na sameku ba lallai wannan burin nawa ya cika ba.
haka kuma ba zan taɓa bari ku lalata alaƙar dake tsakanina da iyayena ba, gwara ace babu ku sa iya mancewa da suna da shegun jikoki a gefe, balle suci gaba da min kallon ɓacin ran dana haifar musu.
amma sai Akila tace,”idan har haka ne to kiyi min alfarma ki taimaka ki bar min su, ina nufin ki mallaka min su mallakawa ta har abada, da yanda ko da yaran nan sun taso ba zasu san cewar ke kika haifesu ba, ke kika ɗauki cikinsu, kuma ke kika haifesu, amma ji nake tamkar ni nai naƙudarsu, wallahi Akila ina sonsu, soyayyar da ubangiji kaɗai yasan yawan adadinta, ni ina sonsu kuma zan zauna dasu a koma ya suke, tunda kece kika haifesu”.
nace da ita,”taya hakan zata kasance bayan kowa yasan da ni ce nai ciki bake ba?”. tana rungume dake a ƙirjinta kina kukan shan nono tace,”zan maye gurbinki Aaliya, zan zama ni ce Aaliya ba Akila ba daga wannan ranar, ki min alƙawarin ba za ki taɓa fallasa wannan sirrin ga kowa ba ko da ace Allah ya qadarta zan dawo cikin alhalina”. “ban gane me kike nufi da idan Allah ya qadarta komawarki ba”. “Aaliya ba zan iya komawa ƙasar da akai watsi da ke ba a lokacin da qaddara ta afka miki, lokacin daya kamata ace an jaki ajiki, ba zan iya komawa inda aka ƙyamaceki ba Aaliya, Abi da Ammi har yanzu suna fushi dake ban kuma san ranar dainawarsu ba, dan haka ba zan taɓa komawa gabansu ba sai a ranar dana san sun yafe miki sun bar fushi dake, haka kuma zan nesanta duk wani abu da zai haifar miki da damuwa ko kuma ɓacin rai, bi ma’ana zan nesantaki da yaran nan kamar yanda kike so, domin abinda kike so shi nake so Aaliya, Aaliya in har rabuwarki da yaran nan zai saka ki farin ciki to ni na miki alƙawarin nisantaki dasu har zuwa lokacin da za ki nemesu da kanki, domin ke uwa ce, kuma ko ba daɗe ko ba jima sai kin buƙace su wataran”.
banji wani ɗar acikin zuciyata ba, hasalima farin ciki nai da hukunci da Akila ta yanke, wanda yake mafita ce a gareni, tunanina ɗaya shine ta yanzu iyayenmu zasu gasgata cewar ni ce Akila kamar yanda ta shirya hakan.
“amma ai kin san akwai shaidar dasu Abi ke gane mu da ita ko”. “shaida ba matsala bace Aaliya, nasan za ki san abinyi akanta. ni dai kawai ki min alƙawarin daga yau kin tashi daga matsayin Aaliya a idon kowa kin koma matsayin Akila harta ga yaran nan…duk da nasan akwai ranar da zata zo kiji kina biɗarsu “. na amsa ma ta dana amince, kuma na kaɗa kaina nai tafiyata ba tare da tausayinta ba ko ɗar a raina, ba kuma tare da tunanin wane hali zata shiga ba, tunda buƙatata ta rabuwa daku ta gama biya.
kuma fitata babu jimawa sai ga Major ya fito da kai Alhassan, wanda ban ya suka ƙarke da shi ba har ta bari ya fito da kai, kamar yanda bai saurareni ba, haka nima ban bi ta kansa ba…kuma daga nan ban wuce ko’ina ba sai germany, inda nasa aka min aikin a wuyana, aikin gaira babu dalili sai don kawai na samu shaidar amsa sunan Akila, muna yara tayi ciwon maƙogoro da har ta kai ga saida aka ma ta aiki, kuma tabon wannan ɗinkin bai goge ba wanda kuma ta shaidar ɗinkinne su Ammi ke iya ganemu.
ban koma gida ba saida na shekara guda bayan aikin ya warke tabonsa ya fito raɗau dai-dai dana Akila. na rayu a ƙasar Germany ba tare da kowa ba, kuma kullum ina ganin yanda ake cigiyarmu a kafafen sadarwa, ranar kuma dana koma gida naje musu ne a zuwan waɗanda akai garkuwa dasu, kuma mun samu mun kuɓuta sai dai a hanyar tahowarmu da muke gudu muka rabe ni da Aaliya, ban san inda ta ke ba da ita da yaranta.
bayan shekara biyu kuma sai ga wani ya kawo mana Alhassan lokacin yana shekara uku, yana faɗin wai an tsinci yaronne tun yana jariri to azurfar da aka gani a hannunsa me tambarin wannan masarautar ita ta bada shaidar cewa shi ɗin na nanne”. wannan shine silar zuwanka garemu Alhassan, sai dai har kwanan gobe ina tantama akan mutumin daya ce tsintarka akai, nafi tunanin mahaifinku shi ya kaika, wataƙila dan ya rasa yanda zaiyi da kai.
to kunji abinda ya faru, tabbas na aikata muku babban laifi Ƴaƴana, ina kuma roƙonku dan Allah ku yafe min”.
tunda Mami ta fara maganar na ɗora kaina akanta nake kallonta har sanda tai shiru, tana saka handky ta goge hawayenta, kuma har tsawon wannan lokacin hannayenta na cikin na Ummi a damƙe kamar wacca ake shirin a ƙwaceta. gefe ɗaya na zuciyata na jinjinawa Ummina Akila, da ta iya wannan sadaukarwar dan kawai rayuwar ƴar’uwarta ta inganta, ta ƙwammaci ita ta shiga wannan ƙuncin rayuwar, da gatanta da komai amma tsawon shekaru goma sha bakwai tana raye acikin ƙauye, lallai samun zuciya kamar tata abune da zan iya kiransa mara yiwuwa.
kallonta nake da irin kallon mamakin da za’ace matashiya kamarta ta ajiye ƴaƴa kamarmu, dan idan ba wanda ya sani ba yana kallonmu tare da ita zai kirayemu da ƙannenta ne. banda uwa ce, kuma banda ina son albarka acikin rayuwata, kuma ina so duniyata da lahirata suyi kyau, dana kirata da irin kalaman ɗacin dake ƙasan zuciyata, infact ma ni ban san a wanne irin sahun zan sakata ba, amma haƙiƙa ita me son kanta ce, tasan da irin halin da ta tafi ta bar Ummi amma tai biris da rayuwarta, tana can hankalinta kwance, bata da wata matsala, ta manta da cewar ta bar ƴar’uwarta a halin ƙaƙa na ka iya, wanda Allah kaɗai ne yasan halin da ta ke ciki, kuma duk tsawon wannan shekarun bata taɓa waiwayenta ba daidai da rana ɗaya dan ta duba halin da ta ke ciki…lallai duniyarta dabance da ta kowa.
nasa hannu na sha re ƙwallar da ta taru a idona, na bita da ido ina kallonta, sai na tsinci kaina a wani irin yanayin da ba zan iya fassara shi ba, yanayin da nake jin wani abu na ratsani tun daga tsakiyar kaina har tafin ƙafata, kamin wata iriyar ƙauna ta uwa ta keta zuciyata da ilahirin jikina, irin ƙaunar da ubangiji ne kaɗai yasan yawan adadinta, lallai uwa uwace, kuma a koma ya uwa ta ke ɗan da ta haifa yana ƙaunarta, haka itama a kowanne irin yanayi ɗanta ya kasance shima yana ƙaunarta, ƙwarai kuwa haka ne, domin ga shi akaina, domin ƙaunar da nakewa Gwaggona da Ummi ta banbanta da tata, ban taɓa jin irin wannan ƙaunar me wani sirrin tasiri na daban ba sai akanta, ƙaunar da nasan tata ce, tata ita kaɗai.
sai naji a gaba ɗaya duniyata babu wani abu daya rage min wanda ko da daga shi ne ace na faɗi na mutu burina ya gama cika, shine na faɗa jikinta, na rungumeta, na sanya kaina a kan ƙirjinta, naji ɗumin jikinta, wannan ɗumin jikin na uwa, wanda ban samu ba, wanda na rasa shi a iyakar tsayin rayuwata.
wani irin shiru ya ratsa cikin ɗakin asibitin, irin shirun da zuciya ke saƙa abubuwa acikinta, Alhassan dai na zaune kawai akan kujera, wanda ya kafe Mami da ido yana kallonta da mamakin da nake ganinsa ƙarara a saman fuskarsa. ni kuwa hannuna toshe yake da bakina saboda kukan dake neman kuɓuce min tun ɗazu, sai dai naƙi bashi dama, domin a yanzu gani nake kamar lokacin zubar da wani abu wai shi ya hawaye ya ƙare min, tunda har gani ga mahaifiyar da ta haifeni, cike da tarin so da ƙaunata da nake gani ƙarara acikin idanuwanta, dama cikin zuciyarta wanda fuskarta ke nuna hakan.
tun ɗazu kanta na sunkuye tana aikin sha re hawaye, na lura da alamu bata so mu gani dan tana gogewa ta yanda ba zamu gani ba, kuma sai yanzu ne ta ɗago ta dubeni, ta kuma saki hannun Ummi sannan ta buɗe min duka hannayenta alamun na da in taho gareta, ba shiri kuwa jikina na sassarfa na ƙarasa gareta nayi ma ta wata iriyar runguma, rungumar da sai dana saka ƙashin bayanta amsawa, itama kuma ƙanƙameni tai kamar mai shirin sakani a zuciyarta saboda ƙauna. “kiyi haƙuri Maryam, ki yafe min kinji…”. sai nai saurin ɗago daga kaina ban bari ta ƙarasa ba nasa hannu na rufe ma ta baki ina faɗin,”ni babu abinda kika min Mami, Uwa bata laifi ga ɗanta, idan ma tanayi ni dai na yafe miki har abada, nima ki yafe min…abinda kawai nake so naji daga gareki shine ki furta min so, wannan soyayyar da kike ikirarin bani da ita a wajenki…”. sai tai saurin rufe min baki nima,”Maryam inji wane yace miki bana sonki?, aina kika taɓa jin uwa na ƙin ɗanta, ko wancan lokacinma ai wauwta ce akaina, amma wallahi tallahi ina matuƙar sonki, daga ke har ɗan’uwanki…ko kin san da cewar na dawo ƙasar nan neman Akila amma na rasata, sai dai na kusan shafe shekara a ƙasar nan amma ban sameta ba ko da labarinta, nasha zuwa ƙasar nan ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba duk akan yawon nemanku, sai daga baya naga ashe ɗacin raine yasa naƙi amsarku, amma kewarku Marym har kusan illata lafiyata tayi…”.
ni dai kallonta kawai nake gaba ɗaya na kasa kwantanta irin emotions ɗin da nake ji a tare da ni, abu ɗaya kawai na sani, da damar da zan tsaga ƙirjina, na kuma buɗe zuciyata, to tabbas zan ɓoye Mamina acikinta, ko dan saboda wannan nadamar da kuma dana sani da suke saman fuskarta su gushe.
“Dama nasan za ki zo”. Muryar Ummi da ta farka ayanzu ta furta hakan a hankali. wani farin ciki ya lulluɓe Mami saita sakeni ta koma gefen gadon ta rungume ƴar’uwarta. “Akila dan Allah ki yafe min…ni banma san me zance miki ba, bakina yayi kaɗan ya furta duk wasu kalamai a akanki”.
Ummi na goge ma ta hawaye tace,”baki min komai ba Aaliya, idanma kin min na yafe miki…ina Alhassan?”.
Mamin ta saketa tana ma ta nuni da shi, wanda ya taso a yanzu shima fuskarsa cike da murmushi, ya tsaya a gabanta yana mai rissinar da kansa tare da cewa,”barkanki dai Gimbiya, Barkanki dai Ƴar Sarki Jikar Sarki, Barkanki dai jarumar Mace, Barkanki dai Macen da babu irinta a wannan duniyar, Barkanki dai Uwa ta gari, Alhassan na gaisheki, yana miƙo gaisuwa da jinjina a gareki, ubangiji yaja zamaninki, Ubangiji ƙara miki lafiya, ya wanzar da farinciki a rayuwarki, yay miki katanga da dukkan wani abin cutarwa da zai riskoki…daga ƙarshe ina ƙara jinjina Ummina, Ummin Alhassan, ɗanki Alhassan na neman albarkarki”. ya ƙarasa faɗa yana zube gwiyoyinsa a ƙasa, tare da duƙar da kansa a gabanta da dunƙule hannu ya ɗaga babban yatsansa ɗaya.
tana murmushin daya bayyanar da duka haƙoranta ta miƙo hannu ta dafa kansa, tana kuma saka masa albarkar kaman yanda ya nema, sannan ya miƙe yana mai kai ma ta sumba a goshinta, itama ta sumbace shi tana me rungume shi da faɗa masa iya adadin tarin soyayyar da ta ke masa, da faɗa masa cewar taso ace shima ta rayu tare da shi, amma kuma ta godewa Allah daya sa ya rayu tare da mahaifiyarsa, wanda hakan ishara ce gareta, yanzu ta gane baka taɓa tsarawa kanka komai sai wanda ubangiji ya tsara maka.
sannan ta jaye shi daga jikinta tana faɗin,”ina ƴata? ina abar ƙaunata? ina masoyiyata? ina farin cikina?”. ta faɗa tana mai dubana, wanda ni kuwa a lokacin na ɓata fuska, ina tura baki gaba kamar zan fashe saboda kishi. ta ƙasan ido naga yanda ta faɗaɗa fuskarta da annashuwa, kamar kuma ta shiga zuciyata taga abinda ke ciki sai naji tace,”ko dan gaba wannan Ummin Maryam ce bata Alhassan ba, ina fatan kaida Babarka zaku shaida hakan…taho gareni Maryam ɗin Umminta”. ta faɗa tana me buɗe min hannu, na tafi gareta kai tsaye na faɗa jikinta da har sai da ƙirjinta ya amsa, na shiga raira kuka a hankali ina bata haƙurin abinda nayi ma ta.
“Ammi da Abi fa?”. tai tambayar ga Mami. tace da ita,”nan da anjima kaɗan zamu isa garesu”. sai ta ƙara cewa,”anya zan iya tafiya na bar su Malam?, Aaliya bana jin zan iya ci gaba da rayuwar wani wajen ba tare da waɗan nan bayin Allahn ba”.
Mamin tace,”nima na sa ni, kuma ko da nazo na sami irin karamcinsu gareki sai lissafin komawa dake ɗaya ya sauya, ƙafarmu ƙafarsu insha’Allahu, indai har sun amince”.
Yagana muka ji tana faɗin,”ni dai ana shiga da hakkina a wurin nan, kusan rabin awa anata magana amma ni Rakiya ban san me ake cewa ba, to Allah yasa dai ba zancena ake ba”.
sai kuma ta dubi Ummi tana faɗin,”ja’ira, ai ki saka ran idan na maida ke gaban iyayenki saina saka wannan masifaffiyar Kakar taki ta jibgeki”. nace,”amma dai Yagana lokacin da bana numfashi ko? dan me taɓa Ummina ko ruwan sama sai nayi niyya, ah toh”. sai ta harareni tace,”kefa ba kya gane mutum na jin haushinki ko?”. na ƙyalƙyale da dariya ina cewa,”Hajiya Yagana muyi daɗi muyi tsiya, aima idan faɗan mu kai zamu shirya”. tace,”inda kike cutata na sakko daga fushin da nake ki haɗa sunana da kalmar Hajiya”.
sai na ƙarasa gareta na dafa kafaɗarta ina faɗin,”ai kinma gama zama Hajiyar da yardar ubangiji, Yagana indai da rai da lafiya kin dinga zuwa hajji da umara kenan har ƙarshen numfashinki, sai dai idan babu familyn Shaik Tamim a raye”.
ta shafa kumatuna tace,”Allah ya amince…yanzu faɗa min abinda wannan baturiyar ta ɗau lokaci tana faɗa muku”. nace da ita,”ki tambayi Ya Amadu”. ta buɗe baki zata masa magana shi kuma ya ɗaga wayarsa da tai ƙara, kuma kalmar daya ambata bayan amsa sallamar da yay ita taja hankalinmu gareshi kowa y tsare shi da ido, kuma ƙirjin kowa na amsawa.
“innaillahi wa’inna ilaihi raji’un, aina ne?”. bamu san me akace masa ta cikin wayar ba sai ji mukai yace,”dan Allah Malam ka taimaka ku miƙa shi asibiti mafi kusa, yanzu yanzun nan zamu ƙaraso da izinin Allah, dan Allah ku taimaka kuyi duk abinda ya dace gani nan ƙarasowa”.
lokacin daya sauke wayar daga kunnensa kowa ya haushi da tambayar meke faruwa?, yana nufar hanyar fita yace,”Kabiru ne yay hatsari, kuma hatsarin me muni dan yanzu haka ma anata ƙoƙarin ciro shi daga cikin mota ne abin ya faskara”. ban san sanda nai mutuwar tsaye ba, ta ke kuma naji wani dunƙulallan abu ga me da Ya Kabiru ya nemi waje ya tsaya a zuciyata, kamin kuma furucin Ya Amadu ya shiga haska min hoton faruwar abin a idanuna, hoton Ya Kabiru acikin jini, acikin mummunan hatsarin da aka ambata, Ya Kabiruna dai!, sai nai saurin gimtse idona ina girgiza kaina dan kawar da wannan hoton dake haska min.
daga can kuma sai naji Mami na faɗin,”tabbas wannan hatsarin shirya shi akai, ba hatsari ne na haka kawai daya same shi ba, wani ne a gefe ya shirya masa shi saboda yana so yaga bayansa”. Ya Amadu da nake gani dishi-dishi naga ya dakata da fita ya juyo yana kallon Ummi. kuma Baba sai yace da ita,”Akila me kike cewa ne?”. Yagana tace,”inaga fa ciwon kamar har da surutai ya sata ko?”. tai maganar tana me gyara ɗaurin zanenta tare da cewa Amadu,”kai shige mu tafi ka bar batun wannan zaran, Kabirun yana ina aka ce maka?”.
Ummi ta buɗi baki taci gaba da cewa,”Malam akwai ɓoyayyen sirrin daya jima yana faruwa a gidanka wanda babu wanda ya san da shi saini, ni ɗinma kuma daga baya na sa ni, wannan SARAN ƁOYEN da aka jima anayi acikin wannan gida tun daga lokacin da Maryam ta kamu da ciwon ƙoda har zuwa kan wannan gaɓar ta hatsarin daya sami Kabir, hatsarin da bashi aka shiryawa ba Amadu aka shiryawa shi sai kuma shirin ya faɗa akansa…sai dai zan iya cewa ba kuskuren aikin aka samu ba, canja tsarin akai”.
tai shiru da wani guntun murmushi a saman leɓenta na baƙin ciki da takaici kafin ta furta,”Amarya! Malam Amarya ce ta shirya wannan hatsarin da manufarta da ban santa ba, amma tabbas aikin Amarya ne, aikin amarya ne ɗirkawa Maryam wannan ƙwayoyin da suka haifar ma ta da matsalar ƙoda, kuma aikin Amarya ne zubawa Maryam abinda ban san menene ba har tai wannan ciwon cikin, kuma aikin Amarya ne yi ma ta turen wannan macijin daya rutsa da ita a banɗaki, Malam dasa hannun Amarya akai kidnapping ɗin Maryam, kuma aikin Amarya ne yin wannan allurar gubar wa ƙafar Gwaggo har ta zama silar mutuwarta, sannan akan gaɓar shirinta na yanzu shine taga bayan Ahmad da Kabir…kuma Malam idan nace maka gonakinka da aka ƙwace ba gwamnati bace Amarya ce ba lallai ka gasgatani ba duk da cewar waɗannan magangunan nawa ma ba lallai su zama abin yarda a gareku ba, tunda banda wata hujja, amma idan baku yarda dani ba nasan zaku iya Yarda da Kabir wanda ya san komai…fatana da adu’ata shine Kabiru ya rayu ko dan saboda alkadarin Amarya ya karye, kuma ko dan ya tsaya min wajen kafa muku hujjar da zaku yarda da abinda na faɗa muku…Ahmad kai gaggawar zuwa inda yake da wuri, ai saurin miƙa shi asibitin da zai sami kulawa duk da ba likitocinne da iyawar ba, ubangiji shi zaiyi iyawarsa”.
abinda zan iya cewa shine ba duka naji maganganun nata ba, na san dai ƙafata ta riƙe kamar an kafani ne a wurin, haka kuma ban san lokacin da ƙafata da nake tunanin ba zan kuma iya ɗagata ba sai sanda naga Ya Kabiru a gabana da lafiyarsa, na motsa na kai bakin ƙofa na tsaya daga gefen Ya Amadu, nai saurin miƙa hannu na riƙo shi saboda juwar da naji tana neman ɗibana, har ga Allah ban san me nake ji ba, ban kuma san meke shirin faruwa da ni ba, idona da basa gani da kyau Ya Kabiru kawai suke son gani domin su washe, kamar ƴar maye ko kuma wadda ke cikin nauyin bacci na tafi luuu na faɗa jikin Ya Amadu wanda yay saurin daidaita min kaina a saman ƙirjinsa daidai lokacin daya sauke wata doguwar ajiyar zuciya da zan iya cewa daga ita ban sa ke jin komai ba.