ALKAWARIN ZUCIYA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

ALKAWARIN ZUCIYA COMPLETE HAUSA NOVEL

ALKAWARIN ZUCIYA COMPLETE HAUSA NOVEL BY M SHAKUR

Wasa wasa 2weeks kenan bataji muryan Aliyu ba, gidansu sai gyare gyare ake na bikin da za’ayi nata dana yayyinta, Anty Mariya was just like a mother to Khairy dan mai gyara ta dauko daga Sudan aka bata daki daya tana gyara Khairy in and out, Khairy tarame tun tana kuka da hawaye yanzu tasoma mara hawaye kawai gatanan ne, yau zasu fara exam duka duka 1 week zasuyi sugama, shiryawa tayi cikin hijabi har kasa da nikabi duk wani abu datasan Aliyu zai iya ganinta yaganeta dashi ta chanza sanan tafito tama Anty Mariya sallama, amotan da Baba yasiyawa Anty Mariya da direbanta tadauka suka tafi bayan ta sanar da mai gadi idan wani namiji yazo nemanta ace batanan, har gaban department dinsu tasa direban Anty Mariya yayi parking sanan tawuce tashiga exam hall wanda yake zasuyi 2hrs aciki tana gama paper ta bama tajira kawayenta ba tafito tana tafiya ahankali kamshin Aliyu taji kaman daga sama amman tadaure taki dago kanta saima sauri data kara zuwa motan, baya taje zama amman saitaje gaba tabude ta zauna suka wuce saida suka sanyi nisa sanan tajuyo Aliyu ta hango tsaye yana sanye da kananun kaya yana kallon exam hall din tasan ya tsaya ne yana jira afara fitowa kozai ganta jitayi kuka yazo mata nikabin takama afuskanta tana kuka sosai.

Wasa wasa yau Friday yau tagama last paper ta yauma still saida taga Aliyu a school dinsu yarame sosai yay duhu yau kukan datayi yafi na kullum dan tasan yaune last day dazata ganshi dagayau bazata kara fita ba ahaka suka tafi.
Parking sukayi a compund dinsu da ake fentin tsakar gidan, ahankali ta sauko nikabin kanta tacire sanan tawuce flat dinsu, ahankali tabude kofa tashiga Zayn tagani zaune afalon su taci gayu yay wani irin bala’in kyau tana magana da Anty Mariya ganinta yasa yadago kai ya kalleta dawani irin sauri ta sauke kanta kasa ahankali tace “ina yini” sanan tawuce dasauri tai stairs. “Ummulkhairy” yakira sunanta ahankali chak ta tsaya batare data juyoba, tashi Anty Mariya tayi tace “bari kaga naje na dudduba aikin da akeyi Zayn” tai maganan tawuce ta gefen Khairy tai sama abinta, ahankali Zayn yace “Khairy” juyowa tayi ahankali kanta nakasa sanan ahankali ta taho yana binta dawani irin kallo ganin yanda takara kyau fatarta harwani sheki take, zama tayi akan kujera kanta akasa, dan murmushi Zayn yayi sanan yadauki wani Leda da flowers red keciki dake gefenshi sanan yataso yazo har gabanta tsugunnawa yayi agabanta sanan ahankali yadaura hannunshi kan nata wani irin rawa jikinta yafara dasauri takalleshi wani cute smile yasakin mata sanan ahankali yakama hannun nata yana kallon fuskanta yasamata flowers don aciki yace “congratulations u are now a graduate wife” wani sarawa taji kanta yayi dawani irin sauri ta lumshe idanunta sanan tabudesu ahankali takalli flowers din Aliyu kawai taji yafado aranta, sharrrr hawaye yazubo daga idanunta dasauri Zayn yace “why are you crying” hannunshi yakai kan fuskanta zai sharemata dasauri ta kauda fuskanta tace “kaina keciwo I want to sleep thank you” sanan tabi ta gefenshi ta tashi dasauri zata wuce karaf taji yakamo hannunta, dawani irin sauri tajuyo takalleshi tashi yayi ahankali yana kallonta sanan yazo ta gabanta Ya tsaya yay folding hannunshi akirji ahankali yace “I love you Ummulkhair! And I wanna spend the rest of my life with you! I accept you as my wife cus ina bala’in sonki! Allah yajikan Mama data bani ke, and I will forever be greatful to her data zabeni a matsayin soulmate na yarta, Ummulkhairy Zayn love you alot” wani irin fizge hannunta tayi dawani irin gudu tai stairs zuwa dakinta maida kofa tayi tarufe tasa kwado sanan tawani cillar da flowers nashi gefe jikinta na kyarma sabida kalamanshi Aliyu kawai suka dinga tunamata fadawa gado tayi tana kuka ahaka bacci yay awon gaba da ita.
Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.

wa.me/+2347012181461
To chat me up on watsapp

This novel is 1k
Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461
Thank u❤️
5️⃣1️⃣

Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.

wa.me/+2347012181461
To chat me up on watsapp

This novel is 1k
Pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461
Thank u❤️

Yau tun safe yama kasa tashi yakai kanshi bayi yay alwala yay salla sabida mugun zazzabin dayake, Abba dabaiganshi a masallaci ba daman jiya Gwaggo tacemai baida lpy amman da Aliyun yazo wajen ya tambayeshi yacemai lafiyanshi kalau yasa yana shigowa gidan daga masallaci straight side din Aliyun yayi ahankali yabude kofan dakinshi yashiga dakin tsaf babu kowa a falo bwdroom nashi yayi yana budewa kakarin aman Aliyu yaji abayi, Aliyu tun yana yaro ciwon shi always comes da amai dawani irin sauri yashiga bayin ganinshi a duke yasa Dad yace “Subhanallahi Aliyu” ruwa yatare Awani bowl yakawo mai da kyar ta kuskure bakinshi sanan Dad ya wankemai fuska sanan yadaukeshi yafito dashi yanajin yanda jikinshi yay zafi, bargo yasa ya lullube shi sanan yajuya zai fita dawani irin sauri Aliyu yakama hannun Dad ahankali yace “Dady” dasauri Dad yazo gaban gadon zama yayi yace “Aliyu menene” ahankali yace “Dad last 3weeks dasuka wuce Ummulkhair called me cewa zasu village, and a village nasu basuda network, Dad I’ve been going to school masu all through last week sabida zasuyi final exam amman batazo ba, Dad I am so worried did something happen to Khairy?” Shiru Dad yayi yana kallon Aliyu duk cikin yaranshi babu wanda yadauko zuciya da hali irin nashi kaman Aliyu, Aliyu bai iyason abu ba, bai kuma iya kin abuba, Aliyu loves da zuciya daya, and he loves completely without rage space, Aliyu is very cool, baida hayaniya da rigima amman akwai zuciya na masifa. Ahankali Dad yace “sabida bakaga Khairy bane yasa kake neman kashe kanka Aliyu? When was the last time kaci abinci” murya araunane yace “I can’t remember Dad” shiru Baban shi yayi yana kallonshi sanan anatse yace “yanzun nan zan taho maka da magani da abinci write down address na gidan su Ummulkhairy for me zanje gidansu, I will go and check her up for you daganan zan nema maka aurenta wajen mahaifinta kafin kaje ka kashe kanka sabida soyayya” Dad yay maganan cikeda tausayinshi dakuma jin haushin shi duka atare sanan ya tashi yafice, yana fita daga dakin sukaci karo da Gwaggo datasa Meena ta turata akeke ganin danta yasa tace “haba nakasa bacci lafiya tun tsakar dare Nike damun ja’irar nan takawoni naduba takadirin yaron nan dan jikina yabani baida lafiya amman taki wai nabarta tai bacci yanzu ma saida nahada mata da kuka tafito dani, wlh Abdul bakai dacen yara ba ko kadan, shikuma ina yake yana cikin ne”? Ganin yanda Maman shi tadamu dan shi kanshi baisan iyakacin irin son da tsohuwar nan kema Aliyu ba yace “muje Gwaggo baida lpy amman yanzu zan bashi magani yayi bacci” kirji Gwaggo tafara tace “hala yanata amai dan cutan Aliyu kenan duk ciwo yay ta uban amai na shiga uku, meke damu shi eh gayamin” shiru Dad yayi ganin yanda tadamu ihu tamai tace “nace kagayamin Abdul” kallon Meena yayi yace “wuce kitafi” wucewa ahankali tayi ta tafi tsugunnawa Dad yayi yace “Gwaggo sabida yarinyar nan dayakeso yake rashin lafiya wai tunda tai tafiya zuwa kauye bai kara samunta awaya ba ko ganinta” fashewa da kuka Gwaggo tayi tace “to laifin wa inba nakaba, tuntuni nike damunka muje mu newama yaron nan Ummulkhairy amman kaki wai abari tagama makaranta yanzu idan wani aka bamawa fa iyye, kaini daki na shirya yau kafata kafanka gidan su Khairiya zamu billahillazi kuwa” kaita dakinta yayi sanan yawuce yahado magani yabawa Aliyu da shayi dakanshi sanan yamai allura kafin mene bacci yakamashi fitowa yayi yakoma nashi dakin shiryawa yayi cikin manyan kaya yana fitowa tsakar gida yaga Gwaggo itama ta shirya cikin lafiyayen atampan ta jajir dashi da aka mata dinkin bubu kan kekenta tai kyau sosai fesfes da ita duk wanda yaganta yaga Yar fulani. Girgizakai kawai Dad yayi cikeda takaici yawuce dakin Aliyu Yar takardan daya rubutamai address yakalla to ai yasan gidan nan gidan Alhaji Muhammad shine Dr Mama data rasu, yasan sunada yarinya mace though baitaba ganinta ba cus yasan basu fadama yarinya Maman nada cancer though baisan sunanta ba, ajiyan zuciya yasauke sanan yafito Gwaggo yasa abayan mota yasa keken ta abaya sanan yashiga gaba yaja motan har zuwa gidan Baba.
Dayake gateman yaganesu budemusu gate yayi sanan yawuce ciki dasauri bin gidan da kallo Dad yayi ganin kaman ma shagalin biki akeyi ko minti daya ba’ayiba Baba dakanshi yafito hakan yasa Dad yasauko daga mota yana bashi hannu yace “Dr barka da zuwa” murmushi Dad yayi yace “mun same ku lpy ina zuwa tareda Gwaggo nake” yay maganan yana ciro keke sanan yazaga yafito da Gwaggo yadaura ta akai ganin tsohuwa yasa har kasa Baba ya tsugunna yace “ina kwana Gwaggo” washe baki yayi yace “lpy dan albarka ya aiki” dasauri Baba yace “Alhamdulillah kushigo yau gidan cike yake dayake ana shirye shiryen biki ne” dasauri Gwaggo tace “bikin wa” murmushi Baba yayi yana bude musu kofan flat dinshi dan a shiga da Gwaggo yace “na yarana” shiga da ita akayi, falon Baffa ne zaune sai Mom dan Ammi bata biyosu ba dan haryau bata shiri da Baffa, sai Anty Mariya afalon, shima Baffa na ganin Dad yace “aaa Doctor kaine” murmushi duk akayi aka shishiga gaisawa Anty Mariya taje takawo musu lemo sanan aka zazzauna akai shiru Gwaggo takalli Baba tace “kaine mahaifin Ummulkhairy” dasauri Baba yace “eh nine” Gwaggo zatai magana Dad ahankali yace “Gwaggo” shiru tayi sanan anatse Dad yakalli su Baba dake kallonshi yace “duk kun sani anan, sunana Abdullahi Abdulwahab Yola, ni likita ne, Gwaggo itace mahaifiyata, matata daya yanzu haka, tafarkon tarasu, yarana bakwai namiji daya sauran duk mata yanzu saura mata uku agida sauran sunyi aure, Yarona na farko sunanshi Aliyu Police ne shi dudda lawyer ne dan abinda yakaranta a school kenan he’s a barrister but he choose aikin police sabida mahaifiyanshi data rasu abinda taso yazama kenan, ASP Aliyu Hydar though Kwanan nan akama karamai girma” dasauri Baba yace “Allahu Akbar ai mu dukanmu nan munsan Aliyu, yanzu dama Aliyu danka ne kaga yanda duniya yake ko amini” Baffa yagayadamai kai sanan yashiga bama Gwaggo da Dad labarin abubuwan da Aliyu yana yarsu Gwaggo sai washe baki take kaman gonna auduga.
Anatse Dad yace “to Alhamdulilah akwai abinda yakawo mu gidan nan naku yau dasafen nan nida mahaifiyata” Dad yadanyi shiru sanan yace “d’ana Aliyu kwanankin baya yazo yasameni yasanar dani yanason Ummulkhairy amman ita tafiso sai tagama makaranta sanan yanemi aurenta…….” Nan yabama su Baba labarin komi har zuwa tafiyan kauyen datace sunyi da yanda Aliyu yadamu baigantaba har zuwa abinda ma yasa sukazo yau shine rashin lafiyan dayakeyi dakin shiru kakeji kaman ruwa yacinye kowa.
Anatse Baba da mamaki ta cinyeshi yakalli Anty Mariya yace “dalilin dayasa Khairy ke zuwa exam da nikabi da hijabi har kasa kenan”? Ahankali Anty Mariya tace “bansani ba gaskiya” shiru Baba yayi sanan ahankali yakalli Dad da Gwaggo ahankali “yashiga basu labarin rayuwansu daga farko har zuwa ranan da Khairy tasani har zuwa yau wanda bikinsu jibi ne ranan asabar yau alhamis…. Baba yakarashe da “Inaga Khairy takasa fadamai gaskiya ne saisa tamai karyan mun tafi kauye” fashewa da kuka sosai Gwaggo tayi afalon dasauri aka shiga bata hakuri, sauka tayi daga kan kekenta ahankali kowa na kallonta dukawa datashiga kokarin yi yasa kowa yamike tsaye ganin tsohuwa tukup tukup zata duka musu dawani irin sauri Baba yatashi yariketa yace “Gwaggo dan Allah karki duka mana” cikin kuka sosai tace “kuwa Allah kubama jikana Auren yarku, wlh sabida marigayiya batasan Aliyu na bane wlh Aliyu zai kulamata da Khairy, zai rikemata Khairy amana, dan Allah kuji tausayin Aliyu na kar wani abu yataimakeshi, Baban Zayyanu Dan darajan iyayenka kubama jikana yarku” jikin kowa yay sanyi babu wanda ya iya cewa wani abu, Dad da jikinshi yamutu da kyar yatashi Gwaggo dake kuka sosai ajikin Baba yakama yanadan murmushi yace “Gwaggo zoki zauna kiga” dakyar ya zaunar da ita sanan yakalli su Baba dakowa jikinshi yay sanyi zaiyi magana Baba yakama hannunshi yace “da ace babu zancen Zayn babu abinda zai hanani baku y’ata naga Aliyu nakuma yaba da tarbiya hankali da natsuwa irin na Aliyu, Aliyu yaro ne nagari nai kare yancin kowa, kuyakuri Dr, kuyakuri” dasauri Dr yace “dan Allah kudena cemin nayahakuri mutum baya wuce rabonshi inda Khairy ta Aliyu ce zai sameta cikin sauki, Allah ubangiji ya Sanya alheri, Allah kuma yabasu zaman lpy, bari nakai Gwaggo gida sai anjiman ku” har wajen suka rakosu Gwaggo na kuka sosai yasata amota jikin koCwa yay sanyi.
Wanan Littafin na kudi ne karki karanta batare dakin biyaba kika karanta min littafi ban yafeba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button