GIDANMU COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

GIDANMU 1&2 COMPLETE HAUSA NOVEL

GIDANMU COMPLETE HAUSA NOVEL

Umaima kuwa ta samu Daddy a waya Dayaga Kiran sai da gabansa ya Fadi bai da lambartaa ammh kiran Waya da Daddare haka yana Fadar ma Da Mutane gaba,Umma Tayi barci Tun Dazu Shima Wani lissafi ya Tsaidashi yasa bai yi barci da wuri ba.
Koda ya Daga Kiran Kukan Umaima ya Faramai Maraba Dakyar ta Tsagaita Tamai bayanin Abunda ke Faruwa Salati ya saka Cikin Rashin jin Dadin Abunda ya Faru ya lallahi Umaiman yace mata da Safe zai kira Abba in ta kama ma zasu zo nan Abuja Haba ai bazasu bari haka ta Faru ba,da kalaman Daddy Umaima taji Sanyi tasan Zasu ja Hankalin Dad ya Dawo da Mami gida.
Salatin Daddy ya tada Umma Daga Barci,Cikin muryan barci Take Tambayansa ko Lafiya cikin Damuwa yake Fadamata abunda ke Faruwa ita kanta Sai ta Dafe Kirji Tana Fadin”Saki..? Abun har yakai ga Saki ne Abban Inttee..?
Cikin jimami yace”Gashi kuwa..Allah dai ya kyauta bari na kira Ya malami muji yadda zamu yi yariyar tana ta kuka ko Saboda yaran..Da kuma an Riga an girma bai kamata ba..,!
Umma ta Sauke Numfashi Tana Fadin”Karamar ce ta kira ko Sajidar..!
Daddy yace”Karamar ce Umaima..!
Umma tace”Allah ya kyauta..Da ka bari sai gobe da safe ka Kirasa yanzu Dare fa yayi sai ka Tayar mai da hankali..!
Kansa ya jinjina alamun Ya yarda da mganarta,Barin kiran Wayar yayi ammh Lissafin da bai karisa ba kenan abun ya Damesa da asuban Fari ya Kira Abba ya Fadaamai yana ma Hanya ne zasu dawo daga masallaci su Yusuf sukayi gaba suka barsa suna mgana shi kanshi bai ji Dadi ba suka Tsaida mganar dashi da Daddy zasu Tafi Abujan su samu Baffa Kabiru Ranar Alhamis,Saboda Abba zai Fara aiki Ranar Monday ne da haka suka Rabu Zukata duk ba Dadi.
Abba bai yi Zencen da kowa ba Shima Daddy bayan Umma bai Sanar ma Kowa ba Baffa Kabiru bai kirasu ba kuma suma basu kirasa ba suna Jira ne kawai ya gansu kwatsam
Aranar da yammah Yusuf yakai Abba Wajen Siyan Mota yace ya Zabi Wacce yake so Abba ya Zabi prado babbar ta Imran baka mai kyau miliyan 6 Sabuwarta nan take yusuf ya Biya kudin bai kai ba Sai da ya Hada Sauran kudin acct dinsa.
Tare da Motar suka isa gida atare Yusuf ya Sallami Wanda ya Rakosu da Motar.
Zuwan Motar ne yasa da Munari ata fadama Inteesar yasa ta jawota Dole tazo taga Mota tayima Abba Murna,Tana ta wani Sunne kai Abba ya jawota Jikinsa yana Fadin shi baya Suruka da ita yarsace ita Ya yusuf kuwa ta Daina Hada ido dashi gogan kuwa Tunda ga Ranar bata kara ganinsa bai nemeta ba itama bata nemesa ba.
Ranar Laraba sun fito daga Lecture din Safe ita da Munari Cafteria suka je suka siyo Lemo da Biscuit,suka Samu wani Inuwa bakin wani Department suka Zauna sun fara shan Lemon kenan suna Hira Wayar Munari tayi kara Tana Dubawa Taga Hafsah ne ta Dauka suna mgana Inteesar na kallonsu duk kan Shagalin da zasu yi da Bikin su ne Suna Fadin zasu bude Bride group za”a Saka ango da abokansa suma zasu sako kawayen Bride.
Munari na Dariya tace”Ke ango bai da Babbar Waya sai Rakani Kashi..!
Gabadaya ita da Hafsah suka saka Dariya Inteesar ta Hade rai Tana Hararanta.
Daga chan bangaran Hafsah tace”To sai mu kyalesa Daman ko yana dashi ke zan jona ki sako manashi..!
Munari ta waro ido Tana Fadin”Wa ni..?Rufamin asiri waya aikeni ballatana yaga na Dade..?
Wlh badani ba yaga ni Sakashi ki auna yadda zaizo ya sauyamin kammani..!
Dariya Hafsah ta Saka mata Munari ta Cigaba da Fadin”Abokai kuma Daya na Sani Ya Sagir..Kuma bamu da Mtsala Dashi..Kawaye kuma Imu imu ne daga ke sai Nasara sai ni sai Tasleen kanwar Anty Safiya Bana jin Intee nada wasu kawaye..!
Hafsah tace”Shikenan ma hakan yayi wai yanzu yaushe Date din Bikin..?Naji ya Sa”id na cema Anty Faree Daada tace wannan na Hannunsu Baffa kuma yace sun yi mgana da Sadam yace Baffa Mustapha yace Date din Biki Sai ya Imu ya Saka Rana da kansa Tunda shine mai gayya da aiki..!
Munari tayi Sakai sakai kafin Tace”Topha ya Imu muke jira kenan..? Dankari..!
Hafsah tace”Nima abunda nace kenan..Ita ai maatarsa in mu muna jin tsoro ita Ta tambayan mana shi mana Muna so muji Lokacin ne yadda zamu Tsara abubuwanmu..!
Da wannan Shawaran suka Rabu Tsakanin Munari da Hafsah.
Inteesar Tayi bakan tana jinsu batace komai ba..
Munari ta Zungureta Tana Fadin”Nasan kina jina da Hafsah ko..?
Mganar Tarewarki ce..Ance fa su Daddy sunce mganar Sanin Hakikanin Date na wajen Ya Imu..!
Yamutsa Fuska Inteesar Tayi kafin Tace”Sai akayi yaya..!
Munari ta Kalleta Cikin mamaki kafin Tace”Kamar ya..?Tambayo mana shi Zakiyi yaushe ne ya Tsaida Lokaci saboda Shirye shirye.!
Inteesar ta Shagwabe Fuska Tana Fadin”Abunda ni ko kulani ma bayayi..Tunda aka Daura mana aure ko dan irin Text messages babu ballatana Kira..Nima kuwa na Sharesa bai nemeni ba nima ban nemesa ba Tun Ranar Monday da muka Hadu kofar gidansu Mama.!
Shakeke Munari ke kallonta kafin Tace”Au ke daman kina Jiran ya Nemeki ne…?
Kin manta Waye ya Imu..?Dankari na Rantse har ga Allah ko Tarewar kukayi ke za ki sha Wahala in har kina Tsammanin ya Sauke wannan Egon nashi ya Nemeki u are mad ma Wlh Ya Imu fa..Kai ai kina ma Cikin Masifarsa zai ce kin gama Rainasa Intee..!

Shakira..
3/25/22, 22:52 – Ummi Tandama😇: GMB2🅿ï¸?20

Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488

Inteesar ta kalli Munari cikin wani yanayi tace”Na shiga uku Munari ya Zan yi yanzu..?
Tafada tana kwalkwal da Idanuwa kamar Zatayi kuka Munari ta gyara Zama Tana Fadin”Ya kuwa..?kin fa san Halin ya Imu mijinki ba irin na kowa bane Inteesar..Kuna son junanku ammh Soyayyar tana Wahalar daku baku Sani ba..!
Inteesar ta Harareta Kafin tace”Ya akayi kikasan muna son juna..?in ni na yarda Yes ina son ya imu shifa kinga alamun Sona a tare dashi..?
Tafada Cikin bayyana Damuwarta.
Munari ta Dan yi mirmishi kafin tace”Wlh Ya Imu yana sonki..So mai Zafin da bai isa ya iya Guje miki ba..soyayyar Data shigesa batare Daya sani ba,Kema kuma kina sonsa soyayya mai Zurfin da baki san yaushe ta Fara ba Intee..!
Inteesar ta kalleta kafin tace”Duk ya akayi kika san haka..?ke da ba Soyayyah kike yi ba..?
Munari tace”Ni ina son soyayya ina son naga Masoya suna Kwasan Soyayya Raba Raba na Dade da Fahintar ku keda Ya Imu kyaleki kawai nayi Naga gudun Ruwanki,Sai kuma gashi komai ya zo karshe kun zama Miji da mata to ai zama bai ganki ba yarinya ba yanzu bane zaki kwanta kice zaki ja ajin nan ba Sai mun kamasa a Hannu in Tafiya tayi tafiya sai muja Zaran mu son ranmu yadda Zai zo ya fara ban baki da Lallashinmu batare da ya sani ba..!
Inteesar ta Sauke ajiyar zuciya kafin tace”Munari Wlh ni kaina sai Daga baya na Fahimci na kamu da Son Yaya Imu ban Fahimci haka ba sai da aka Daura mai aure da Sajida kamar na Mutu haka naji alokacin..Ammh ni yanzu Damuwata Daya ne Shin ya karbi Aurena saboda yana sona ko Saboda ba yadda zai yi ne kamar na Sajida..?
Munari tace”Saboda soyayyar dayake miki yasa ya aureki ba komai ba..Wlh Ya Imu yana sonki zaki ce na Fada miki Inteesar..!
Inteesar tace”In hakane meyasa bai Taba Fadamin ba..?bai taba nunamin alama ba..?
Munari tayi karamin Tsaki Tana Fadin”Shi Ya Imun ne zai Fada miki Yana sonki a wannan gabar ko..?U are not Serious Ai shi kanshi yana karyata kansa ne bai gama yarda yana sonki ba kece zaki sakasa ya Furta alokacin da bai sani ba..!
Inteesar Tayi shiru kafin tace”Ta yaya..?ta wacce Hanya zan bi hakan ta Faru..?
Munari ta Rike mata Hannu Tana Fadin”Ai kin Riga kin kama Zuciyarsa..Ya Imu bai taba bama Wata Mace dama a Rayuwarsa kamar yadda ya baki ba..Kin ga kenan kina da Babban Mtsayin da ba kowa ke dashi ba..yanzu gyarawa zaki yi ki Sani Ya Imu ya TSani Raini shiyasa bazai Taba Nemanki ba yana ganin in yayi Haka Zaki Rainasa,Ammh ke in kika Rika Nemansa ya zaki saka ya Fahinci kina basa Girmansa a mtsayinshi na Mijinki ko bai kiraki ba ki kirashi dan Text din ba Fasawa Zaki yi ba ki cigaba da yayi a wannan gabar Lokacin sa ne Ki bari namu Lokacin na gaba..Lokacin da zaki ja ajinki son Ranki kuma Dole ya Biyoki ya Lallasheki Saboda ya riga ya Fada Komarki Alokacin bazai iya Karyata Kansa ba bazai iya karyata Soyayyar Da yake Miki ba..!
Inteesar ta gyada kafin tace”Yanzu me zan yi..?
Munari ta gyara Zama kafin tace”Kiransa Zaki yi kice kin Kirashi ne ki gaishesa da aiki..In mun Tashi Daga School mu wuce gidanmu ki Dagaci dawowarsa Daya shiga Daki ki Dauki Ruwa ki bisa dashi In kika kai mai ke Macece kinsan yadda Zaki yi ki Tambayesa Yaushe yake ganin Za”ayi Bikin Tarewarku muji mai Zai ce..!
Inteeesar ta jinjina kafin Tace”Allah yasa kada ya gwasale ni..!
Munari tace”Dillah ke ce fa..?wlh baya gwasaleki..!
Inteesar batayi mgana ba ta Fiddo da Wayarta acikin jaka ta lalubo Lambar Imran ta Kirasa wajen Kira Biyu tayimai bai Dauka ba ana uku sai ya Latsa mata Busy ta Dago kamar Tayi kuka Tana kallon Munari tace”Ya fa kashemin Kira..!
Munari tace”Kara kira me nema ai yana tare da Hakuri..!
Batayi musu ba ta kara Kira wannan karom bata Dade Tana Ringing ba ya Daga cikin Kaushin Muryansa na Koyaushe ya katseta Daga Sallaman Datake yi mai yana Fadin”Tunda kika ga kina ta Kira ban daga ba meyasa bazaki Fahimci ina aiki bane Inteesar….!!!!
Yadda yaja sunansa sai da Jikinta ya amsa wani yarr Lumshe ido tayi kafin ta Bude,Munari na gefenta tanajin komai Duk da ba a amsa kuwwa aka Saka wayar ba Tanajin abunda yake Fadi Tunda suna Zaune ne kafada da kafada
Zungurin Inteesar tayi ganin tayi Shuru Ta kasa mgana Sai ta Kalleta sai ta Fara mata alamun tayi mgana da idonta ganin tayi Shuru yasa yace”Kin Tsaidani ina aiki kuma kin yi shuru..?meyasa kika kirani..?any problem..?
Da Sauri Inteesar Tace”Am..Ba..Bakomai..Daman na Kiraka na gaisheka ne ya aiki..?
Yana Daga zaune saman kujeran sa Hannunsa Daya saman Laptop din Dake gabansa Dayan ne ya Sagala Wayar a kunnensa kafin yace”Kin kirani ne ki gaisheni..?yaushe kika Fara Kirana ki gaisheni..,?
Bai bata Zarafin mgana ba ya Cigaba da Fadin”Bakisan inda nake kwana bane..?Yarinyar nan Tsabar kin Rainani ma ni kike gani kina Guduwa kamar kin ga wani Sakarai ko..?na Kyaleki ne naga iya inda Zaki Tsaya ni ba Shashasha bane da zan saki aikin gabana na koma ina Lalacewa wajen Lallashin ki me akayi miki..?ko auran ne baki so..?
Inteesar da idonta ya Fara cika da kwallah Tace”Yi hakuri.!
Da sauri yace”No ba zencen yi Hakuri bane ko baki son auran ne kin fi so a warware kije ki auri wanchan Yaron..?
Inteesar da Sauri Tace”Ban ce ba..!
Tafada Tana Tura baki Sanyi yaji acikin Ransa kafin yace”To meyasa da kika gani kika gudu kina kuka..?na Dake ki ne..?kada fa ki manta ko ba Mtsayin Girman Miji ba ni yayanki ne so kinga ina da Girma Biyu a wajenki ammh na Lura baki kiyaye ko Daya ina Mijinki ammh Sai ki tashi ki Kwana ki Wunu baki neme ni ba irin U don”t care din ko..?
Uhm ai yayi miki kyau zan kula Dakai na bana Bukatar komai Daga Wajenki sai dai bazan yarda ki Taremin agida da nayi mgana ki Faramin kuka ba..!
Yafada kai Tsaye cikin kokarin Fadin Abunda ya Dade yana Damunsa acikin Rai.
Kasa mgana Tayi jin tayi Shuru yasa yace”Is ok..ina aiki ne we tok later..Ko kuma in na dawo..!
Da Sauri Tace”Am sorry..!
Kansa ya shafa yana jin bacin Ransa na Sakinsa yace”Ya zan yi Dake..?ai dole na Hakura kada nace ban hakura ba ki Fara kuka Har sai Daddy daga Kaduna yaji Labari Tunda an Hadani da Shagwabbiyar kamarki ai an Hadani da aiki ni kuma gashi ban iya Lallashi ba ban da Taushi ko kadan Kananun kuka suna batamin rai Wani Lokacin ya za”ayi kenan..,?
Dariya tayi batayi mgana Munari na gefe tana jinsu tana kallon Inteesar Wato Love kenan mai saka ko Sarki ne ya Rusuna.
Jin Tana Dariya yasa yace”Au dariya ma na baki..?zaki yi bayani ne in muka Hadu..Later..!
Yana Shirin katsewar wayarsa Munari na mata Rada tana Fadin”Banza kice i Miss u Allah ya dawo min dakai Lafiya Mijina..!
Inteesar ta kalleta tana Kyafta ido Munari ta kara Fada tana wani kare Bakinta kada yaji batasan shi Tuni yaji ba har zai kashe Wayar yaji ana mgana Kasa kasa kunnensa kamar na Maciji yake yana da karfin ji sosai shiyasa ya Dakata mamaki ya kamasa Wato ma mara kunyar yarinyar nan Tana kusa kenan..? Ai shi fa ya gama Shiga Ciki Tunda ya auri Irin su Munari ammh Dole ya Tsare Giransa ya Tauna Tsakuwa Domin aya taji Tsoro.
Bai yi mgana ba sai da Inteesar tace”Hello Ya Imu kana jina..?
Idonsa ya Lumshe kamar Tana ganinsa yace”Uhmm..!
Sai da ta Runtse ido kafin tace”Allah ya dawo min dakai gida Lafiya..And…!
Ta kasa fada ta Fara Raba ido Munari na Zungurinta cikin Danne yanayinsa yace”And What..?Umh..!?
Da sauri tace”I miss u…!
Da sauri ta Datse kiran Tana Fadin”Ina jin kunya Munari..Ya Imu ne fa..!
Munari tace”dillah sai me shi ba Namji bane..?ana koya miki yadda Zaki kamsa a Hannu kina wani Shirme ke kika sani Wlh ya ta baki Wahala..!
Inteesar na shirin mgana wayarta ta Dauki kara Tana Dubawa ta Zaro ido Tana Fadin”Munari na Higesu Ya Imu ne ya Sake kira..!
Munari tace”Shine me..?ki Dake ki Dauka kefa yanzu Matarsa ce kina da Damamarki da yawa ba kamar irin mu bace..!
Jin haka yasa Hannunta na rawa Tana Dauka kafin tayi mgana yace”Saka wayar a amsa kuwa..!
Cikin Zaro ido tace”Eh me kace..?
Dakuna Fuska yayi kafin yace”Abunda kikaji a Farko..!
Dagowa tayi tana kallon Munari itama Tana kallonsta kafin ta Sauke Wayar a Kunnenta ta sakata a amsa kuwwa.
Cikin Nauyin baki tace”Na saka..!
Gyara zama yayi yana Fadin”Sannu da aiki Jullet Uwar soyayya..?har ke ce kika tsara ace min i miss u ko..?Mara kunya yaushe kike..?da har kikasan ana kiran I miss u..?daman ba Karatu kike Tsayawa yi ba abunda kike koya kenan ko..?
Munari ta kwaso Rantsuwa ya Dakatar da ita yana Fadin”Stop..Stupit ni sa”anki da zaki rika karanta mata abunda Zata ce min don Kaniyarki..?Jikin ki na kaikayi ko..? tsaya Tsaya ma waya baki Izinin miji da mata suna mgana ki shiga Tsakiya..?ke Matar aure ce ko uwar mata…?
Munari da bata rai kafin tace”A”a..!
Cigaba yayi da Fadin”Oh ko ni kuka maida abokin Wasanku..?
wlh as from to Day in muna Mgana ki rika Tsshi Daga wajen ko Tarinki na kara ji sai na Tattaki kina so ki koyi Rashin kunya ko..?sai ki bari in kin kawo wanda kike so muka aurar Dake sai ki koyi gayamai U miss u..Bush gril kawai kuma ki bari mu Hadu Dake ki gani sai nayi kwallo Dake..!
Bai jira cewarsu ba ya Datse kiran yana Jin Aransa na baci Inteesar din ce ta Rainasa ba wata ba itama zai koma Gidan sai ta Raina kanta.
Munari kamar tay kuka Take Fadin”Daga Taimako..?ai shikenan..!
Inteesar mai Zatayi banda Dariya Munari na Kallonta batace komai ba Ta sha kunu ta Dauki Lemonta ta Suri Jakarta ta wuce Inteesar ta Rakata da Dariya Lalle ne ma Ya Imu Wato munarin ce nawa take..?
Bata san I miss u ba..Ita kadai in Ta Tuna Sai tayi Dariya sai da tagama shan Lemunta kana ta tashi tatafi Neman Munari Cikin Ajin Da suke Lecture ta ganta Tana karatu Tana ganunta ta Hade Rai Inteeaar na Danne Dariyanta ta isa kusa da ita Zauna ta Fara bata Hakuri Dakyar Munari ta Hakura ammh ta Dauki alkwarin bazata Taba yarda su hadu ba Ballatana Har yayi kwallo Da ita.
Sai 6pm Suka Tashi Daga makaranta Direct Gidan su Munari suka Wuce,Sun iske Abba baya nan sun Fita gari shida Yusuf a Sabuwar Motar Abba din Anty Safiya ce agidan ita kadai agajiye suke abinci sukaji Sukayi wanka Lokaci Daya da Dauro alwala Tunda an Kira Sallar mangariba.
Shashen Anty Safiya sukaje suna Hira Cikinta Har ya Fito sosai yana cikin Watansa na shida Suna nan har aka Kira Sallar Isha”i suka tashi sukayi Sallar sai lokacin sukaji Dawowar su Abba Falo suka Fita suka gaishesu ya amsa yana Tambayansu makaranta Suka ce Alhamdulillah.
Nan falo suka Zauna Tunda Ya yusuf ya Dawo yana Tare da Anty Safiya Abba kuma ya shiga Ciki.
Inteesar ta kalli Munari Lokaci Daya Tana kallon Kofar Dakin Imran tace”Ya imu ya dawo kuwa..?
Munari na Dannar wayarta tace”Ki Dubasa mana..!
Tafada cikin gatsali Inteesar Sai da tayi Dariya tashi tayi ta Leke Haraban Gidan Taga Motarsa ta Dawo Tana cema Munari”Ya dawo fa ga Motar sa chan..!
Munari bata ma kara kallonta ba Inteesar ta koma Ta Zauna kenan Imran ya shigo cikin Sallama karama iya Saman Lebensa.
Gabadayansu suka Dago suna kallonsa Munari sai da gabanta ya Fadi Da Sauri ta Mike tana gaisheshi ya amsa bai ko kalleta ba Inteesar ya kalla Wacce tayi Saurin Sadda kanta kasa bai ma Tsaya bi ta kan Munari Data Kwashi Sauri zuwa Dakinta ba Hannunsa Cikin Jallabiyansa ya Tura Kofar Dakinsa ya shige.
Inteesar ta Sauke ajiyar Zuciya tshi tayi ta shiga Kitchen ta Dauko Ruwa mai Sanyi da Nutri milk ta Dora saman wani Tire da Karamin Kofin glass guda Daya sai da ta tabbatar Abba bai fito ba kana Tayi Sadaf Sadaf ta Kwankwansa Dakin Imu yana jinta jikinsa ya bashi itace shiyasa yace mata ta Shigo.
Shigowa Tayi Lokaci Daya da Sallama,Ya amsa mata iya saman Lebe yana Zaune gefen gado yana Duba Wayarsa Kiran Khalil ya gani kila Lokacin Daya tafi masallaci ne ya bar Wayar agida.
Daburcewa Tayi ganin yadda ya Dauke kansa Kamar bai san da Wanzuwarta acikin Dakin ba ganin ta Tsaya mai kikam a saman kansa yasa ya Dago yana kallonta Cikin Dan Hade Rai yace”In bazaki ajiye ba ki koma Dashi mana..!
Yafada Kai Tsaye yana kallonta Da Sauri ta ijiye nan saman Drower din gadon,Ta koma gefe Tana Fadin”Ruwa na kawo maka sannu da zuwa..!
Yana kallonta baya so ya gwasaleta Yasa yace”Is ok..Nagode..!
Da haka ya mike Laptop dinsa ya Dauko Cikin Briefcase dinsa ya Dawo ganinta nan Tsaye tana waasa da Zoben hannunta Daga sama har kasa Tana Sanye cikin Riga da Sikat na wani leshi kayan sun mata Das ajiki gabadaya Sturcute dinta ya bayyana Saurin Dauke kansa yayi jin yanayinsa na Sauyawa,Karamin kugunta yake kallo ta gefen ido kan gadon ya zauna yana Bude Laptop din gabansa Lokaci Daya yana Fadin”Kina Bukatar wani abu ne..?
Yafada yana kokarin Daidaita kansa Cikin Shagwaba ta Dago Tana Fadin”Bakai bane kana ta Fushi Dani ba..!
Waro ido yayi yana kallonta kafin yace”Ni..?yaushe..nace ina Fushi Dake ai kin bani hakuri kuma na Hakura..me kuma nayi Ni Imrana bawan Allah Sarkin Laifi..!
Yafada yana Tattara Duka Hankalinsa akanta Cikin Sha”awar kallonta.
Lamgwabe kai Tayi tana Fadin”To naga sai Fushi kake dani kaki Sakin Fuskarka..!
Kai ya gyada kafin ya Mike Lokaci Daya yana Ture Laptop din gabansa yace”kinsan yanayina..Ni bakimin komai ba..!
Sake Bata Fuska tayi Zatayi mgana yayi Saurin cewa”Kada kimin kuka..Plz am not in d mood..Kuma ni ban iya Lallashi ba sai duka..!
Baki ta Tura kafin tace”Yanzu sai ka Dakeni..!?
Gira ya Dagamata yana Fadin”Yes of course kina ganin bazan iya bane..!
Zaneki Zan yi Tsab yadda baki da wani kiba nan..!
Yafada yana yar Dariya Lokaci Daya yana kallonta kasa kasa.
Cikin Tura baki tace”Laala..Matar taka Zaka Daka..?
Tafada Tana kallonsa ido na cikin ido,irin yadda yake kallonta yasa tayi Saurin Sadda kanta kasa Imran ya Dage giransa yana Fadin”Really..?Hakane fa ke Matatace!
Yafada yana shafa Sajensa kafin yace”Zo…!
Da sauri ta Dago Tana kallonsa kafin tace”Ni..?
Daure Fuska yayi kafin yace”A”a Ni..!
Yafada yana kauda kansa jin haka yasa ta Fara takawa zuwa gabansa Kanta na kasa sai da taji Tana jin Hucin Numfashinss kana ta Tsaya Tana Fadin”Gani..!
Yana kokarin Daidaita kansa yace”Ai na ganki..!
Yafada yana kallon kirjinta da suke mai Maraba,jikinsa ya Fara Shaking bai san yaushe ne ba kawai ya jisa ya Saka Hanmu ya jawota jikinsa ya Rumgumeta kamkam kamar wani zai Kwace masa ita atare suka saki ajiyar Zuciya Cikin Salama Inteesar kara gyara Kwanciya tayi a Faffadan Kirjin Imu Tana shakan kamshin Turaransa mai Dadi da Tafiya da zuciya Har Lumshe ido take yi shima kansa ya Dora Saman kanta Lokaci Daya yana Zagaye bayanta da Faffadan Hannunsa Jinsa yake kamar yana yawo a gajimare saboda Farinciki da Salama.
Dankwalin kanta ya Sabule ya Fadi kasa,Inteesar ta kara Rikesa sosai Ta saka Hannunta ta Zagaye kugunsa cikin yanayin da batasan ma Tayi ba Wani irin yarr Imran yaji wanda yasaa ya Tusa kansa cikin Kitson galaban Dake kan Inteesar Neman rasa Control dinsa yake yi yasa Cikin Wata Murya yace”Waya miki wannan kitson..?
Inteesar Dataji kamar tayi ta barci Har Abada a jikin Imran tace cikin Wata irin murya”Munari ce..!
Hannunsa Daya yasa yana shafa kan nata gabadaya sai inteesar taji Tsigar Jikinta na tashi Wuyanta ya Shafo Takara Rikesa da karfi jin wani Zirr acikin jikinta Lokaci Daya Tana Fadin”Washh..!!!
Tafada cikin wata kasallaciyar muryan da bata san tana dashi ba Wannan Muryan datayi amfani da Rikon Datayimai yasa gabadaya yaji yana neman rasa Controlling dinsa yasa yayi Saurin Sakinta ya koma ya Zauna gefen gado da sauri Saboda kada taga Girmansa yadda ta Mike Tsaye Sambal ta bayyana kanta.
Kansa ya Dafe ya kasa ma Dagowa saboda yana so yayi kokuwa da yanayin Dayake ciki.
Inteesar sai Lokacin taji kunya ya kamata tayi Saurin Daukan Dankwalinta ta Daura Ta juya Cikin Rawan jiki dana Kafa Zata bar Dakin taji yace”Baki fadamin abunda yasa kika shigomin daki ba..?
Yafada cikin Sanyin muryan Datake cike da sha”awa.
Cak ta Tsaya bata waigo ba tace”Dama..Dama.!
“Dama me.?Malama ki juyo kimin mgana ni yaro ne da zaki juyamin baya kina min mgana..!
Bata da yadda Zatayi gabanta na Duka ta Juyo Bata yadda ta Kallesa ba shi kuma Duka Shanyayyun idanuwansa ya Zuba mata.
Cikin Dakewa tace”Dama na Tambayeka yaushe ne Ka Tsaida Bikin Tarewar mu..?
Kallonta yake cikin mamaki kafin yace”Kin kosa ne..?
Da Sauri ta Dago kamar tayi kuka Tace”Wlh A,a..Su munari ne suka mtsa suna so suji saboda Shirye shiryen fa..Ni yaushe nace na kosa..!
Tafada Tana Tura baki.
Kansa ya shafa yana Fadin”Yaran nan sun cika azarbabi..To da suke Tambaya Kayan Daki zasu hada miki ko su zasu min akwatin auran ne da suke Tambaya..?
Inteesar ta marairaice Tace”Sufa Saboda Events din da zasu shirya ne..!
Kasan kuma hakan na Bukatar Tsare Tsare..!
Imran ya Hade Fuska yana Fadin”Event..? A bikin waye zasu yi Event din..?
Yafada yana wani Kara Dakuna Fuska.
Inteesar tayi narai narai kafin tace”Bikin Tarewar fa..!
Tabe baki yayi yana Fadin”an gama mai wuyar Tunda aka Daura auran..Ba wani shanshanci kuma dazai biyo baya in nagama Shirina ni da kaina zan Daukeki mu tafi bana son Hayaniya da wata mgana Ok..!
Inteesar ai mamaki ya Kasheta bata samu Damar mgana ba ya cigaba da Fadin”Kuma ma Wa yace a zo a Tambayeni..?meyasa baku kira Daada ko su Daddy ko Abba ba..Kun Rainani ko..?ke kuma mara wayau kece yar aike ko..?da sun sani sun Tare ni da kansu..!
Inteesar tace”Ai Daddy ne yace kai zaka Tsaida Date din
Imran na Dariya yace”Nagodema Daddy..Ki Fada musu nan da Next year lokacin nima na Tara kudi sosai Kema kinga Lokacin kin Shirya tunda ai yanzu kin ce baki kosa ba..?
Inteesar takallesa Kafin ta kauda kai Lokaci Daya Tana Tura Baki yana Danne Dariyansa yace”Eyye ni kike Tura ma baki..?
Ai bata ma bari ya kara mgana ba ta Fice da Sauri ya Rakata da Dariya aransa yana Fadin”Yaran fa basu da Hankali so suke su min bidia a bikina…Ashe kuwa zan karya yarinya..!
Daki ta koma ta iske Munari na Charting nan ta zauna ta Fadamata Abunda Ya Imu yace Munari tace”Bari zan kira Ya Sagir muyi mgana..yasin Bazamu yardaba sai munyi Bidian da baya so..In yaki ma Daada zamu hadasa ko da su Abba..!
Inteesar tace”Gaskiya..Shifa yarda yake so dagani sai shi ba biki ba komai fa..Kamar wata mara Galihu..!
Munari tace”Bafa zai sabu ba yadda mukaci Burin bikin nan sai fa an sha Hidima iya Hidima Amaryan Oga Imu..!
Dariya suka saka gabadayansu kafin su cigaba da Hiransu sama sama.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button