GIDANMU COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

GIDANMU 1&2 COMPLETE HAUSA NOVEL

GIDANMU COMPLETE HAUSA NOVEL

Washegari kamar yadda Inteesar Ta bukata Bayan Munari ta Shirya Gidansu Sagir ta Fara Biyawa Inda Allah ya Taimaketa Imran yana Gida bai Fito ba koda tazo Inteesar ta Shirya ita take jira basu Bata Lokaci ba Sukayi ma Mama sallama Suka Fito Ta bisu da addu”an Allah ya Tsare,Suna Fitowa suka Tsaya Bakin Shagon Sagir ya Fito suka gaisa Shi Kanshi ya godema Allah Imran baizo ba Kila da anyi wani karamin Shirin Film,500h ya basu suka ki karba yace sai dai in sin Raina Shiyasa Munari ta Karba Daganan basu Samu Abun Hawa ba sai da suka Taka da Kafarsu suna Hira Har bakin Titi kana suka Samu suka Hau zuwa Cikin makaranta,Koda sukaje ana Ta Shiga ajin Dole suka bi ayarin yan ajinsu suka Shige suma Domin yin Abunda ya kawosu.
Ranar ma Tare suka wuni,Basu Je Cafteria ba sai da sunje Shago sun Siya Lemo Inteesar tazo musu da Biskit da,Donut sukaci suka Koshi Suka Tsinke da Hira Ranar Munari ta Sha Labarin Daddy da Umma da ya Basheer Har gaisawa sukayi da Daddy Daya kira yaji Inteesar Cikin Fara”a yake Tambayanta tace Besty ta samu Tabana Munari suka gaisa yana ta Saka mata albarka Munari Taji muryan Daddyn Intee kamar na Abbanta Sai dai bata yima Inteesar din mgana ba Shi kuwa Daddy Daga Barayin Yasan Munari ta Musamman ne Tunda Har Daga Haduwa Suka Kulle da Juna yana Fatan Allah yasa kawancensu ya Zama alheri ga juna.
Ranar 4pm suka Tashi Daga makaranta Daganan gida suka Taho,Munari bata Sauka Daga gidan su Sagir ba,Saboda Tana Tsoron Haduwa da Imran illah kamar ta Sani yana Cikin Shagon Sagir,suka Rabu bayan Inteesar ta Karbi Wasu Note Hannun Munari Zata kwafe Tunda Gobe suna Gida bazasu Shiga makarantar ba.
Lokacin Data Sauka Imran da Sagir na Fuskantar Kofar Shagon Sagir kadai ya ganta Shima bai Dade da Dawowa Daga cikim makarantar ba,kanta na kasa ne Tunda Shago ne na Dinki akwai Dandalin Maza awajen Har ta Wuce batama Dago Kanta ba,Imran kansa na gefe yana kallon Wani Atamfa da yaron Sagir ke yankawa Shi bawai yana son koya bane No sai dai yana Kallom komai Dake Gudana a Shagon kuma yana Dauke sa acikin Kwakwalwarsa Batare da ya bama Abun Muhimmanci ba.


After 10Days..
Bayan kwana Goma da Haduwar Inteesar da Munari Sosai kawancensu Yayi nisa wanda yasa Kowa bai iya Boyema Daya Labarinsa,Har takai Abba da ya Yusuf da Safiya sun san Sunan Inteesar Besty Munari a bakinta Abba yaji Dadin jin Diyar kanwar Mama ce Mahaifiyar Sagir Hakama Ya yusuf,Shima bai Hanata ba jin na Gidane Tunda yanzu suna Kokarin Daidaita komai nasu ya Dawo kamar Baya ne.
Haka itama Inteesar din Daddy da Umma da Ya Basheer sun san da Zaman Munari Tunda In suka kira a makaranta indai suna Tare da Munari sai ta basu sun gaisa sun santa da Murya Sosai Harta da Nasara ma ta san Labarin Munari sun ma Taba gaisawa Watarana Datakira Inteesar din suna Tare da Munarin ta bata suka gaisa.
Inteesar ta Taba Zuwa Gidansu Munari sau Biyu bata Hadu da Ya Yusuf ba Imu kuma yana Dakinsa Shi a labarin ma bai sani ba Domin Munari bata yarda ta Furta Indai Labarin Zai kaimai ba.
Sai ta Hadu da Abba ita kanta Inteesar ganin Farko Datayi ma Abba sai da Tayi Shock Ta Dinga kallonsa Tana so Ta Tuna ina ta Taba ganinsa ta kasa Shekarun Dayawa Tana karama ne,Sannan kuma yanayin da Muryansa kamar ta Daddynta,Sai dai itama abun na Ranta bata iyama Furtama kowa ba,Sai ya Yusuf da suka Hadu Rana ta Biyu Data Dawo Shi kanshi Taso ta ganesa Domin da Girmanta Tataba Raka Daddynta Dukku suka Hadu dashi yazo Shida Marigayi Nura alokacin Sai dai kamaninsa ya bace mata Tunda ya Kara Girma aure yasa ya Zama wani Budede Sai kawai ta Watsar da Abun acikin Ranta ko Zencen batayi ma Munari ba.
Tana jin Dadin zuwa gidansu Munari Sabida Abba da Anty Safiya Suna da Matukar kirki Haka Abba zai ta janta da Hira yana musu Fadan su maida Hankali ga Karatu,ita kuma Anty Safiya ta jasu Shashenta suyi ta Hiransu,Ta maida kanta Sa”arsu Ranar ma da Inteesar din tazo Suna Shashen Anty Safiya sai gasu mommy sun zo ita da Anty Saratu da Tasleem Dama Tun jiya Mommy tace Safiya tasa Idonsu Dayake ta Dade ta Tura musu Kwatancen Gidan basu sha Wahalan gane Gidan ba Tunda ba yana Lungu bane.
A falo suka Fara ganin Abba yana Zaune yana kallo Suka Gaisa Dashi,Kafin Safiya ta Fito ganinsu Mommy yasa ta Murna ta Rumgumesu Cikin Farimciki nan take Fadama Abba Mamartace da yayarta da kanwarta suma ta gabatar musu da Uban Mijinta Suka kara gaisawa Sosai Abba ke ta Godiya sai da Mommy da Anty Sarati suka ji wani iri.
Sun zo Da kaya sosai a manya Ledoji Safiya tajasu Zuwa Shashenta sun ga abun mamaki kayan arziki haka,Ba ko sisinsu,Nan inteesar da Munari suka gaishesu Tasleem ma suka gaisa da Munari ta gabatar mata da Inteesar,Nan suka barsu suka Koma Dakin Munari suka Cigaba da Hiransu Daga Baya nan Tasleem din ta Dawo suka Hade su uku suna Shan Hira Tasleem na Fadin itama Buk Zata Cike Taje chan su Hade tare.
Safiya kuwa Ta Dinga ina zata saka da Iyayenta,Daman ta yi girki Dazu ita da Munari,Farar Shinkafa Miyar Kaza Sai Kunun aya da sukayi shi ta Zubo musu sukaci suka saka albarka suka Leka ko”ina suna yabawa Anty Saratu ta Kada baki tace”Ni kam ai banga aibun da Alhassan ke Fada akan wannan Gidan ba..Ga Baban Mijinta Dattijon yasan Karamci ji yadda yake mana Godiya mu da muka kawo musu ya ba komai ….Ji Abun arziki Mero..Ji Safiya tayi kiba kamar ba ita ba ai wannan gida..Tabbas Gidan Aure ne Wlh..Allah ya Zaunar Lariya..!
Hajiya Mero Tana ta Dariyan Farnciki,Sun zo mata da kayan Kitchen,da Turarun ka Daki Dana Jiki sai Speciess na girki da Garin kunu da Zogale Bushashiya,da su Kubewa,kuka Da Sauran abubuwa sai Kayan gyara,Da kayan gara irin su Mangyada da manja da Kwalayen Indome da Taliya da Macaroni suka Gyara Kitchen din suka Jera komai gwanin Sha”awa Basu Tafi ba sai yamma da Yusuf ya Dawo suka gaisa,Lokacin Inteesar tatafi Gida Tasleem da Munari suka Rakata Gida suka Dawo suna Dawowa Suka Tafi su kansu suna ta yima Yusuf Godiya Shi kuwa aransa yana Fadin ai Shi ke da Godiya Safiya ai Kamar Zinare ce a wajensa Bayan sun Tafi ta Nunamai kayan da suka kawo mata ya gani ya saka albarka har Abba ta Fadamawa Shi ma ya saka albarka
Sun Tafi sun barta Cikin Farinciki Suma sun koma Cikin Farinciki suna Yabon Irin Gidan da Safiya tayi aure aciki.

*Shakira.. *
3/22/22, 23:05 – Ummi Tandama😇: GIDAN MU..!
(Our House)
Book 1

Wattpad:Jamilaumar351
Mallakar:Janafty❤️

            🅿�18

  Yau din Takama Ranar Sati ne Wato Asabar ce Tun Safe Inteesar tatashi da ayyuka,Da wankin kananun Kayanta ta Fara Iners dinta da bata ba dasu Wanki,Daman Tun tana gida ta iya kowani aiki banda wankin kaya sai Dai tana wanke Inners Dinta Sauran kayanta kuma Wanki a ke kai musu Nataa da na Umma sai dai a dawo Dasu a goge tas dasu.
Hakama Datazo Gidan Mama Tana Kowani aiki in Tana Gida banda Wanki,Itama Maman bada kanta Take Wankin nata ba kaiwa akeyi Sai da Inteesar din tazo ake Hadawa da kayanta Sagir ke kai musu Suma sai dai adawo dashi agoge.
Tana yin girki Duk Ranar Datake Gida kamar asabar da Lahadi,In bata nan Tana makaranta sai Mama tayi.
Yau ma hakan ce ta Faru bayan ta gama Wankin Kayan nata ta Share Daki ta gyara tayi mopping ta kuma Wanke Bayin Daki Da kuma na Waje ta Share Tsakar gidan ko”ina Tayi Tsaf, Da Mama tace ta bar Girkin ta Dora sai tace Maman ta barshi Ita Zatayi Shinkafa da Miya da wake ta Dafa musu,Da Salat Bayan ta gama tayi wankanta ta Saka Wata Doguwar Rigar atamfarta Gold mai kalan ja da Brown Anty Hauwa Matar Ya Basheer ta Dinkamata shi,Ta kashe Daurinta na Zara Buhari Fuakarta Tayi kyau Sosai Duk ita ba ma”abociya Kwalliya bace.
Sallaya ta Shimfida ta Tada Sallar Azahar Daman Daga Tiolet ta Dauro alwala,Bayan ta Idar da Sallar ne taje Kitchen ta Dibo ma Mama Abinci Ta kawomata Zobon da Tayi Jiya da Daddare Bata Taba gwadawa ba Ko tana gida sai dai Tana ganin Talatuwa mai aikin Umma nayi Shine jiya Dataga Mama nada kayan Hadin Zobon Tace bari ta gwada sai gashi kuma Yayi Dadi,ammh Sai da Munari Tazo ta Taimakamata.
Sannu da aiki Mama Tayi mata Tana Daga kan Darduma bayan ta Idar da Sallah Tana Lazimi.
Inteesar ta amsa mata Cikin Jin Dadi Domin Tana bala”in jin dadin Zama da Mama Tana ganinta kamar Umma abaya ta Zata tafi Kowa Kewar Gida sai gashi Tana jin Dadin Zaman Gidan Mama,Sai dai kewa ta iyaye kuma gashi Suna mgana ta waya Kusan kullun sai sunyi Waya Daddy Fiye da Sau Uku Rana Umma ce ma sai Bayan an kwana Zata kirata taji ya Karatun ko Bata kirata ba Takan kira Maman su gaisa.
Ganin Zata Koma Cikin Uwar Dakin ne yasa Mama ta Daga baki Tana Fadin”Inteesar ina zaki kuma..? Ke banga kin Debo abincin Kinci ba kuma kin gama Dafa Abinci da kanki..!
Inteesar ta Juyo Tana Fadin”Mama ba yanzu Zanci ba sai anjuma..Dambun Namam da naci da Safe ya Cikamin Ciki..!
Mama tace”Ina Dai Lura Dake baki san cin abinci sai kayan kwalama da Shan Zaki Shiyasa gaki nan Har yau bakya Kiba..!
Dariya Inteesar Tayi kafin Tace”Kai Mama Allah ina ci..Rashin kibata kuma wlh ina jin Dadin kaina ahaka Sam bana son kiba..!
Mama tace”ai shikenan nayi Shuru..!
Yar Dariya Inteesar Tayi kafin Tace”Mama zan Dan kwanta In ya Sagir ya Shigo Abincinsa na Kitchen..!.da kai Mama ta amsa mata Tana cigaba da Laziminta ita kuma Inteesar ta Juya ta koma Ciki kan gadon Datake kwana ta yada kanta Lokaci Daya Ta Dauki Wayarta Ta kira Munari har Sau Biyu bata Dauka ba Lokaci ta Duba taga Har 1:30pm Tayi,Sai tayi mamaki Rashin Zuwan Munari alhalin sun Rabu ajiyan kan cewa yau Zata zo da Wuri suyi Karatu Tare suna Taimakon juna inda Daya bai gane ba in Daya ya gane sai ya Tada Dan”uwansa haka suke yi Duk Karshen Sati basa yarda su Zauna haka ko suce sai Test yazo ko Jarabawa Zasu Fara karatu a”a su Tuni suke Karatun Duka Course dinsu Saboda Karatun Shi suka sakama gaba ba Shirmen da wasu ke yi ba..
Har Barci ya kwasheta Munari bata Biyo Bayan kiran nata ba,Karfe 2:30pm ta Farka ta sake Duba Wayarta Ganin Ba Missedcall din Munari yasa ta Kara Kiranta Nan ma bata Daga sai Hankalinta ya tashi tasan ba Lafiya ko Bata kusa da wayar in tazo ta gani Zata kirata.
Saukowa Tayi Daga kan gado Tana gyara Daurinta Daya Warware gabam Madubin Dake Dakin ta Tsaya taga Fuskarta  ganin batayi komai ba yasa ta Bude Akwatinta ta Dauko Jan Mayafinta ta Yafa ajikinta Ta Nufi Wajen da tayi Domin Ma”ajiyar Takalmaanta,Ta Dauko wani Flat Shoe red Colour Shima ta Saka ta Dauki Wayarta ta Fito falo ta Samu Mama na Zaune ta gama cin Abinci Tana gyanyandi Cikin Dariya tace”Mama kina jin Barci basai ki Shiga Ciki ki kwanta ba..?
Kina ta gyangyadi a azaune kamar yadda Inno take yi..?
Mama ta Farka Cikin Muryan Barci Tace”Kaniyarki Innon Kike cewa Tana gyangyadi a zaune..!
Inteesar na Dariya tace”Kai Mama keda Umma bakwa so kuji an Taba Inno..mallam Babba yafi ku ji da wannan yar Tsohuwar matar tasa..!
Mama ta yunkura ta mike tana Fadin”Kinga Laifinsa..? Mutum da matarsa kuna sakamai ido..!
Inteesar Tace”Tsofai Tsofai dasu Mama..!
Mama ta harareta Tana Fadin”Bana son Shakiyanci Iyayen namu ne Tsofai Tsofai Ai Soyayya bata Tsufa sai dai Masoyan su Tsufa Ballatana Irin Soyayyarsu su na Mutan Da..!
Inteesar Dariya kadai ta saka Kafin Tayi mgana Mama ta Rigata da cewa”Ina Zaki kuma..? Ni ina nan Zaune bayan na gama cin Abinci gyangyadi ya kwasheni ban sani ba..Asama sama nake jin mganarki..!
Inteesar tace”ki shiga ki kwanta Mama ahakan ai sai Kanki ya Sage..!
Mama tace”To bari na dan Mike Saman kujeran nan..!
Inteesar tace”Yauwa ko kefa Mama..Bari in leka Munari Tace yau Zata zo muyi Karatu kuma najita Shuru,Na kirata bata Dauka ba.!
Mama na ZAma kan kujera Tace”Eh Leka Ki gani ko Lafiya..in Lafiya take ai da yanzu ta Shigo Gidan nan..!
Inteesar ta Duka Tana Kwashe Filet din da Mama taci Abinci ta Fice dasu Mama ta Bita da adawo Lafiya.
Sai da ta Biya Kitchen ta ijiye abun Hannunta Nan taga Sagir bai ma ci Abincin ba kenan bai Shigo ba Shima Ficewa Tayi Daga Gidan Cikin Takun na Natsuwa Zuwa Gidansu Munari.
Sun gaisa da Iro Megadi Kamar yaushe In tazo gidan kana ta Nufi Cikin Gidan Cikin Sanyinta Iska na kadata kamar Zata Fadi.
Sallama Tayi Daga Kofar Babban Falon Gidan nasu Munari Abba Dake Zaune Shiyajita sai ya Amsa mata Duk da bai san ko wacece ba.
Turo Kofar Tayi ta Shigo Lokaci Daya tana kara yin wata Sallamar.
Wannan karon Harda Safiya Da Yusuf a masu amsa mata Tana daga gefe Wajen Dining Tana goge goge Abba na Zaune Kan Daya Daga Cikim kujerun Falon Center Table na gabansa Dauke da Ruwa da karamin Kofin Tangaran,Sai karamin Qur”anin Dake Hannunsa,an Dauke wuta Shiyasa yau babu karan Tv.
Abba yana Sanye da Shadda mai Ruwan madara Riga da wando kansa ba Hula ammh Yana sanye da Farin glass dinsa.
Imran ne agefensa kansa da Idanuwansa na Duke ne yana kallon Zanen cafet din Dake Falo,sanye yake da Vest Fara Wacce ta kama jikinsa Sosai Har ta bayyana Karfinsa Domin gabadaya Muscles dinsa sun Bayyana sai Wando Baki 3Quaters,Tun Shigar Da yayi da Safe ce yaje jogging,Karan Sigari ce a Hannunsa Tana kunne Hayakinta na Fita sai sai ba Sha yake ba Gabadaya kansa na kasa ne ba wanda ma ya Fahimci wani Hali yake Ciki,Sai yusuf Dake gefen Imran din Sanye da Jallabiya mai Ruwan Madara.
Abba ne ke mai Fadan Shan Sigarin Dayake yi ganin,Tun Safe bai ci komai ba bayan ya Dawo Daga Jogging Dinsa suna Breakfast Safiya tayi mai Tayi yace ya koshi Da Rana Tayi Lonching ma bai ci ba ammh Yusuf ya Shiga Dakinsa ya Tarar sai Busa ma Cikinsa Hayaki yake yi Shine ya kawo kararsa Wajen Abba For d First Time ganin yanzu Abba Alhandulillahi ya Dawo Hayyacinsa.
Jikinta a sanyaye kanta na kasa ta kariso Falon Tunda taga da Mutane afalon,Gaban Abba ta Zube kanta na kasa Tana gaishesa ya juyo yana Kallonta Cikin Fara”a yace”Daugther Kin Tashi Lafiya..?
Inteesar ta amsa kanta na kasa Ta Gefen Idon ta Hango Yusuf Zaune da Sauri Tace”Ina yini ya Yusuf..? Ina Yini Anty Safiya? Tafada bayan ta Daga kanta sun Hada ido da Anty Safiyan Dake goge Saman Dining Din da wani karamin Towel.
Shima Cikin Sakin Fuska ya amsa mata da Cewa”Lafiya Lau Inteesar Hala kin ji kawar taki Shuri kika Biyo Sawunta ko..?
Kai ta gyada Lokaci Daya Hancinta na Shako mata Warin Sigari Tunda ta Shigo Yayi mata Maraba sai bata kawo hakan ba aranta tace bamai Shan Sigari agidansu Munari sai ta Lakanta hakan da Yadda bata son Warin Sigarin Shiyasa take jin kamar Tana Jin Warinta sai dai zuwa yanzu Data dan jima afalon ta Fara gasgatan Hancinta.
Safiya ce Dagachan Tace”Ai kawar taki yau Tatashi Batajin Dadi Shiyasa Baki ganta ba..Ki tashi ki SHiga Tana Cikin Dakinta..!
Da Sauri Inteesar ta Mike kamar Tana kan kaya Zuciyarta ce ta Fara Tashi Miyanta ya tsinke,Sai kawai ta Saka Gefen mayafinta ta Toshe Hancinta Daidai Lokacin Data kai Dubanta kan Inda Taga Hayakin Sigarin na Fita Zuwa Saman Fuskar ma mallakin Hannun Dake Rike da Sigari Bata ga  Fuskarsa sosai ba ammh ta Cika da Mamakin ganinsa Domin bata Taba ganinsa ba Sai dai tasan Munari na Fadamata Bayan Ya yusuf Tana da Wani yayan kuma yarda ta Lura Tana Matukar Tsoronsa.
Abba ne ya Lura da yadda take Toshe Hanci Cikin kulawa ya kalleta yana Fadin”Inteesar Lafiya kuwa..?
Da Sauri Inteesar tace”Abba..Warin Sigari bana so..Yana samin Tashin Zuciya da Amai..!
Adaidai Lokacin Dayaji Muryanta kamar Saukan aradu acikin kunnuwansa tun Shigowarta bai maida Hankali Wajenta ba Yana Fama da Dacin Ran Fadan da Abba kemai,Sai yanzu yaji mganarta Sai kuma ya gane Muryanta Da Sauri ya Dago Idanuwansa ya Sauke a nata Karaf wannan lokacin a karo na Biyu Suka kara Hada Idanuwansu Lokaci Daya kuma Zuciyoyinsu suka Kara Bugawa atare kamar wanchan Lokacin.
Imran kara Girman Idanuwansa yayi yana kallonta Tabbas itace ammh miye kawota Gidansu?
Mganar Abba ce ta katse mai Tunaninsa Inda yace”Yi Hakuri..Maza shige Wajen Munari..Yanzu nake mai Fadan yawan Shan Sigarin Dayake tana Illah ga Lafiya Ke gashi ma Warinta amai yake sakaki shi kuma Hayakin itace abincinsa..!
Kamar Abba ya Watsamai Gwarwashin Wuta haka yaji mganar Abba aransa ya ayyana Dama Marinsa Abba yayi wlh Daya fiyemai wannan Tozarcin gaban wannan Mara Mutumcin yarinyar nan za”a Tasashi ana mai Fada Lalle me ya Zama Dole yaci Ubanta Ko Zata gane Shi din ba”asanta bane,Duk da Abba ya riga yagama Sakawa yarinyar ta kara Rainasa Yana mata Fada agabanta.
Mikewa yayi a Fusace kamar wani Damisa Daidai Lokacin da Inteesar ta Fara Tafiya Zuwa Dakin Munari yace”Ke..!
Cikin Kakkausan Muryansa Cikin Tsawa da Bacin Rai Cak ta Tsaya Lokaci Daya ta Juyo Tana Kallonsa ai Ransa bai kara baci ba sai Da yaga yadda Take kara Toshe Hancinta da Mayafinta Sai yaji kamar yayi Tsalle ya gansa a gabanta yana Kwallo Da ita Har sai ya Rakata Waje da Duka.
Abba da Yusuf suka Saki baki suna Kallon Ikon Allah Safiya bata Wajen Tana Kitchen sai dai har chan Taji Tsawan Shiyasa ta Fito da Sauri.
Cikim Takunsa na Takama da Sassarfa ya Fara Taku zuwa gabanta yana Fadin”Ni sa”an wasan ki ne..? Ni Tsaran wasan ki ne kina kallona kina Toshemin Hanci..?
Ya Karishe Fada yana Nuna kansa Cikin Dakuna Fuska Inteesar kuma jada baya take yi acikin Ranta kuma Tana ayyana Lalle ne ma wannan Mutumin bai da Mutumci Dukanta Zai yi ko menene Nufinsa..!?
Fadi take Munari batayi Sa”an Yaya bane..Mara Mutumci Tsageri Kuma Dan iska Saboda Tsabar Tacewa Shi a gaban Abba ma Shaye Shayensa yake Baya ko Shakkar Boye Mummunan Laifinsa kamar yadda Sauran masu aikata Laifi irin nashi suke yi.
Yusuf ne ya Mike yana Fadin”Kai Imu Lafiyan ka kuwa..?
Abba kuma yana Zaune ne kawai yana Kallon Ikon Allah.
Inteesar Tana da Tsoro ammh kuma Bata bari a Takata ko Yayane Juya Manyan Idanuwanta tayi Lokaci Daya Tana Tura bakinta ta Cikin Mayafin Hannunta tace”To nifa bana son Warinta..Amai take sakani..!
Tafada Lokaci Daya tana kallon karan Sigari da Har Lokacin Take Rike Tsakanin yatsunsa manya Guda Biyu na hannunsa Cikin kwarewa Inteesar tace acikin Ranta”Jar uba..Lalle wannan ya kware a Harkan ji wani Rike Sigari..!
Bata gama Mganar Zucinta ba Taji yace”Ashe kuwa yau Zaki Aman kayan Hanjin ki..Maza ki Cire Abunda kika Sama Hancin ki..Zan gani yau ko Zaki mutu ne…!
Yafada Lokaci Daya kawai Ransa na kara kuna ganin yadda yarinya kamar Wannan da bai Wuce ya saka Hannu ya Damketa ya Murjeta ba itace Zata Tsaya yana Fada Tana Fada..? Kai bata isa ba Dole ya koyamata Hankali ayadda yake ji kamar yayi ta Dukanta Har ta suma Ta Daina Numfashi.
Kallon Anya kana da Hankali Inteesar Tayi mai kafin ta Nuna kanta Tana Fadin”Wai ni…!!?
Kai Imran yaji kamar Wuta ne acikim Zuciyarsa Saboda yadda ta Fara Tafasa Tuni Jiyoyinsa sun Tashi na Saman kansa Radau Tuni ya Fara Fitar da wani Huci Kirjinsa na Sama yana kasa.
Kamar kiftawar Wani abu sai gashi a gabanta so yayi ya saka kafa ya Tadiyeta ta Fadi sai ya fasa ya Daga Hannu zai kai mata wani Dukan da Kila sai tayi Sati acikin Coma bata Farfado ba,Inteesar Da Tsoro ya kamata ganin yanayinsa ta Falfala da Gudu Zuwa Bayan Safiya Cikin Alamun kukan Shagwabanta Tace”Wayyo Allah na..Abba ka gansa ko..?
Tafada Tana kara Boyewa Bayan Safiya Jikinta na Rawa ganin yadda ya Rikide ya Sauya Lokaci Daya
Ganin haka yasa Abba yace”Yusufa Rikomin shi kada ya Illata yar Mutane..!
Da Sauri Yusuf ya Mike ya Rikosa sai ya Fizge,Kallon Inteesar kawai yake da Rinannun Idanuwansa yana Tunanin Ko Kasheta ma zai yi ya Huta da Yadda yaji Zuciyarsa na Fitar da Wani Zafi.
Abba ne ganin haka ya Mike da kansa ya isa ga Imran ya Rikosa Da yaso ya Bangaje Yusuf din sai ga Abba sai ya Dakata yana Sakin Huci.
Sigarin Hannunsa Abba ya amsa ya Mikama Yusuf yana Fadin”Fita da ita..!
Amsa yayi ya Nufi Hanyar Fita da ita Shi kuma Abba ya Riko Hannunsa ya Zaunar dashi kan kujera yana Fadin”Imran wannan bakar Zuciyar taka ina Rokom maka Allah ya Rabaka da ita..Tun Zuwaira nada rai Tasha maka kukan wannan bakar Zuciyar taka..Tasha Fadamim Tayaya kana irin wannan abubuwan Za’a Dauki mace abaka..? Wanda bai iya Kula da Rayuwarasa bane zai kula da na wata..?
Ko Dago kansa bai yi ba kansa na kasa Shi Abba wai baisan kara ma wutar Abun yake ba yana Mai fada gaban wannan Mara mutumcin yarinyar bane,Shiyasa kawai ya Mike saboda in yacigaba da Zama komai zai iya Faruwa ba Cikin Sassarfarsa ya Wuce Dakinsa ya Shige Lokaci Daya yana Bango kofa Bumm!
Abba ya Bisa da kallo Kafin ya Kada kai yana Fadin Allah ya Shirya.
Inteesar ya kallata Da Tayi Tsuru Tsuru Yace”Inteesar kiyi Hakuri kin ji ko..? Yi tafiyarki Wajen Munari haka yayan naku yake sai Hakuri..!
Kamta ta Sadda kafin tace”Bakomai Abba..”
Ta juya zuwa Dakin Munari sai ma ta ganta akofar Dakinta Ashe Tun Tsawan Farko ta Fito ganin Abunda ke Faruwa ya bata Tsoro yasa ko Fitowa ta kasayi kada ganin Wajenta tazo itama ahada da ita.
Hararanta Inteesar taja Tana Fadim”Ashe kina Tsaye kina ganin wannan Mahaukacin yayan naki Zai Dake ni..?
Munari batayi mata mgana ba Tayi Saurin jan Hannunta suka fada Dakinta ta maida Kofa ta Rufe Tana Waigre Waige,sai abun ya bama Inteesar Dariya ta Zauna Bakin gado Tana Fadin”Dillah bsshi fa anan Dakin..Naga kina ta Waige Waige ne..!
Munari ta Zauna kusa da ita Tana Sauke Numfashi tace”Baki san wanene ya Imu ba..Da baki Fara yana mgana kina maidamai ba Besty..!
Inteesar ta Saki karamin Tsaki Tana Fadin”Munari Daman wannan Dan iskan ne yayan ki..? Tabdijam gaskiya baida Mutumci Wlh…!
Kallon da Munari tayi mata ne yasa ta Fahimci barnan Datayi da Sauri ta Wayance Tana Fadin”Yi hakuri ba Haka nake nufi ba..Ammh kawai sai ya Dakeni..? Kuma fa Shaye Shaye yake har acikin gida agaban Abba..? Ranar da na Fara ganinshi Tare da Sagir yana Shan Taba sai da nayi amai yanzu ma haka Zuciyata tashi Take yi Wlh..!
Ta karishe Fada tana wani Dakuna Fuska.
Munari ta karkace kai gefe tace”Ya Imu baya Shaye Shaye Besty..!
Inteesar ta Kalleta tace”Ita Sigarin kin Cireta a Ciki ne..!?
Munari Tace”Kefa wani Lokacin kina jin kanki kamar Wata bagwariya..Sigari ai ba Bugarwa kuma Bata saka maye bata Cikin kayan Shaye Shaye..!
Inteesar ta Bugamata Harara Tana Fadin”Kare mai Tunda Yayanki Ne besty..Ammh ni kam kiyi hakuri bazan fasa Fadin gaskiya ba Itama Sigarin ai Duk Mayen ne miye maraban Dambe da Fada..? Nifa Tun ina karamata Na daukan mai Shan Sigari nake Dan iska..!
Munari Tayi Mirmishi Tana Fadin”Ko Daya..Ba ina karema Ya imu bane sai Don yana Dan”uwana ba A”a Sai dan Gaskiya nake Fadamiki baya Shan kowani kayan maye banda Sigari..Ita kam Ta Zama addict atare tsshi Dashi..Zai iya Shanta Daga Safe Har Dare bai Nemi wani abinci ba ko Ruwa ba..!
Inteesar ta Zaro ido Tana Fadin”Kuma Lafiyarsa Kalau..?
Munari tace”Ba gashi kingani ba..Ai da kim Tsaya daya Nuna miki Lafiyarsa kalau..!
Inteesar tace”Tabdijam wa ni..? Na Tsaya ya Karyani..? Naga yadda yake Huci kamar Zakin Daya Kwana Biyu bai Samu Nama ba..tsoro ya kamani badomin su Abba ba yau da na gama Yawo wannan Mara mutumcin yayan naki!
Kallon ta kawai munari tayi batayi mgana da Sauri tace”au na manta Sorry..!
Munari ta kada kai kafin Tace”ke mai Sa’a ce Besty..!
Inteesar ta Kalleta Tana Fadin”Sa”ar me..?
Munari tace”Banta ba ganin ya Imu ya Tsaya yana mgana da mace Haka kamar yadda kukayi ba..ko mu da muke kanmensa baya mgana Damu Mu maida masa martani Daga kusa kusa..Baya som ka Rainashi ko alama Yana Daga Cikin Abunda ya Tsana Kazo wucewa ko kazo gabansa yana Shan Sigari ka Toshe Hanci..! Wlh ni nan ya Taba kamani na Toshe Hancina Domin Nima bana son Warinta Wlh Tallahi Daya Kama Bakina ya Damke Ya Rika Fesamin Hayakin Sigarin acikim Hancina sai da kara Daya ta kare Hayaki na Shiga Cikina da ace ina da Asthma na Tabbata da sai na Mutu Har Lahira aranar..!
Inteesar ta Kwalalo ido Cikin mamaki da Tsorata tace”Kai Besty..Kuma kika Tsaya..? Meyasa baki gudu ba..!
Munari ta saka Dariya Tana Fadin”Dana Gudu da kila Har da Duka Zai Hadamin..Ai shi bakayi mai Laifi Ya Kiraka ka Gudu..Zai ga ka Rainashi Saboda Zuciyarsa In ya kama Dukan Mutum sai ya Sumar dashi..!
Zuwa Lokacin Inteesar ta gama Tsorata Cikin Kwalkwal da ido Tace”Na Shiga uku Besty..Ya Zanyi na koma Gidan Mama yau..!Me munari Zatayi in ba Dariya ba Harda Dukawa Inteesar ta Daka mata Duka abaya Tana Fadin”Shegiya Daman Ciwon karya kike yi ko..?Domin ni ban ga alamun patient anan ba..!
Munari ta Dago Tana Lamgwabe Wuya Tana Fadin”Wlh bani Lahiya
Zazzabi yau na Tashi Dashi..Taba Jkina ma kiji..!ta fada Tana Daukan Hannun Inteesar ta Dora Saman Wuyanta.
Inteesar taji da Dumi tace”Eh gaskiya kina Fever to kin sha mgani..?
Kai ta gyada mata Tana Fadim”Tashin na kenan tunda nssha Mgani..Sai naga Kiranki a waya ina Shirin kiran ki naji Tsawan ya Imu Shine na Leka sai na ganki Kina ta Zare ido nace yau Besty ta Fada inda bai Dace ba..!
Inteesar tace”Umh bari kawai..Ai Insha Allahu bazamu kara Haduwa ba.Na tsorata da Labarin da kikabani im na Auna yadda naga Lokaci Daya ya koma..Ammh dai ke bai taba Dukkan ki ba ko..?
Munari tace”ya taba Kamar sau Biyu ko…Inaganin. shima mari ne da Tokari.Ni ai ina Kiyayemai Anty Asma”u ce Tasha Wahalan sa sosai Har Sumar da ita ya taba yi Dayake ita ke Binsa..!
Inteesar taji Gabanta ya Fadi ta Dafe Kirji tace”Innalillahi Anya bai da Aljanu..!
Munari tace”ke Lafiyansa kalau fa..!
Ta karishe Fada Tana Dariya Inteesar Tace”Ai naji abun nasa ne bana Hankali bane..Allah Sarki Yanzu ina ina Anty Asma”u? Hala tayi aure ne..naji baki taba bani Labarinta ba..!
Munari Tayi Shuru batace komai ba Inteesar ta Kalleta kafin Tace”Ko Ta Rasu ne..?
Munari ta Kalleta da Sauri tace”Ya akayi kika sani..?Inteesar Cikin jimami Tace”Yadda naga kin yi ne Besty..Am sorry bansani bane da Ban Tambaya ba Allah ya jikansu da Rahma Kice Bayan Rashin Anni Harda ta Asma”u ma kunyi..So Sad..!
Dayake inteesar din ta Taba Tambayanta Ina Mahaifiyarsu tace mata ta Rasu.
Cikin Wani yanayi Munari ta amsa da Ameen.
Daganan suka bar mganar suka Shiga Wata,Suna ta Hira makaranta suna Dariya,Sai ga Anty Safiya ta Shigo Itama ta Shige Cikinsu suna ta Hira,Sai bayan La”asar Inteesar Tayi Shirin Tafiya bayan Tayi Salla,Basu yi karatun ba sai gobe lokacin Munari ta kara jin Sauki, Sun Fito Falo Munari taji Sauki ta Rakota suka Iske Anty Safiya tana Kallo Munari ta Tambayeta Abba tace Yusuf ya Dauketa sun Shiga Cikin gari zama Wuri Daya ba Dadi Munari ta kada kai Tace hakan nada kyau sosai.
Daganan Sallama Inteesar Tayi mata Suka Fice Haraban Gidan suna Tafe suna Hirarsu basu ma Lura da Wanda ke Tsaye a Haraban gidan ba jikin Mashin Dinsa,da Tun Fitowarsu Idanuwansa Gabadaya yana kansu..!

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button