GIDANMU COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

GIDANMU 1&2 COMPLETE HAUSA NOVEL

GIDANMU COMPLETE HAUSA NOVEL

Tana Fitowa suka kusa cin karo dashi ya Fito Daga Dakinsa Zai Shiga Dakin Abba Baya taja Tana kallonsa Kafin tace”Gud Mrning ya Yusuf…!
Kauda kansa yayi Saboda baya so ta Fahimci yayi kuka yace”Mrning Sisy how was ur Nite..?Yafada Cikin Sanyinsa kamar ko yaushe.
Da kallo ta Bishi ganin yana ta kauda kai sama da kasa karemai kallo Dogo ne sosai mai Dan Jikin murjewa Sannan Shima Fari ne kamar ita sai dai ta Dan Fishi Haske suna Tsanananin kama da juna Kamanin Abba suka Debo kamar an Tsaga kara.
Cikin Zargi da Tantama tace”Ya Yusuf Lafiya..? Domin bata ga yayi wani Shirin tafiya aiki ba kamar yadda aka saba ba,Kansa ya sosa yana Fadin”Lau..Me kike jira baki tafi school ba..”?Maimuna tace”Yaya kaifa nake jira..Har na gama Breakafast baka fito ba..”Hannu kawai ya saka a gaban Aljihun Jallabiyansa ya Dauko 1k ya Mika mata ta karba da mamaki kafin Tace wani abu ya Rigata da Fadin”Ki hau adaidaita kitafi makaranta yau ba zan je aiki ba ina gida..”Yafada Lokaci Daya Yana Kokarin Rabata ya Shige Dakin Abba da Sauri taRiko Hannunsa yakiya waigo sai ta koma ta gabansa ta Tsaya tana Kallon yadda Idanuwansa sukayi Jajir,alamun yayi kuka Cikin Tsausayinsa tace”Meya faru ya Yusuf..?kuka fa kayi..?
Da sauri yace”Kuka kuma Sisy..? Ni ban yi kuka ba..’
Yafada yana kokarin Sakin Mirmishi,itama Mirmishin ta Sakarmai Mai ciwo kafin tace”Kuka kayi ya yusuf..Ko baka Fadamin ba Nasani..”Ta karishe Fadai itama Hawayenta suna zubo mata Da Sauri ya Dafa Duka Kafadunta yana Fadin”Me ye na kuka Sisy..? Bafa kuka nayi ba kaina ne ke Ciwo Shiyasa kika ga kamar nayi kuka..”Kara saka mai kuka tayi Tana Fadin”Bari naje na kira Anty Safiya na gayamata kila ita Zaka gayamata meke damunka..”Tafada tana Kokarin wucewa da sauri ya Rikota yana Fadin”Kada ki kirata Munari
Da sauri ta kallesa jin yadda yayi mgana sai taga kawai ya gyadaa mata kai yana fadin”Domin ko kin kirata bazata zo ba..Itama an Rabamu da ita Sisy..”Ya Karishe Fada Hawayen DayakeBoyewa suka Zubomai,Maimuna Dataji abun Daga sama Taji Jikinta yakarayin sanyi,Cikin wani yanayi tace”Itama din Yaya..? Itama din an gayamata Abban mu Mahaukaci ne,Sannan bamu da uwa bamu da kowa sannan itama an gayamata ya Imran bayajin mgama yana Shaye Shaye..? Itama din Am bata Labarin Gidanmu ko Yaya.. ?Ta ke Fada tana wani Gunjin kuka Da Sauri ya Rumgumeta kamkam Yana Fadin”An gayamata Sisy..An ce ma iyayanta irin kallon da Mutane suke mana Munari..Itama na rasata Munari..”Haka yake Fada yana kuka itama kukan take aka rasa mai Lallashin Daya acikinsu Sai da suka gaji kana suka saki Juna Maimunatu bata tsaya ba ta kwashi Gudu Zuwa Dakin ya Imran Dake gaba Kadan Da Dakin Abba da Ya Yusuf da kallo ya Bita Ita yafi Tsausayi gwarasu maza ne ammh itama fa mace ce,tafi su Rauni,
Hawayensa ya Share da Sauri ya Tura Kofar Dakin Abba ya Shiga da Sallama.

Bubbuga Kofar ta shiga yi Tana Kiran sunansa,Yana zaune akan Kujera kwara Daya Tal Dake Cikin Bedroom din nashi Yana Kishingide Taba ne a Hannunsa yana Busawa Hayaki ta baki ta Hanci Bai ma jinta Bugar Kofar Domin ya shigawata Duniya Sai zuwa Chan yaji Kiran sunansa Da Buga Kofar Bude Jajayen Idanuwansa yayi yana mamakin waye yazo zai Dameshi.?ko yace zai katse mai Jin Dadi Mikewa yayi a Fusace Dauke da Taban a Hannunsa ya isa ga Kofar ya Bude yana Fadin”Wai Wayeee…!
Yafada Cikin kakkausan Muryansa Kallon kallon sukayi Tsakanin shi da Maimuna wacce ke Zubar kwallah Sama da kasa yake Kare mata kallo Lokaci Daya ya Karkata kansa gefe ya Saka Tabarsa abaki yayi mata wata Zuka,kafin ya Fesar Da Hayakin zuwa Fuskar maimuna Baya Taja Tana Toshe Hanci Saboda bata kaunar warin Taba.

Kara Hade rai yayi ganin Tanawani Toshe Hanci Cikin Muryansa ta Kaushi ba Tausasawa yace”Ke…Ubam wa kike Toshe ma Hanci..?Ni sa”an ki ne..? Yafada yana Nunata da yatsa kafim ya Cigaba da Fadin”Cire hannun ki a saman hancinki..In ba Haka ba kika Tunzurani wlh zan kamaki na Danne ki sai na Karar da Hayakinta a cikin bakin ki..”Ya karishe fada yana Nuna mata Taban hannunsa Dake Kunne tana Fesar da Hayaki Lokaci Daya yana Zare mata Jajayen manyan Idanuwansa kamar na mace.
Dagowa Tayi tana kallonsa Tana kukan Tsausayinsa da Tsausayin kansu shima sai Lokacin ya Lura da kuka take Da sauri ya kwara ware ido yana kallonta,Kamar yadda take kallonsa Dogo ne sosai Har yafi Yusuf Tsawo kuma Shi Faffada ne Da kuma Kirar Karfi da Zafi Jikinsa yana Cure ne Domin baya wasa da Motsa jiki Fari ne shi ammh ba sosai ba Sunfishi Haske,yana da manyan Idanuwa mai Dauke da Doguwar Fuska Sai Sajensa daya Zagaye Bakinsa,wanda ya fara koma baki baki saboda busa taba,kansa Nannade yake Da Askin nam na Dada,kuma ya Dace dashi Domin ya Tafi da bakin gashin Fulanin daya wani Nannade Bisa kansa Daga Shi sai Bakin Dogon wando Ko Riga bai Dashi Faffadan Kirjinsa mai Cike da gargasa duk yanawaje ne.

Kukan da Maimuna take yi ya Dakatar dashi Domin shi bai ma Lura da kuka take ba Da sauri ya kariso gabanta yana Fadin”Ke..Kukan me kike yi ne.? Ya fada Cikin Daga murya da Bayyana Damuwa Domin Duk Iskancin Imu yasan Gidansu Baya kaunar yaga wani Daga Cikinsu Cikin Damuwa kasa mgana Tayi har sai da ya Harzuka ya Daka mata Tsawa yana Fadin”U better stop dis Nonsess ki gayamin abunda ke Faruwa…Tun kafin na jimi ki Rauni anan wajen..”Ya karishe Fada Lokaci Daya ya Dukan Bangon Wajen da Hannunsa mai Dauke da Taban Wacce ta Fadi kasa ya sa Kyakywan Farar kafarsa ya Take Wutan ko Zafi bai ji ba saboda Zuciya da Sauri Maimuna taja Baya sanin Halinsa in yayi wannan Bakar zuciya sai ya iya mata Targade ai tun kafin ya juyo tace”Ya imu..Dama..Daman ya Yusuf ne ke kuka..”Ido ya sakar mata Cikin wani yanayi kafin a Hankali ya Furta..”Kuka..? Cikin alamun Tambaya..”
Kai ta gyadamai Cikin Kaushin Muryansa yace”Yana ina..! Da sauri tace”Yana Dakin Abba..”Bai ma Tsaya Sauraranta ba ya wuce Fuu kamar zai tashi Sama da Sauri ta maramai Baya zuwa Dakin Abba.

Yusuf na Zaune gefen Abba yana Ballamai mgani yana bashi yana sha Daga Gefen Dirowam gado kuwa Mug ne na Tea da Bread wanda Yusuf din ya Dauko ma Abba yasha Saboda yasha mgani Suna Cikin wannan Halin Imran ya Bango Kofa ya Shigo Cikin Muryansa mai Cike da Amo da Sauti yace”Uban waye ya saka ka kuka Yusuf…!
Ya fada Cikin Sauke Jajayen Idanuwansa kan Yusuf din wanda bai ma dago ya kallesa ba illah Mikama Abba mganin Daya Ballo masa ya karba ya saka abaki yabi da Ruwa Lokaci Daya Yusuf ya karbi Ruwan yana Fadin”Abba ka kwanta ka Huta don Allah..”

Abba bai yi mgana ba illah yabi Yusuf da kallo yajuya yabi Imran da Munari da kallo kamar yana so ya Tantance su,Ganin haka yasa Yusuf ya kamashi ya kwantar Lokaci Daya yana Rufamai Bargo Daga kafarsa yana Fadin”Kayi barci..Wannan kuma Daya Shigo Imu ne Abba Mara Hankalin kanin nan nawa ne..”Yafada yana dan Mirmishi sai Shima Abba ya Murmusa yana kallon Imran wanda ke tsayr Kikam yana kallon Abba Yusuf ne ya waigo yana kallonsa kafin yace”Kai wai yaushe ne zakayi hankali ne..? Sai an ce ka gaida Abba zaka gaishe shi..?
Imran ya wani Dage Hanci yana Fadin”Indai banyi hankali at age of 30 ba Kila sai age of 36..”Yafada lokaci Daya yana karisa ga Abba Hannu ya bashi Suka Tafa yana Fadin”Abba kana Hutawarka fa..!Kaji Dadinka Allah ya baka lafiya..”Ya karishe fada yana Shafa Gemunsa Abba yayi mai Dariya kafin yace”Allah yayi muku albarka..”Yana Fadin haka kuma sai duk sukayi wani iri Yusuf kuwa Hanyar fita ya kama Bazai iya tsayawa ba Fita yayi Daga Dakin Maimuna tabi Bayansa Imran kuwa Durkusawa yayi gaban Abba Idanuwansa ya kara Kadawa yace”Allah ya baka Lafiya Abba..”Yake Fada yana Rike da Hannunsa Kansa Abba ya Dafa Yana mai Mirmishi Cikin Muryan Barcin Daya Fara Fuzgan Abba yace””IMRAN…..!
Bai karisa ba barci ya Tafidashi Dayake mgangunan akwai na Barci Imran Dake kallon Fuskar mahaifinsu yaji kamar ya Kurma Ihu Kai ya girgiza kafin ya mike Dakyar ya iya Sabule hannun Abba ya gyaramai kwanciya ya kuma Rage mai karfin Sanyin Dakin kafin ya Fice Zuwa Falo anan ya iske yusuf da Maimuna suna Zaune mgana suke suna ganinsa sukayi Shuru,bai damu ba yana zuwa gaban Yusuf ya tsaya yana Fadin”Kukan me kake yi ne kamar wani mace..?kasa wannan Shagwabbiyar kanwar naka itama tazo Tana Damuna da kuka..”Ya fada Lokaci Daya yana Tura Hannunsa Cikin aljihun wandonsa sai ga Taba ya Fito da ita da Lether ya saka abaki ya kunnata ya Zuka ya Fesa musu Hayakin yana Fadin”Ina Tambayarku kumin Shuru..Kada ku bari na Harzuka fa..Mahaukaci kuka maidani ko me..?
Ya karishe Fada yana Fitar da Hayaki ta Hanci Dukkansu kallonsa suke ba wanda yayi mgana Daga kafa yayi ya Buga Jikin Kujera Cikin Tsananin Fushi yace”Nace waye ya saka ku kuka ne..?Yau yagane ba wanda ya isa ya saka wani Daga Gidanmu Zubda Hawaye..”
Yusuf dai baice komai ba Maimuna ce ta Tsorata taja Baya Tana Fadin”Safiya ce..!

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button